2025-08-14@11:58:10 GMT
إجمالي نتائج البحث: 3191

«Ya ku mutane»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Olubadan na Ibadan, Oba Owolabi Olakulehin ya rasu, yana da shekara 90 a duniya. Kakakin iyalan basaraken ne ya tabbatar da mutuwarsa da safiyar yau Litinin cikin wani saƙo da ya aike wa manema labarai. Kwanaki biyu da suka gabata ne basaraken ya gudanar da bikin cikarsa shekara 90 a duniya a wani ƙasaitaccen biki da aka gudanar a fadarsa. A shekarar da ta gabata ne aka naɗa Sarki Olakulehin a matsayin Olubadan na Ibadan bayan rasuwar wanda ya gabace shi Sarki Alli Okunmade II.
    An kashe mutane tara tare da jikkata wasu huɗu a wani da mayakan Boko Haram suka kai yankin a Malam Fatori da ke Jihar Borno. Gwamna Babagana Zulum, wanda baya kasar a halin yanzu, ya tura tawaga ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Sugun Mai Mele, domin jajanta wa waɗanda abin ya shafa da kuma tantance halin da ake ciki. Mai Mele ya jaddada aniyar Gwamna Zulum na jajircewa wajen tabbatar da tsaron Malam Fatori saboda muhimmancinsa. Ya sanar da shirin tura manyan injina domin tona ramuka a kusa da hedikwatar ƙaramar hukumar don hana hare-hare nan gaba daga Boko Haram da ISWAP. Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato Sarkin Ibadan ya...
    Hukumomi a jihar Texas da ke Amurka sun tabbatar da mutuwar fiye da mutum 80 sakamakon ambaliyar da ta auka wa jihar tun a ranar Juma’a. Mutum 68 daga cikin waɗanda suka mutu ciki har da ƙananan yara 28, a gundumar Kerr suke. Har yanzu akwai ƴanmata 10 da mai kula da wurin shaƙatawar Mystic da ba a ji ɗuriyarsa ba. Alƙaluman waɗanda suka mutu na sauyawa cikin hanzari, yayin da masu aikin ceto ke ci gaba da lalubo gawarwaki. Shugaba Trump ya ce ya tsara zuwa yankin da lamarin ya faru cikin wannan mako
    A wani yunkuri na bunkasa samar da wutar lantarki da kuma bunkasar tattalin arziki, gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da rabon kashi na farko na taransfoma 500 ga al’ummomin karkara a fadin kananan hukumomin jihar 44.   Gwamna Abba Yusuf ne ya kaddamar da shi a hukumance a Kano a wani shirin da nufin magance kalubalen rashin samar da wutar lantarki.   Gwamna Yusuf ya ce samar da taransfoma wani shiri ne na bunkasa masana’antu da zaburar da harkokin kasuwanci musamman a yankunan karkara.   “Wannan rabon shi ne kashi na farko na aikin samar da wutar lantarki a yankunan karkara, ba wai kawai wani aikin samar da wutar lantarki ba ne, wani muhimmin mataki ne na inganta samar da...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran wanda yake halattan taron kungiyar raya tattalin arziki ta Bricks ya yabawa kungiyar kan yin tir da Amurka da kuma HKI kan keta hurumin kasar da yaki na kwanaki 12 da kuma da kuma kaiwa cibiyoyin nukliyar kasar ta zaman lafiya wadanda suke Fordo Natanz ta kuma Esfahan. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalti ministan yana fadar haka a taron kungiyar karo 17 wanda ke gudana a hilin yanzu a birnin Rio De jenero na kasar Brazil. A ranar 13 ga watan Yunin da ya gabata ne jiragen yaki na HKI suka kutsa cikin Iran inda suka kashe manya-manyan kwamandocin sojojin kasar da kuma masana fasahar Nukliyar kasar ga shahada. Bayan haka...
    Shugaban Kungiyar Harka Islamia a tarayyar Najeriya Sheikh Irahim Zakzaky ya taya mutanen kasar murna saboda nasarar da suka samu kan HKI da kuma Amurka a yakin kwanaki 12 a cikin watan da ya gabata. Ya ce wannan nasarar bata takaita da mutanen kasar Iran kadai ba , hada har da al-ummar Musulmi da kuma da kuma masu sun yenci a ko ina suke. Ya kuma yaba da yadda gikuwan nmalamai na kasar Iran suka sami nasarar kare kasar daga mafi yawan hare-haren  HKI a kan kasar. Ya bayyana cewa Iran ta sami nasara a kan kasashen yamma da makamai wadanda suka fi nasu karfi da inganci, har’ila yau sun sami nasara a kan ma;aikatan yahudawan da suke taimaka masu...
    Miliyoyin yan Najeriya ne suka gudanar da tattakin Ashoora a birne daban daban a kasar a jiya Lahadi. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran, da farko ya nakalto daruwan da suka fito tattakin na Ashoora a Abuja babban birnin kasar a safiyar jiya Lahadi. A wannan karon dai masu tattakin Ashoora a Abuja sun fito ba tare da sanya bakaken kaya ba saboda kaucewa rikici da kuma kamu daga Jami’an tsaro a birnin, kamar yadda suka sabayi a shekarun da suka gabata. Labarin ya kara da cewa an gudanar da irin wannan tattakin na Ashoora a garurwa kimai 25 a duk fadin kasar, kuma an kammala ba tare da wata matsala ba. An gudanar da tattaki a jihar Bauchi...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Zaɓaɓɓun shugabannin gwamnati sukan naɗa wasu muƙarrabai don su taya su sauke nauyin da aka ɗora musu. Wasu na zargin naɗin ba ya rasa nasaba da sakayya ga irin rawar ga waɗanda aka naɗa saboda rawar da suka taka yayin yaƙin neman zabe. Shin irin waɗannan nade-naɗe na da wani tasiri ga rayuwar al’umma? NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta? DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan nade-naɗen masu taimaka wa shugabanni da irin tasirin da suke da shi. Domin sauke shirin, latsa nan
    Mataimakin firaministan kasar Sin Liu Guozhong, ya yi kira da a gaggauta samar da sabbin fasahohin kimiyya a fannonin aikin gona da kiwon lafiya, da karfafa cin gashin kan fasahar kirkire-kirkiren magunguna da na’urorin likitanci. Liu, mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya bayyana hakan ne yayin ziyarar bincike da ya kai lardin Guangdong da ke kudancin kasar Sin daga ranar Alhamis zuwa Asabar da ta gabata. Ya jaddada cewa, ya zama wajibi a mai da hankali kan bukatu na gaggawa da ake da su a bangaren masana’antar da kuma ba da karfi ga muhimman fannoni kamar masana’antar fasahar samar da iri, da injunan noma, da kayan abinci, da fasahar shuka da kiwo. Liu...
    “Na yi Allah- wadai da amfani da madafun iko da tsara sakamakon zabe kafin zabe ta hanyar amfani da karfin mulki da hukumomin gwamnati.” “Wajibi ne Hukumar Zabe ta samu hanyoyin magance wadannan matsalolin a wajen jefa kuri’a maimakon neman hakki a bangaren shari’a wanda daga karshe kotu za ta sanya wasu dubaru ta kori kara mai kyau ta fashin zabe.” Ya bayyana. Ya ce irin wannan matsalar na samar da mutanen da ba su ko iya cin zabe a cikin dangin su ko al’ummar su amma sune ke tinkahon lashe zabe. A cewarsa a matsayinsa na dan majalisar dattawa suna kokarin gabatar da dokokin da za su shawo kan wadannan matsalolin, ya ce sun san hukumar zabe ba za...
    A cikin ‘yan kwanakin nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mayar da jawabi ga malamai da daliban tawagar musayar al’adu ta matasan Amurka masu buga wasan kwallon pickle daga gundumar Montgomery ta jihar Maryland, wadanda suka ziyarci kasar Sin a karkashin shirin gayyatar matasan Amurkawa 50,000 zuwa kasar Sin domin yin musaya da kuma nazarin karatu a cikin shekaru biyar.   Xi ya ce, makomar alakar Sin da Amurka ta dogara ce da matasa, yana mai bayyana fatan wakilan tawagar za su zama sabbin jakadu na sada zumunci a tsakanin kasashen biyu, da ba da gudummawa sosai wajen yaukaka zumuncin da ke tsakanin jama’ar kasashen biyu. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna...
    Raundunar sojan jamhuriyar Nijar sun sanar da cewa, an kashe  sojoji 10 da kuma jikkata wasu 15 a wasu hare-hare biyu da masu dauke da makamai su ka kai a yankin Telaberi da kudu masu yammacin kasar. Yankin Telaberi dai yana cikin yankunan da masu dauke da makamai su ka fara kai hare-hare saboda kusancinta da iyakokin kasashen Mali da Burkina Faso. Bayanin na sojojin kasar ta Jamhuriyar Nijar wanda kafafen watsa labarun kasar su ka watsa ya kunshi cewa; Daruruwan masu dauke da bindiga sun kai hare-hare a kan sansanonin soja biyu da suke a yankin Telaberi da hakan ya yi sanadiyyar kashe sojoji 10 da kuma jikkatar wasu 15.” Sai dai kuma sanarwar ta ce, sojojin sun yi...
    Sanatan ya bayyana cewa gwamnonin yankin na farko sun ba da gagarumar gudunmuwa wajen jagorantar hadin kai wajen cimma muradun yankin daga kan ikon sarrafa albarkatun kasa zuwa matsalolin muhalli da sauransu. A kan wannan ya yi kira ga gwamnoni.masu ci a yanzu da su ci gaba da wannan al’adar, kuma su kara kokari kan ciyar da yankin a gaba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Ɗaya daga cikin hadiman gwamnan jihar Yobe, Hon. Babagana Yakubu Mohammed, ya ajiye muƙaminsa na mai taimakawa gwamna na musamman ya kuma fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADC. Babagana, ya sanar da ajiye aikin nasa ne cikin wata wasiƙa da ya aikewa Sakataren Gwamnatin Jihar, Baba Malam Wali. Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha A kwafin wasiƙar da LEADERSHIP ta samu, Babagana ya bayyana matuƙar damuwarsa kan yadda aka yi watsi da wanda suke hidimtawa gwamnati da taimaka mata. “Don haka ina sanar da ajiye aiki na a hukumance daga matsayin mai taimakawa gwamna na musamman” cewarsa. A ƙarshe, ya godewa...
    Gangamin Ashura ya zama lamarin mafi girma da cunkoson jama’a inda tattakiin Tuwairij yake gudana tare da faɗaɗa da ba a taɓa ganin irinsa ba Tattakin Tuwairij na bana zuwa birnin Karbala na fuskantar hallara da cunkoson jama’a da ba a taba ganin irinsa ba, inda dimbin masu ziyara  daga sassan duniya ke tururuwa zuwa hubbaren Imam Husaini da kuma titunan da ke kewaye. Mai ba da shawara ga babban sakataren cibiyar Hubbaren Imam Husain {a.s} Fadel Oz a cikin wata sanarwa da ya aikewa kafafen watsa labarai ya bayyana cewa: “A shirye-shiryen wannan juyayi, babban Sakatariyar Haramin Imam Husain (a.s) da haramin Abbas sun samar da dukkan sharuddan da suka dace don kula da masu ziyara da kuma tabbatar...
    Babban Mufti na masarautar Oman ya yi kakkausar suka kan kasashen da ke neman kulla alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya bayyana mamakinsa kan yadda wasu kasashe ke son kulla                     alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, wata kasa ‘yar mamaya maras tushe. A cikin wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X, Ahmed bin Hamad Al-Khalili ya ce: “Abin mamaki ne yadda wasu kasashe ke son kyautata alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, alhali su kansu suna kallon wannan mahalukiya a matsayin wata kasa mai gushewa ko ba dade ko ba jima, al’ummarta dai suna son ci gaba da yakin ne kawai don ci gaba da wanzuwarta, in ba haka ba,...
    Lamarin da ya haddasa daya daga cikin bala’i da mutane suka taba fadawa, inda sama da mutum miliyan 12 suka tsere daga gidajensu. Darfur ta kasance yankin da nan da nan rikici kan tashi, inda RSF ke iko da yawancin yankin, in banda birnin el-Fasher wanda ya ci gaba da kasancewa a hannun rundunar sojin kasar da kawayenta. Birnin el-Fasher ya sha ruwan bama-bamai a yayin da RSF ke kokarin kama shi. A watan Afirilu RSF din ta sanar da shirin kafa gwamnati domin zama kishiya ga gwamnatin soji, abin da ya haddasa fargaba cewa hakan zai kai ga rarraba kasar. Alawia ta ce yayin da fadan ya tsananta ake ta ruwan bama-bamai a watan da ya gabata, dole ita...
    Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya halarci zaman makokin da aka gudanar a hussainiyar Imam Khomaini (q) da cikin gidansa a nan birnin Tehran a daren Ashoorah a jiya Asabar da yamma. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Hujjatul Islam Masaoud Ali wanda ya karanta makokin yana fadar cewa, kasar Iran zata dauki darasi daga Imam Hussain (a) na rashin mika kai da azzalumai. Ya kuma bayyana yunkurin da Iraniyawa suke yi a halin yansu yana daga cikin gwagwarmayan duniya don fuskantar azzaluman duniya karkashin jagorancin HKI da Amurka.   Ya kuma kara da cewa musulunci ne yake gaba da gaba da kafircin duniya a cikin yakin kwanaki 12 wanda HKI da Amurka...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa dukkan kasashe mambobia a kungiyar ECO ta raya tattalin arziki na kasashen yankin sun yi tir da HKI a taron kungiyar wanda aka gudanar a birnin Khankendi. Na kasar Azerbaijan. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka bayan tawowarsa daga taron a daren jumma’a a kuma shafinsa na X. Shugaban ya kuma kara da cewa Tehran a shirye take ta hada kai da wadannan kasashe makobta don taimakawwa juna a dukkan bangarorin rayuwa wadanda suka hada da kyautata tattalin arzikin yankin da al-adu da sauransu. Shugaban ya bayyana cewa yana godiya ga dukkan kasashen kungiyar ECO da kuma sauran kasashen yankin da sauran kasashen duniya wadanda...
    Ibrahim ya bayyana cewa, sun rarraba mukamai na rikon jam’iyyar a tsakaninsu, kafin babban taro na kasa a nan gaba. Gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ya tabbatar cewa; hadakar ta ADC, ta zabi Aregbesola a matsayin sakatarenta na kasa na riko, har ma ya wallafa a jawabin karbar mukamin da ya yi a shafukan sada zumunta. Matakin ‘yan adawar na shiga ADC, na zuwa ne bayan kasa cimma bukatarsu ta yi wa sabuwar kungiyar mai suna ‘All Democratic Alliance’ (ADA), rajista a matsayin jam’iyyar siyasa, sakamakon jan kafa da suka rika samu daga babbar hukmar zabe ta kasa (INEC). Haka zalika, Atiku Abubakar da wasu manyan jam’iyar PDP, sun nemi ‘yan jam’iyyar da su hada hannu da su wajen shiga...
    Zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD da sauran kungiyoyin kasa da kasa a birnin Geneva Che Xu, ya yi jawabi a gun taron tattaunawa na shekara-shekara, kan gudummawar fasahohi karo na 59, na majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD a jiya Juma’a, a madadin walikan kasashe fiye da 70, game da raya hidimomi ga nakasassu ta hanyar fasahar AI, inda ya yi kira ga raya fasahar AI don inganta fasahohi, da karfin hidimomin da ake samarwa nakasassu, da kuma sa kaimi ga sassan kasa da kasa, ta yadda za su iya more fasahohin bunkasa fasahar AI. A cikin jawabin nasa, ya gabatar da shawarwari uku. Na farko ya ce kamata ya yi a mai da hankali ga bukatun dan...
    Rahotanni daga kudanci Lebanon sun ce, sau uku jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a kan gidajen mutane da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu da dama. A garin Shaqra’dake yankin Bint-jubail, jiragen sama marasa matuki sun kai hare-hare da ya yi sanadiyyar jikkatar mutane biyu da raunuka, kamar yadda ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar. Har ila yau wani jirgin maras matuki na abokan gaba ya kai wani harin akan wata mota a yankin “Safful-Hawa” da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya. A garin Shab’a kuwa ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan wani gida, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutanen dake cikinsa. Majiyar asibiti a garin Marja’iyyun ta ce an kai...
    Dakarun kare juyin musulunci na Iran sun fitar da bayani a lokacin tunawa da sace jami;an diplomasiyyar Iran 4 a birnin Beirut, wanda ya kunshi cewa: Ya zama wajibi ‘yan sahayoniya su kwana da sanin cewa; Duk laifukan da su ka aikata a baya za a yi musu sakamako a kansa,kuma duk wani sabon wuce gona da iri, zai gaggauta zuwa karshensu ne.” Sanarwar ta kuma ce: Muna tunawa ne da zagayowar cikar shekaru 42 daga wancan aikin ta’addanci, da a yanzu kwanaki kadan ne su ka wuce na kawo karshen yakin da HKI da Amurka su ka kallafa mana na tsawon kwanaki 12. Yaki ne wanda martani mai karfi da jamhuriyar musulunci ta Iran ta mayar yake kara fito...
    Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro wanda ya bude bikin baje kolin littatafai na kasa da kasa a kasarsa, ya yi jinjina ga Imam Khumaini  ( r.a) da kuma jagoran juyi Ayatullah Sayyid Ali Khamnei. Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto cewa, A yayin bikin bude taron baje kolin, shugaban kasar na Venezuela ya bayyana girmamawar da yake yi wa jagoran juyin musulunci, tare da yin ishara da ganawarsu a shekarun 2000 da 2010. Haka nan kuma shugaban kasar ta venezuella ya bayyana yadda ya ga al’adu da ci gaban al’ummar Iran da su ka ja hankalinsa da burge shi matuka. Bugu da kari shugaba Maduro ya bayyana zurfin hikimar da ya gani a tare da jagoran juyin musulunci, ...
    Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim  ya mayar da martani ga wadanda suke son, kungiyar ta mika makamanta, yana mai cewa; Ku fara da neman makiya su fice daga cikin Lebanon, domin babu hankali ace ba ku cewa komai akan ‘yan mamaya,ya zamana kuna neman wanda yake gwgawarmaya ya ajiye makamansa.” Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Duk wanda ya amince da mika wuya, ya yi, amma mu ba za mu laminta da hakan ba. Mu almajiran makarantar Imam Hussain ( a.s) ne da yake cewa: Ba Za Mu Taba Lamunta Da Kaskanci Ba.” Sheikh Na’im Kassam ya ce: Wadanda suke jingina da kasashen waje, suna kuskuren lissafi, domin masu gwgawarmaya ba su ganin wani kwarjinin...
    Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano: Gani suke ai in su nuna suna samu kamar matan nasu za su dora musu hidima da yawa, sun gwamma ce su bar matansu da wahala. Wani ma dan rashin imani kokari yake ita matar ta ciyar da shi alhalin yana da damar sa, shi ya sa ko yaran wani lokaci in suka taso komai na mahaifiyarsu sai daga baya ya zo ana da-na-sani mara amfani a lokaci da ba shi da amfani. Rashi tausayi ne kawai kuma kusan yanzu ma kaso casain na maza haka suke, ka so daya ne suke kyautatawa iyalansu. Kalubale babba ma kuwa shi ya sa sam! yanzu auren ma ba ya karko, karshe a jefa...
    Yadda za’a hada: Asamu biredi mai yanka-yanka a shafe shi da bota a ajiye a gefe. Sai a zuba mai a cikin karamin kaskon miya sai a zuba yankakkiyar albasa a dan soya na minti biyu, sai a zuba jajjagagen su attaruhu din nan a ci gaba da soyawa. A zuba kayan kamshi da kayan dandano, sai a zuba yankakken kabeji. Idan aka tabbatar duk sun soyu sai a dauki kifin gwangwani a tsiyaye man cikinsa sai a faffasa shi a zuba a kai a ci gaba da juyawa har komai ya hade jikinsa. Akunna injin gasa buredi, sai a dauko wannan buredi mai yanka-yanka wanda aka shafa bota a jiki sai a zuba wannan hadin su kifin nan a...
    Kungiyar Kananan Hukumomin Nijeriya (ALGON) reshen Jihar Kaduna, ta mika sakon taya murna ga Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa lambar karramawa ta CON da shugaban kasa ya yi masa ado da ita, wacce ke matsayin wata alamar girmamawa a Jamhuriyyar Nijeriya ta Hudu. Wannan karramawar, wata alama ce a sarari ga sadaukarwar mai girma gwamna, da gagarumin nasarorin da ya samu a hukumance, da kuma jagoranci mai tsari da yake kai domin ci gaba da tsara tafiyar dimokuradiyyar kasa. Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8) Wannan na kunshe ne a cikin wata takarda dauke da sa hannun sakataren yada labarai...
    “A kowane mako, muna karbar yara fiye da 100 da ke fama da cutar maleriya. Sannan kuma, mafi yawancin lokaci; ba a kawo su asibiti, sai cutar ta tsananta”, in ji likitan. – Ciwon ciki da amai da gudawa (kwalera): Lokacin damina na kawo yawan samun gurbataccen ruwa, wanda ke haddasa cututtuka kamar ciwon ciki, amai da gudawa da kuma zazzabin taifod. Wannan na yawan shafar yara, musamman ‘yan kasa da shekara biyar. Dakta Ahmad ya kara da cewa, “Yara na da rauni a garkuwar jikinsu, sannan kuma idan suka kamu da gudawa, jikin nasu na rasa ruwa cikin sauri, har ta kai ga samun mace-mace.”   -Kaikayi da kurajen fata: Likitan ya ce, lokacin damina na matukar kawo danshi,...
    Wacce irin gudunmwa kafofin samun ilimi suke badawa ta yadda za a samu hanyar kara ilimi A kokarin da ake yi na yadda za a samar da dama wadda kowa zai iya samun ilimi mai kuma inganci,ta kuma kafofin sadarwa na zamani. Hanyoyin koyo da kafofin sadarwa na zamani,kamar digirin da ake yi saboda yin karatun digiri ta kafar sadarwa ta zamani,da kuma a kasnce kamar ana cikin aji ne,saboda a ba dalibai wata dama wadanda kuma suka kasance daga wuraren da suka bambanta, manufa anan itace yadda suka zo daga wurare daban daban.Rin wannan ci gaban wanda ya kan kasance ga mutane ko al’umma daban daban,wadanda zasu iya fuskantar bambanci saboda daga wurin da suka fito, lamarin kudi,ko kuma...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    “Wannan aiki ne, wanda za a iya cewa; tamkar a yanzu ne muka fara dora damba a kansa”, a cewar shugaban. Haka zalika, shugaban ya kuma sanar da wadanda suka halaccin taron kaddamar da shirin tabbacin cewa; wadannan ayyuka na noman zamani, za su kara taimakawa wajen kara samar da ayyuka a fannin aikin noma sama da 2,000. Ya ci gaba da cewa, kayan za su kuma taimaka wajen kara ayyukan masana’antun kasar da samar da damar gudanar da yin bita da kuma kwararrun kayan aikin noma 9,000. Shugaban ya jaddada muhimmancin yin amfani da kayan aikin noma na zamani, wanda hakan zai taimaka wa manoman wannan kasa. Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; kaddamar da wannan...
    Sheikh Na’in Kasem shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ya bayyana cewa kungiyar bata bukatar Izini don kare kasar Lebanon daga makiyanta. Yama fadar haka ne ga wanda suka cika kunnen duniya kan cewa dole ne kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar. Kamfanin dillancin labaran Tasnim ya nakalto Sheikh Kasim yana fada a wani jawabin da ya gabatar a ranakun Ashoora na Imam Hussain (a) ta kafar Bidiyo. Ya kuma kara da cewa wadanda suke maganar kungiyar Hizbullah ta mika makamanta ga gwamnatinsa kasar, ya fiye masu sauki su fadawa yan mamaya su fice daga kasar Lebanon su kuma dakatar da hare-haren ta’addancin da suke kawo mata. Ya kara jaddada cewa kungiyarsa zata ci gaba da rike makamanta sannan...
    Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye, ta bada sanarwan cewa da ita da sauran kungiyoyi da suke gwagwarmaya da HKI kimani shekaru biyu da suka gabata, sun amince da batun tattaunawa da kuma tsagaiuta budewa juna wuta wanda masu shiga tsakani suka gabatar. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa, shugaban kasar Amurka Donal Trump ya ce, wai HKI ta amince da shawarar budewa juna wuta da ya gabatar, amma kuma har yanzun ba’a bayyana dalla-dalla menen a cikin yarjeniyar ta kunsa ba. Har’ila yau gwamnatin kasar Masar ta ce tana kokarin ganin an samar da tsagaita budewa juna wuta na kwanaki 60.
    Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a. Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da...
    ‘Yan kasuwa sun yi hasashen cewa za a yi sabon tsarin farashin daga ranar Lahadi. Tun a ranar Talatar da ta gabata, wakilinmu ya lura cewa sauran masu gidajen man da masu shigo da kaya sun daidaita farashinsu domin nuna sabon tsarin farashin da ya biyo bayan tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Iran. Daga Naira 920, akasarin gidajen sun rage farashin zuwa matsakaicin farashin Naira 845 akan kowace lita. A cewar Petroleumprice.ng, RainOil, Pinnacle, Matrid, Emadeb, Wosbab da First Royal suna sayar da man fetur a kan Naira 845 a Legas ranar Talata. Hakazalika, NIPCO, Aipec sun sayar da mai akan Naira 850 akan kowace lita. A sauran defot da ke wajen Legas, irin su Warri da Fatakwal, ana sayar...
    Shugaban kasar Amurka Donal Trump Ya Bayyana cewa nan da kwana guda ko sa’o’ii 24 masu zuwa ne zai sani, ko kungiyar Hamas ta amince da ‘shawararsa ta tsagaita wuta da HKI kuma ta karshe a gaza. Shafin yanar gizo ta labarai ‘Arabnews ta kasar Saudia’ ta nakalto Trump yana fadar haka a yau jumma’a. A wani bangare shugaban ya ce yayi magana da gwamnatin kasar Saudia dangane da fadada yarjeniyar Ibrahimia wacce ya samar da ita a shugabancinsa na baya wacce take bukatar kasashen larabawa su samar da huldar jakadanci da HKI, wanda kuma ya sami nasarar a kan wasu kasashen larabawa na yankin tekun Farisa. Daga shekara ta 2023 ya zuwa yanzu yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 56,000...
    A bana ake bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU, ana kuma daf da gudanar da sabon zagayen taron jagororin Sin da EU. Sakamakon hakan, jerin ayyukan cudanya a matsayin koli tsakanin sassan biyu na kara jan hankali. A baya-bayan nan, an gudanar da dandalin tattaunawa na manyan jami’ai tsakanin Sin da EU karo na 13 a birnin Brussels na kasar Belgium. Kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da shugabannin EU, tare da ziyartar kasashen Jamus da Faransa. Bangaren Sin ya jaddada cewa, bunkasar tafarkin ci gaban alaka tsakanin Sin da EU ya nuna kyakkyawar dangantakar sassan biyu maimakon adawa da juna, kuma hadin gwiwarsu shi ne...
    Har ila yau, da yake jawabi, mai gudanar da taron, Bonabenture Melah, ya ce makasudin tattaunawar shi ne, inganta dabarun sadarwa, da inganta fassarar bayanai, da samar da hadin gwiwa tsakanin kwararru a NiMet da ‘yan jarida, ta yadda ‘yan jarida za su yi aiki yadda ya kamata. Har ila yau, darektan Sabis na Hasashen Yanayi (DWFS) a NiMET, Farfesa Bincent Weli, ya lura cewa, “sauyin yanayi na da tasiri kai tsaye a rayuwarmu ta yau da kullum.” Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin kasarsa sun koya wa ‘yan sahayoniyya masu wuce gona da iri babban darasi Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a taron kolin kungiyar Hadin Gwiwar Tattalin Arziki ta ECO da aka gudanar a kasar Azarbaijan a yau Juma’a, ya jaddada cewa: Sojojin kasar Iran bisa doka mai lamba 51 na yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya  sun kare al’ummar Iran da mutuncin kasar da cikakken ikonta a yakin da aka yi a baya-bayan nan, kuma sun koyar da masu wuce gona da iri darasi mai girma da kuma dakile yaduwar yaki a wannan yanki. A yayin taron koli karo na 17 na kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da aka...
    Shugaban kasar Iran ya gana da fira ministan kasar Pakistan Shugaban kasar Masoud Pezehkian ya gana da fira                             ministan Pakistan Shehbaz Sharif a gefen zaman taron kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da Jamhuriyar Azabaijan ta karbi bakunci. Fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif ya yaba da irin rawar da shugaban kasar Iran ya taka a lokacin da yahudawan sahayuniyya suka kai wa Iran hari tare da tabbatar da goyon bayan Pakistan ga Iran da kuma hada kai da hadin gwiwa da Iran don samar da zaman lafiya a yankin. Sanarwar da ofishin fira ministan Pakistan ya fitar ta ce: shugaba Masoud Pezehkian ya gana da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif a gefen zaman taron kungiyar hadin kan tattalin arziki...
    Hadin Gwiwa Da Hukumar IAEA Shugaban kasar Iran ya rattaba hannu kan dakatar da hadin gwiwa tsakanin Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, bisa wata doka da Majalisar Shawarar Musulunci ta kafa kwanan nan Sanannen abu ne cewa: Wannan doka ta zo ne bayan hare-haren da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, a daidai lokacin da Iran ke shirin tunkarar tattaunawar nukiliya karo na shida da Amurka! Har ila yau, an san cewa shawarar ba ta zama ficewa daga yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi ba, a’a, ta dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ce ta IAEA...
    Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehra mya bayyana cewa: Hukuncin shari’a da ya hau kan Trumpm da Netanyahu shi ne kisa Limamin da ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran a yau ya bayyana cewa: Amurka da karen da suka horar sun yi barazana ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma wannan wauta ce. Hakika dokar Musulunci ta Trump da Netanyahu ita ce mutuwa. Sun kashe mutane fiye da 55,000 a Gaza. Su suka kai Qasim Sulaimani da yin shahada da sauran abokansa. Su ne masu aiwatar da kisan kai da ayyukan fasadi a duniya. Sun yi wa Jagoran juyin juya halin Musulunci da al’ummar Iran barazana. Abin farin cikin shi ne, dukkanin hukumomin...
    Yakubu ya jaddada kokarin hukuma wajen yin adalci. “Za mu duba dukkan bukatun cikin adalci ba tare da la’akari da matsayin wadanda suka kawo su ba, lallai hukumar zabe ba za ta taba karya ka’idojinta ba.” Shugaban INEC ya musanta zarginsu cewa hukumar kokarin hada kai da wasu domin saba ka’ida wajen yin ragisara, ya tunawa da irin wannan zargin da ba tare da hujja ba da aka yi a shekarar 2013. Ya bayyana cewa hukumar ta amince da dukkan wasikun da aka karba illa guda shida, wadanda za a yi aiki a kai kafin karshen mako. Haka nan ya lura cewa dokoki da ka’idojin zabe ta 2022 kan jam’iyyun siyasa yana nan a shafin intanet na hukumar. Yakubu ya...
      Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Gwamna Abba ya bayyana gamsuwarsa da ƙwarewar sabbin jami’an da aka naɗa, inda ya bayyana cewa za su taka rawar gani wajen aiwatar da manufofin gwamnatinsa. Ya ce jajircewa da ƙwarewarsu na daga cikin dalilan da suka sa aka zaɓe su domin su taimaka wajen ci gaban Jihar Kano. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A yayin bincike, ’yansanda sun ƙwato motocci huɗu, wuƙa, kayan sojoji, da harsasai. Game da fashi da makami, rahoton ya nuna cewa an samu rahotannin guda biyar daga watan Mayu zuwa Yuni, kuma an kama mutane 17 da ake zargi da aikata laifin fashin. Kwamishinan ya kuma ce an samu rahotannin safarar yara guda huɗu, inda aka kama mutane takwas da ake zargi. A cikin makaman da rundunar ta ƙwato akwai bindigogi AK-47 guda uku, ƙaramar bindiga ƙirar gida guda ɗaya, bindiga ƙirar Baretta, bindiga mai fitar da wuta, bindigogin LAR guda biyu, da harsasai guda 36. Sauran abubuwan da aka kwato sun haɗa da: gatari guda ɗaya, na’urar sadarwa (walkie-talkie) guda tara, da kuɗi Naira 79,000. Daga kanmu,...
    Hukumar ta NSEMA ta jagoranci gudanar da aikin, tare da tattara kayan aiki gami da tura kungiyoyin bayar da agajin gaggawa tare da hadin gwiwar hukumomin kananan hukumomi.’ Arah, ya bayyana cewa, kafin lokacin damina, hukumar ta NSEMA ta kaddamar da shirin wayar da kan jama’a game da ambaliyar ruwa a duk shekara a matsayin gangamin gargadin farko a ma’aikatun masarautu takwas, da nufin kara wayar da kan jama’a. “NSEMA ta kuma bayar da agaji ga wadanda gobarar gidaje da kasuwanci ta shafa a sassan jihar”. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban kasar Amurka Donal Trump Ya Bayyana cewa nan da kwana guda ko sa’o’ii 24 masu zuwa ne zai sani, ko kungiyar Hamas ta amince da ‘shawararsa ta tsagaita wuta da HKI kuma ta karshe a gaza. Shafin yanar gizo ta labarai ‘Arabnews ta kasar Saudia’ ta nakalto Trump yana fadar haka a yau jumma’a. A wani bangare shugaban ya ce yayi magana da gwamnatin kasar Saudia dangane da fadada yarjeniyar Ibrahimia wacce ya samar da ita a shugabancinsa na baya wacce take bukatar kasashen larabawa su samar da huldar jakadanci da HKI, wanda kuma ya sami nasarar a kan wasu kasashen larabawa na yankin tekun Farisa. Daga shekara ta 2023 ya zuwa yanzu yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 56,000...
    Bayan an rufe sararin samaniyar kasar Iran saboda yaki na kwanaki 12 wanda HKI ta dorawa kasar a ranar 13 ga watan yunin da ya gabata, a yau Jumma’a a bude zirga-zirgan jiragen saman a duk fadin kasar daga karfe 5 na safe zuwa 6 na yamma daga ranar Jumma’a 4 ga watan July 4, 2025. Sake dawo da zirga zirgan jiragen sama yana daga cikin matakan da hukumomi a Iran suka dauka don dawo da nutswa a cikin kasar bayan yakin kwanaki 12 da HKI. Hukumar zirga zirgan jiragen sama na kasar ta dakatar da sauka da tashin jiragen samane jin kadan bayan da HKI ta awkawa Iran da ya ki a ranra 13 ga watan yuni don lafiyar...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da labarin da ministan harkokin wajen kasar Jamus ya watsa dangane da shirin Nukliyar kasarsa ya kuma kara da cewa labarin jabu ne. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X . Ya kuma yi watsi da zancen ministan harkokin wajen kasar Jamus wanda yake cewa, jinginar da aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya wato IAEA wanda JMI ta yi,  ya na nuna cewa ba wanda zai bincika ayyukanta na makamashin nukliya ba, kuma ta rufe kofar tattaunawa Kenan. Aragchi ya bayyana cewa wannan ba haka bane, saboda shirin nukliyar kasar Iran a halin yanzu ya na karkashin majalisar...
    Gwamnatin Nijeriya na da shiraruwa da dama da manufar wadata kasa da abinci, inganta samun kudin shiga a karkara da rage fatara ta hanyar shiraruwa masu dorewa na bunkasa aikin gona, sai dai a kodayaushe kalubalen ‘yan ta’adda na hana shiraruwan samun nasara. Rahotanni da dama sun ruwaito yadda ‘yan ta’adda ke tilastawa manoma biyan haraji gabanin su ba su damar shuka da girbe amfanin gona a gonakin su wanda hakan babban kalubale ne ga manoma da kasa bakidaya. A bisa ga kasa biyan harajin da barayin dajin ke tilasta masu, dimbin manoma sun rasa rayukan su wasu kuma da dama sun yi gudun hijira daga garuruwan su domin tsira da rayukan su. A watan Yuni da ya gabata kadai...
    Ministan Babban Birninn Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya musanta labarin cewa ya yanka wa ’ya’yansa manyan filaye a Abuja, inda ya ce in ma haka ne suna da hakki a matsayinsu na ’yan Najeriya. Ana dai zargin Wike da ba biyu daga cikin ’ya’yansa fili mai fadin murabba’in hekta 2,082, dayan kuma mai fadin hekta 1,740, wanda aka kiyasta darajarsu ta haura Naira tiriliyan tara. Da yake zantawa da ’yan jarida a Abuja ranar Alhamis, Wike ya karyata labarin na cewa ya ba ’ya’yan nasa filayen a unguwannin Maitama da Asokoro. Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza To sai dai duk da haka, ya kare...
    Yan Najeriya da dama na ta bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan sabon hadakar ‘yan siyasa zuwa sabuwar jami’yyar ADC.   A yayin da wasu ke ganin wannan hadaka za ta cire musu kitse daga wuta, wasu kuwa gani suke yi duk kanwar ja ce. A ranar laraban nan ne dai gaggan ‘yan siyasa daga jamiyyu daban daban suka hadu don dinkewa wuri daya da niyyar kalubalantar jamiyya mai mulki ta APC, a cewar su za su ceto Najeriya daga halin da jamiyyar ta jefa su a ciki. NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan...
    Kazalika, gazawar Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA da kuma sauran hukumomin na jihohi na sauke nauyinsu, hakan ya nuna a zahiri, na irin kalubalen da ake fuskanta, na rashin sauke nauyinsu, na bayar da agajin na gaggawa. Misalii, an ruwaito cewa, a sansanin na ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman yadda suke kwana a kan tandarmin kasa, tare da kokawa da cizon Sauro, ‘ya’yansu ke ci gaba da zama a cikin yunwa, wanda hakan, ya kara harzuka su, fita yin zanga-zangar. Bisa wasu akaluma da aka samu daga Biniwe, sun nuna cewa, a sansanin na Yelwata, an samu haihuwa 15 da kuma mata da suka samu juna biyu, su 122, wadanda kuma suke ci gaba da rashin...
    Taron nay au dai an ba shi taken; Girmama Kwamandan Farmakin ” Wa’adussadiq” za kuma a yi shi ne da marecen yau a birnin Tehran a Husainiyyar ” Fatimatuzzahra ( a.s) dake karkashin rundunar soja ta ” Arrasulul-Muhammad ( a.s). Shi dai Birgediya Shahid Hussain Salami ya yi shahada ne a wani harin ta’addanci da HKI ta kawo wa Iran a ranar 13 ga watan Yuni tare da wasu kwamandoji da soja.
    Babban magatakardar MDD Antonio Gutress ta sanar da kaduwarsa da kuma jin haushin yadda wahalhalun Falasdinawa a Gaza suke karuwa, yana mai cewa: Sauran abinda ya rage da zai rike rayuwa a Gaza, ya kusa karewa saboda rufe hanyoyin da suke shiga Gaza da HKI ta yi. Kakakin babban magatakardar na MDD  Stephen Dujarric, ne ya ambato maigidan nasa yana fadin haka akan yanayin da zirin Gaza yake ciki, tare da kuma da cewa; MDD tana son ganin an bai wa fararen hula kariya da kuma biya musu bukatunsu. Antonio Guterres ya kuma bayyana firgitarsa a lokaci daya kuma da bacin ransa akan yadda Falasdinawan Gaza su ka cikin mawuyacin hali, yana mai kara da cewa da akwai adadi mai...
      Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
      Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
      Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran cin amanar diflomasiyya ce Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana harin da sojojin Amurka suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya a matsayin cin amanar diflomasiyya da kuma cewa wani mataki ne da ba a taba ganin irinsa ba ga tsarin doka da hakkin kasa da kasa da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya. Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da Ronald Lamola, ministan hulda da kasa da kasa da hadin gwiwa na Jamhuriyar Afirka ta Kudu, sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya bayan dakatar da hare-haren soji da yahudawan sahayoniyya...
    Kwamandan sojojin kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin Iran sun shirya tsaf don kare juyin juya halin Musulunci da kasarsu A yayin ziyarar da ya kai wa iyalan shahidi kwamandan tsaron cikin gida na kasar Iran Kanal Mohammad Alizadeh; Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Jajirtattun sojojin kasar Iran a shirye suke da dukkanin karfinsu wajen kare kyawawan manufofin juyin juya halin Musulunci da kuma dukkanin yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a cikin kowane irin yanayi da kuma fuskantar duk wani mai neman wuce gona da iri. Manjo Janar Amir Hatami, babban kwamandan sojojin kasar Iran, tare da rakiyar Hujjatul-Islam Ahmad Jalili Safat, mataimakin shugaban bangaren rukunan siyasa ta sojojin kasar, Manjo Janar Muhammad...
    Rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai ban tsoro ya bayyana cewa: Manyan kamfanoni suna da hannu wajen aiwatar da kisan kare dangi a Gaza Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya bayyana sunayen wasu manyan kamfanoni na duniya sama da 60 da ke da hannu a tallafawa wajen gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida a yankunan gabar yammacin kogin Jordan da kuma hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza. Rahoton wanda wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese, ta wallafa ya samo asali ne daga bayanai sama da 200 daga kasashe, kungiyoyin kare hakkin bil adama, masana ilimi da kamfanoni. Ta...
    Rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai ban tsoro ya bayyana cewa: Manyan kamfanoni suna da hannu wajen aiwatar da kisan kare dangi a Gaza Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya bayyana sunayen wasu manyan kamfanoni na duniya sama da 60 da ke da hannu a tallafawa wajen gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan kaka gida a yankunan gabar yammacin kogin Jordan da kuma hare-haren wuce gona da iri kan Zirin Gaza. Rahoton wanda wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese, ta wallafa ya samo asali ne daga bayanai sama da 200 daga kasashe, kungiyoyin kare hakkin bil adama, masana ilimi da kamfanoni. Ta...
    Sojojin mamayar Isra’ila sun kai munanan hare-hare kan Falasdinawa da suka rasa gidajensu da fama da masifar yunwa, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan mutane da dama Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan ‘yan gudun hijira da kuma wadanda ke jiran agaji a zirin Gaza, inda a daren jiya zuwa safiyar Alhamis, hare-haren wuce gona da irinsu suka yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama, tare da jikkata wasu baya ga bacewar wai adadi mai yaw ana mutane a karkashin baraguzan gine-gine. Asibitin Al-Shifa ya sanar da shahadan fararen hula 11 da suka hada da yara da mata a wani sabon kisan kiyashi da sojojin mamayar Isra’ila suka aikata ta hanyar kai hare-haren bama-bamai...
    A yau Alhamis ne mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya halarci bikin bude dandalin tattaunawa kan zaman lafiya na duniya karo na 13, a jami’ar Tsinghua inda kuma ya gabatar da jawabi. A cikin jawabin nasa, Han Zheng ya bayyana cewa, a halin yanzu an samu babban sauyi a duniya, tare da fuskantar batutuwan kasa da kasa da yankuna da dama, don haka ana fuskantar kalubale a sha’anin kiyaye zaman lafiya da samun ci gaban duniya. Ya ce, tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama, da kiran samun bunkasar duniya, da kiran kiyaye tsaron duniya, da kuma kiran kiyaye al’adun duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, sun samar da ra’ayoyin Sin kan daidaita manyan...
        Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Wata Kotun Majistare da ke jihar Kano ta yanke wa fitaccen ɗan TikTok, Umar Hashim da aka fi sani da Tsulange, hukuncin ɗauri na shekara ɗaya bisa laifin aikata abinda ya saɓa da tarbiyya a bainar jama’a. Alƙaliyar kotun, Hadiza Muhammad Hassan, wadda ke zaune a Gyadi Gyadi, ta samu Tsulange da laifi na zubar da mutunci a idon jama’a bayan gabatar da hujjoji da shaidu. Ta bayyana cewa an tabbatar da cewa ɗan TikTok ɗin ya aikata laifin ne cikin gangan. Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano A hukuncin da ta yanke, ta ba da umarnin da...
    Ta la’akari da wannan yanayin da kasar Amurka ke ciki, ma iya cewa, ita kanta ta zama kamar wani dutse ne da ke fadowa, kuma tabbas wata rana zai taba kasa! (Bello Wang) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
      Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon. A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren. Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa. Da vatagarin suka hango...
    A jawabin godiya, wani mutumin yankin, Kwaghgba Isaac, ya yaba da shirin, yana mai cewa hakan zai ƙara ƙarfafa noman abinci da rage yunwa a ƙasa. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A ci gaba da sauya sheƙar da ’yan Majalisar Wakilai na Tarayya ke yi a ranar Alhamis wasu mambobi bakwai daga Jihar Akwa Ibom sun sanar da sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC mai mulki. Cikin waɗanda suka sauya sheƙa sun haɗa da shida daga Jam’iyyar PDP da kuma ɗaya daga Jam’iyyar YPP. ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Shugaban Majalisar Wakilan Tarayya Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙunsu na sauya sheƙa a zauren Majalisar a ranar Alhamis yayin zaman majalisar. ’Yan majalisar dai sun yi nuni da ƙara samun rarrabuwar kawuna da rigingimun cikin gida a cikin Jam’iyyar PDP a matsayin dalilin da ya sa suka...
    Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce wahalhalu sun yi yawa a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, wanda har ya sa mutane suka fara fatan dawowar tsohon Shugaba Muhammadu Buhari. Yayin da yake magana a birnin Abuja, Amaechi ya ce Najeriya ta taɓarɓare matuƙa, inda ya ce sauyin gwamnati ne kawai zai magance matsaloli. Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota “Farashi kayayyaki ya tashi sosai. Mutane ba za su iya siyan abinci ba. Babu kuɗi. Komai ya lalace,” in ji shi. Ya ƙara da cewa rayuwa ta yi tsanani har mutane sun fara tunawa da zamanin Buhari da muradin dawowarsa kan mulki. “Yanzu mutane na so Buhari ya...
    Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce wahalhalu sun yi yawa a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, wanda har ya sa mutane suka fara fatan dawowar tsohon Shugaba Muhammadu Buhari. Yayin da yake magana a birnin Abuja, Amaechi ya ce Najeriya ta taɓarɓare matuƙa, inda ya ce sauyin gwamnati ne kawai zai magance matsaloli. Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota “Farashi kayayyaki ya tashi sosai. Mutane ba za su iya siyan abinci ba. Babu kuɗi. Komai ya lalace,” in ji shi. Ya ƙara da cewa rayuwa ta yi tsanani har mutane sun fara tunawa da zamanin Buhari da muradin dawowarsa kan mulki. “Yanzu mutane na so Buhari ya...
    Babban hafasan hafsoshin kasar Iran Major General Abdolrahim Mousavi ya bayyana cewa idan HKI ta kuskura ta sabonta yaki da kasar Iran ta zata fuskanci maida martani mafi tsanani. Janar Musawi ya bayyana haka ne a jiya laraba a lokacinda yake hira da tashar talabijan ta almayaden ta kasar Lebanon Ya kuma kara da cewa a yakin da ya gabata wato wa’adussadik na ukku na watan da ya gabata, sojojin Iran basu fitar da dukkan makamansu su. Ko kuma dukkan karfinsu ba. Don haka idan yahudawan sun  kukura sun sake farfado da yaki da JMI sai sun hadu da martani wanda ya fi na farko zafi, Janar Musavi ya kara da cewa HKI ta dauki shekaru tana tanajin ranar da...
    Dubabban falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan ne gwamnatin HKI ta kora daga gidajensu tun bayan ta fara wani shiri wanda ta kira Katangan karfe a farkon wannan shekarar. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kungiyar Doctors without Borders wato MSF a takaice tana fadar haka a jiya Laraba. Rahoton ya kara da cewa HKI tana son korar dukkan falasdinawa da suke rayuwa a yankin yamma da kogin Jordan ne don samun damar kafa kasar Yahudawa zallah kamar yadda suke fata. Rahoton ka kara da cewa falasdinawa a garuruwan Tulkaram Jenin da kuma Nurushamne al-amarin ya fi shafa inda yahudawan suka kore falasdinawa akalla dubu 40,000 daga farkon wannan shekara ta 2025 sun kuma rusa gidajen...
    A jiya laraba ce aka gudanar da taron addu’a da kuma girmama shahidan yakin kwanaki 12 wanda HKI da Amurka suka farwa kasar Iran a ranar 13 ga watan Yunin da ya gabata. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa an gudanar da taron girmamawan ne a masallacin Imam Khomane (q) da ke nan Tehran. Labaran ya kara da cewa shahidan yakin kwanaki 12 dai sun hada da manya-manyan sojojin kasar kwamandan dakarun IRGC shahida Hussain salami, da babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Shahid Muhammad Bakri da kwamandan rundunar sojojin Khatamul anbiya (s) da ke nan Tehran Ghulam ali Rashti. Da sauransu. Sai kuma masana fasahar makamashin nukliya guda 6 da kuma wasu fararen hula wadanda...
    Ministan tsaron cikin gida na HKI Itamar Ben-Gvir ya yi kira ga babban murya kan cewa dole ne HKI ta mamaye dukka zirin gaza ta kuma kori falasdinawa da suke cikinsa. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalato Ben Gafir yana fadar haka a jiya ya kuma kara da cewa mamaye gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan da kuma shi ne kawai zai sa a samar da kasar yahudawan zalla inda babu ba falasdine ko guda a yankunan guda biyu. Kiran nasa dai ya gamu da maida martani daga yan siyasa a ciki da wajen HKI. Tun shekara ta 2023 ne gwamnatin HKI take son mamyar zirin gaza ta kuma kori Falasdiwa a yankin. Bayan yaklin...
    Kakakin majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof  ya bayyana cewa HKI zata gamu da maida martani mafi tsanani idan ta seke farfado da yaki da JMI, sannan sai sun yi nadamar fara yakin kamar yaki da kwanaki 12. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Qalibof yana fadar haka a jiya Laraba a lokacinda yake gabatar da jawabi a taron tunawa da kuma yin addu’a ga shahidan yakin kwanaki 12 wanda HKI da Amurka suka kawowa kasar. Ya ce HKI ba zata jurewa yaki mai tsawon lokaci ba, saboda Iran ta fi karfinsu, sannan wannan ne yasa gwamnatin Amurka ta shiga yakin, inda ta takaita da kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar a fordo da Natanz...
    Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara. Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya. ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato Wasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin. Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi. Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an...
    Rundunar Sarayar Kudus dake karkashin kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na Sydriot hari da makamai masu linzami da su ka yi sanadiyyar kashe da jikkata sojojin mamaya.  Su kuwa kafafen watsa labarun HKI sun samar da cewa, an tsinkayo harba makamai masu linzami guda 3 daga Gaza zuwa Sydriot. A gefe daya dakarun “Kassam” na kungiyar Hamas sun sanar da cewa sun kai wasu hare-haren da makamai masu linzami zuwa yankin Q20 a sansanin ‘yan share wuri zauna na ” Nir-Ishaq” da “Miftahim. Bugu da kari dakarun na “Sarayal-Kuds’ sun sanar da kai wa tankar yaki samfurin Mirkava hari ta hanyar wata nakiya mai karfi akan hanyar Zannah,dake gabashin unguwar Shuja’iyyah a birnin...
    Tsohon kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Muhsin Rizai ya bayyana cewa; Jagoran juyin musulunci Ayatullah sayyid Ali Khamnei ne ya jagoranci da kuma bayar da umarnin yakin “Wa’adussadiq 3” akan HKI. Dr. Muhsin Rizai wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron girmama shahidai da aka yi a jiya Laraba a babban masallacin juma’a na Tehran ya kara da cewa; A karon farko jagoran juyin musulunci ne ya rika bayar da umarni da kuma jagorantar yadda yaki da HKI ya kasance. Dr. Muhsin Rizai wanda shi ne kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran a lokacin kallafaffen yaki da Iraki, ya kuma ce; An yi aiki tare a tsakanin babbar shalkwatar soja ta “Khatamul-Anbiya” da kuma babbar cibiyar...
    Minstan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya mayar da martani da kakkausar murya akan furucin jami’ar diplomasiyya ta tarayyar turai Kaya Jallas na cewa Iran ta dakatar da shirinta na makamashin Nukiliya, yana mai cewa; Jallas ta jahilci abinda dokokin NPT su ka kunsa. Abbas Arakci ya ce; Idan manufar ganawa da kwamitin hadin gwiwa akan yarjeniyar Nukilar iran shi ne kawo karshen Shirin makamashin Nukiliyar Iran, to kuwa Jallas ta jahilci abinda yake kunshe a cikin yarjejeniyar hana yaduwar makaman Nukiliya. Ita dai babbar jami’ar harkokin wajen tarayyar turai Jallas ta rubuta sako a shafinta na X cewa; Ya zama wajibi a bude tattaunawa da sauri da Iran akan yadda za ta kawo karshen shirinta na makamashin Nukiliya, kuma...
    Wani ɗan Ghana da aka yi ƙoƙarin yaudararsa shi ma ya tsere, ya koma Ghana, inda ya kai rahoto ga hukumomi, abin da ya haifar da haɗin gwiwar ƙasashen biyu don ceton Sammed. Sakamakonhaɗin gwiwar da ’yansanda suka yi a Abuja, an ceto Sammed. Adejobi ya ce an ɗauki matakai don kama waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki domin su fuskanci hukunci. A wani samame daban, ’yansanda sun kama wasu mutane uku da ake zargi da garkuwa da mutane da kuma ta’addanci a Abuja da Jihar Kaduna. An kama su ne a ranar 29 ga watan Yuni, 2025, bayan samun sahihin bayani da kuma haɗin kai ƙarƙashin jagorancin ACP Victor Godfrey. An kama su a wurare daban-daban ciki har da...
    Jaridun kasar Amurka sun bayyana cewa; Isra’ila ta kasa cimma manufofin da ta ayyana a yaki da Iran, sannan kuma ta kara zama saniyar ware a duniya. Mujallar “Foreign Policy” ta yi ishara da sakamakon yakin da take cewa, ya zamarwa Amurka da kawarta   Isra’ila juyewar reshe da mujiya,domin harin da su ka kai wa Shirin Iran na Nukiliya bai iya kawo karshensa baki daya,maimakon haka ma sai ya jazawa Tel Aviv asarar mai yawa da kuma karfafa kishin kasa a tsakanin Iraniyawa.” Har ila yau, rahoton mujallar ta “”Foreign Policy” ya ci gaba da cewa; Asarar da aka yi a Isra’ila, tana firgitarwa”,amma a cikin Iran babu cikakken bayani akan girman barnar da aka yi- da hakan yake a...
    Ko da yake ba a bayyana irin rashin lafiyar da ta kama shi ba, wannan bayani ya kawo ƙarshen jita-jitar da ke yawo game da lafiyar Buhari, musamman bayan da mutane suka lura da jinkirin dawowarsa daga ƙasar waje. Buhari ya bar mulki a watan Mayun 2023 bayan ya kammala wa’adinsa na biyu. A lokacin da yake shugaban ƙasa, ya saba shafe lokaci a Birtaniya domin neman lafiya. Shehu dai bai faɗi ranar da Buhari zai dawo gida Nijeriya ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu...
    Ko da yake ba a bayyana irin rashin lafiyar da ta kama shi ba, wannan bayani ya kawo ƙarshen jita-jitar da ke yawo game da lafiyar Buhari, musamman bayan da mutane suka lura da jinkirin dawowarsa daga ƙasar waje. Buhari ya bar mulki a watan Mayun 2023 bayan ya kammala wa’adinsa na biyu. A lokacin da yake shugaban ƙasa, ya saba shafe lokaci a Birtaniya domin neman lafiya. Shehu dai bai faɗi ranar da Buhari zai dawo gida Nijeriya ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Tun kafin sanar da sabuwar ƙawance da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yi wa wannan haɗaka zagon ƙasa da kawo cikas ga tafiyar. Ɗaya daga cikin irin waɗannan zagon ƙasa da ake zargin wasu da yi wa wannan sabuwar haɗaka, ita ce na sanar da su rashin samun ɗakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci ƙalilan gabanin taron. NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan...
    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da cibiyar Fasaha ta Zamani ta Arewa maso Yamma da hukumar sadarwa ta ƙasa (NCC) ta gina a Kano, wadda matasa suka lalata a lokacin zanga-zangar ƙuncin rayuwa ta #EndBadGovernance a watan Agustan 2024. Ministan Harkokin Sadarwa Dr. Bosun Tijani, ne ya wakilci shugaban ƙasa a wajen bikin ƙaddamarwar. A jawabin sa, Minista Tijani ya bayyana cewa wannan katafaren aiki da gwamnatin Tinubu ta samar ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, zai iya zama babbar hanya ga matasa su tsira daga talauci idan har suka yi amfani da damar yadda ya kamata. Ya bayyana damuwarsa kan lalata cibiyar mako guda kafin a ƙaddamar da ita, duk da cewa an kammala aikin tun watan Janairu....
    Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Sun kuduri aniyar kare kan iyakokin Iran da tsaron kasar da kuma al’ummarta Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce: “Suna goyon bayan zaman lafiya, kuma ba su amince da yaki ba, amma a lokaci guda kuma, suna tabbatar da aniyarsu ta kare kan iyakokin Iran da tsaron kasarta da kuma al’ummarta.” A yau, Laraba ne, Shugaban kasar Iran Pezeshkian ya wallafa wani rubutu a shafinsa na sadarwa, inda ya jaddada babban kudirin gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na kare kan iyakokin kasar da tsaro da al’ummar kasar. Yana mai jaddada cewa: “A tushen al’adu da wayewar Iran, suna da gogewa da yawa wajen rage wahalhalun da mutane ke fuskanta.” Shugaban ya kara da...
    Iran ta nuna makamai masu linzami wadanda suka bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya A martanin da gwamnatin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran, sojojin Iran da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar sun nuna karfinsu na soji a matsayin wani bangare na “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda suka harba daruruwan makamai masu linzami na ballistic da hypersonic. A wani bangare na wannan harin na ramuwar gayya, Iran ta kai jerin hare-hare na hadin gwiwa, wanda kaso mafi tsoka na makamai masu linzami kamar Emad, Ghadr, Fattah 1, Sejjil da Khaybar. A halin yanzu rahotonni da hotuna daga haramtacciyar kasar Isra’ila suna kara fitowa kan yadda makamai masu linzamin Iran suka tarwatsa wurare masu muhimmanci na gwamnatin haramtacciyar...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani mutum, mai shekaru 35 daga ƙauyen Kunji da ke Kwadon, bisa zargin mallakar jabun kuɗi. Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama Kawu ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025, a ofishin ’yan sanda na Lawanti, sannan aka kai shi ofishin Amada domin ci gaba da bincike. Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba Ya ce an samu dalar Amurka 1,000 da ake zargin na bogi ne (kimanin Naira miliyan 1.5), da kuma Naira 10,000 a cikin kayansa. A yayin bincike, Kawu ya amsa cewa kuɗin na wani mutum ne. ’Yan sanda sun ce suna ci...
    Yau Laraba, Hukumar Kula da Fasaha ta Kasar Sin (MIIT) ta ba da rahoton yanayin tafiyar masana’antar manhajoji ta kasar daga watan Janairu zuwa Mayun shekarar 2025 da muke ciki. A cewar rahoton, masana’antar manhaja da hidimar fasahar sadarwa ta Sin tana gudana yadda ya kamata. Da farko, yawan kudaden shiga da aka samu kan sana’ar manhaja ya karu karara. Daga Janairu zuwa Mayu, adadin ya kai kudin Sin yuan triliyan 5.5788, wato ya karu da kashi 11.2% idan aka kwatanta da na makamancin lokaci a bara. Na biyu, ribar da aka samu a fannin kuma ta habaka da kashi 10% ko fiye. Daga Janairu zuwa Mayu, jimilar ribar da aka samu a bangaren sana’ar manhaja ta kai kudin Sin...
    ‘Yan tawagar jam’iyyar UDA ta kasar Kenya da suka kawo ziyara kasar Sin sun kwatanta jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da bishiyar kuka, suna cewa, “Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tamkar bishiyar kuka ce, wadda ke da ingantattun saiwoyi da ma babban karfi na warkar da kanta, tana ta fid da furanni da ‘ya’ya ba tare da tsayawa ba” “bishiyoyin kuka suna da tsawon rai na sama da shekaru dubu”. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana cikin karfinta, kuma za ta ci gaba da kokartawa domin bauta wa jama’a, tare da dogara da jama’a don cimma karin nasarori.   Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da Amurka a yankin yammacin Asiya ya kara rashin zamn lafiya a yankin. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadin haka ne a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Girka a jiya talata . Ya kuma kara da cewa hare-haren sun yu watsi da hanyar zaman lafiya da kuma zaman lumana a yankin. Ya kuma yi sanadiyyar karin tashe tashen hankula a yankin. Ministan ya bukaci kasashen duniya gaba daya su yi tir da HKI da kuma Amurka wadanda suka keta hurumin kasa mamba a MDD ba tare da wani daloli nay an haka ba. Ya ce hare-haren da...
    Wani rikicin gado a kan fili da ya ɓarke tsakanin wasu ahali biyu a ƙauyen Kopkopshe na gundumar Tunkus da ke Ƙaramar Hukumar Mikang ta Jihar Filato, ya yi sanadiyyar mutuwar mutum ɗaya tare da ƙone gidaje da dama. Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, bayan aukuwar rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu wanda sun shafe fiye da shekaru biyu ba sa ga maciji a kan asalin mai haƙƙin gadon gonar daga iyayensu. An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin Hadimin Shugaban Ƙaramar Hukumar Mikang kan harkokin yaɗa labarai, Nkat Joseph Lakai, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce...