‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
Published: 13th, October 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar wa al’ummar jihar a shirye ta ke ta ci gaba da kare mutuncin daidaikun mutane da kungiyoyin da suka sadaukar da kansu domin samar musu da sahihin bayanan sirri da za su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijar.
‘Yan sanda a jihar Neja da ma Nijeriya ƙwararru ne don haka za su ci gaba da aiki da kuma nuna basira da ƙwarewa tare da ƙa’idarta ta sirrin rashin bayyana tushen bayanansu don samun sakamako mafi girma.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman wanda ya bayar da wannan tabbacin a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna, ya bayyana cewa a kwanan baya ya halarci wani taron bita da hedkwatar ‘yan sanda ta shirya kan masu bada bayanai wato Informant domin kara kwarewarsa.
Sai dai Adamu Abdullahi Elleman ya danganta raguwar ayyukan aikata laifuka a Minna babban birnin jihar da sahihan bayanai da aka samu daga jama’a, goyon baya daga babban sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun da gwamnatin jihar Neja a karkashin jagorancin Gwamna Umar Bago, da sarakunan gargajiya da kuma matakin da ya dauka na cewa a mafi yawan lokuta yakan shiga sintiri a Minna, wanda DPO da kwamandojin yankin suka goyi bayansa.
A cewarsa sakamakon wannan yunkurin da aka yi da dama daga cikin miyagu da suka tsunduma cikin ayyukan ‘yan daba, an kama su, an kuma gurfanar da su a gaban kuliya, tare da daure su a matsayin misali ga wasu.
Adamu Abdullahi Elleman ya ci gaba da cewa, ya kuma gargadi Hakimai na yankin da su rika taimaka wa miyagu cewa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya manta sabo.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, ya kuma yabawa babbar mai shari’a ta jihar, Mai shari’a Halima Ibrahim bisa goyon bayan da ta bayar wajen ganin an samar da shari’a cikin gaggawa, tare da samun hadin kai tsakanin ‘yan sanda da sauran kungiyoyin tsaro baya ga sabon alkawari da jami’an sa da mazaje suke yi na yakar miyagun laifuka da aikata laifuka a duk lungu da sako na jihar.
Adamu Abdullahi Elleman ya kuma kara da cewa a karkashin sa a matsayinsa na sabon kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja, jin dadin jami’ansa da jami’an rundunarsa shi ne babban abin da ya fi ba da fifiko wajen kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyuka masu inganci.
INT Aliyu Lawal.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kariya Minna
এছাড়াও পড়ুন:
A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
Tukur Muhammad Fakum, daya daga cikin jagororin al’ummar ya shaida wa BBC cewa an riga an kai makura, don haka a yanzu fatan su kawai bai wuce neman wa kai mafita ba.
Ya ce ”Mu yanzu muna nan muna gangami, mai ‘yar karamar gona ya sayar, mai dan karamin gida ya sayar, in muka sayi bindigogi a ba matasa su ma su yi kokari su kare mu.
”Gwamnati ta ba mu kariya, idan kuma ba ta iyawa to ta bamu makamai a ba matasa, su matasa na iya kare rayukansu da garuruwan su,” in ji Tukur Muhammad Fakum.
Dangane da halin da irin barnar da ‘yan bindigar suka yi masu kuwa, Tukur Muhammad Fakum ya ce ”Babu dai abinci, wanda bai taba kwana masallaci ba ya yi, ka tashi ka tafi garin da ba ka taba kwana ba, ka kwana dole. Bala’in ya baci.”
Ya kuma ce lamarin rusa kusa duk wata harkar tattalin arziki a yankin.
BBC dai ta yi kokari jin halin da ake ciki daga bangaren gwamnati da jami’an tsaro, amma hakan ba ta samu ba.
Jihar Sokoto na daga cikin jihohin da matsalar ‘yan bindiga ta addaba sosai a shekarun nan, inda suke aikata barna, musamman a kananan hukumomin Isa da Sabon Birni da kuma Kebbe.
Bayan ‘yan bindiga masu biyayya ga Bello Turji da suke ayyukan su a jihar, an kuma samu bulluwar mayakan Lakurawa, wata sabuwar kungiyar da masu sharhi a kan harkokin tsaro ke gargadin cewa za ta iya zama sabuwar annoba ga jihar da ma yankin Arewa maso Yamma baki daya.
A jihar Kebbi da ke makwabtaka da Sokoto ma wasu ‘yan bindigar sun kai hari a kan jami’an tsaro, a Garin Dirin Daji da ke Karamar Hukumar Sakaba ta jihar.
Wata mazauniyar garin ta ce ”Sun kai hari a kan sansanin sojoji da na ‘yansanda, wanda ke gadi a sansanin sojojin sun harbe shi, kuma nan take Allah ya mashi cikawa.”
Ta kara da cewa ”Daga baya an turo jami’an tsaro, wadanda suka kawo dauki cikin gaggawa, kuma da alama kura ta lafa.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA