Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Published: 12th, October 2025 GMT
Sai dai duk da cewa Ousmane Dembele na kungiyar kwallon kafa ta PSG ne ya lashe gasar- Yamal ya samu nasarar kyautar gwarzon matashin dan wasa na Ballon d’Or karo na biyu a jere.
Lamine Yamal, ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yanwasa mafiya farin jini tsakanin masoya kwallon kafa, musamman ma matasa saboda karancin shekarunsa da kuma yadda yake buga wasa cikin raha.
Shekara da shekaru, duniya ta dauka cewa zama fitacce a fagen kwallon kafa na bukatar jajircewa da sadaukarwa. Saboda kafin dan wasa ya iya lashe wannan kyauta sai ya yi aiki tukuru.
Sai dai duk da nuna kuruciyarsa, hakan bai hana Yamal cimma burinsa a fagen kwallon kafa ba. A baya ya bayyana cewa: yana da burin samun Ballon d’Or masu yawa idan ya samu dama.
Matasa da dama sun so Yamal ya lashe Ballon d’Or a wannan shekara, musamman irin kokarin da ya yi a bara, da kuma lashe kyautar gwarzon matashin danwasa da ya yi a bara. Kuma rashin samun kyautar ba ta yi wa matasa da dama dadi ba.
Ana ganin samun nasara a tawagar ‘yan wasan kasar Sifaniya zai fi ba shi damar lashe kyautar fiye da kungiyarsa ta Barcelona, amma idan har Barcelona ta iya lashe gasar cin kofin zakarun turai tabbas zai iya lashewa.
Amma kuma akan fifita nasarar da dan wasa ya yi a kasarsa fiye da kungiyar da yake bugawa wasa, kuma a bayyane take Kofin Duniya na daya daga cikin manyan abubuwan da zai sa mutum ya lashe kyautar.
Saboda haka idan har Sifaniya ta lashe kofin duniya a shekara mai zuwa ta 2026, Yamal zai iya samun kyautar Ballon d’Or. Kasancewar a yanzu yadda yake da cikakken gurbi a tawagar kasar, babu yadda za a yi Sifaniya ta ci kofin ba tare da kwallayensa ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: lashe kyautar kwallon kafa
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
A safiyar Litinin ɗin nan ƙungiyar Hamas ta saki rukunin farko na ’yan ƙasar Isra’ila bakwai da ta yi garkuwa da su a Zirin Gaza.
A ɗaya ɓangaren kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako.
Tuni jami’an kungiyar agaji ta Red Cross suka shiga gidan yarin Wada a safiyar domin ɗaukar wani fursuna Bafalasdine da za fitar, wanda ke fama da rashin lafiya.
Hamas ta mika su ne ga kungiyar Red Cross a Gaza a yayin da ake da ran sako wasu ƙarin mutum 13 na gaba a Litinin ɗin nanm a cewar hukumomin Isra’ila.
Wannan na faruwa ne a yayin da Shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya taka muhimmiyar rawa a sulhun, yake ziyara a ƙasar Isra’ilan a safiyar Litinin.
Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — AtikuWannan na zuwa ne bayan yarjejeniyar zaman lafiyar da ɓangarorin biyu suka sanya hannu a kai a baya-bayan nan.
A bangare guda kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako, a matsayin ɓangarenta na musayar fursunonin yaƙin.
Ma’aikatar Harkokin Gida ta Isara’ila ta fitar da jerin sunayen mutanen da aka saki da shekarunsu:
Eitan Abraham Mor, 25 Gali Berman, 28 Ziv Berman, 28 Omri Miran, 48 Alon Ohel, 24 Guy Gilboa-Dalal, 24 Matan Angrest, 22Na gaba ake da ran muka su ga iyalansu a wani sansanin soji a Kudancin Isra’ila.
A ɗaya bangaren kuma kungiyar kula da Fursunoni ta Palastinu ta fitar da jerin sunayen mutane 1,718 da Isra’ila za ta sako.