Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
Published: 13th, October 2025 GMT
Kungiyar ‘Yan Dako ta kasa reshen jihar Jigawa ta kaddamar da Malam Muhammad Tajudeen Maigatari a matsayin sakataren kungiyar na jihar.
Da yake jawabin a lokacin bikin kaddamawar a garin Maigatari, Shugaban kungiyar na jihar Malam Nasiru Idris Sara, ya bayyana shugabanci a matsayin rikon amana a maimakon hanyar tara dukiya da alfahari, a don haka akwai bukatar sakataren ya yi aiki tukuru dan kare martabar sana’ar dako da masu yin ta.
Yana mai cewar shugabancin kungiyar zai hada kai da shugabannin kananan hukumomi da masu rike da sarautu da jami’an tsaro a matsayin abokan kawo cigaba wajen daga likkafar sana’ar dako.
Nasiru Idris Sara ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan dako a fadin jihar da su yi rijista da kungiyar domin kasacewa a karkashin inuwa daya ta yadda za su ci moriyar tanade tanaden ta, sannan su kasance masu mutunta shugabanci da kuma bin doka da oda domin inganta rayuwar su.
Ya ce yayin da kungiyar ta ke da ‘yan dako kimanin dubu 20 a karkashin ta, akwai bukatar duk ‘yan dakon da ba su da katin zabe su karbi sabo ko kuma su sabunta wanda ya bata ko ya lalace domin amfani da damar su wajen zaben shugabanni.
A sakon sa, Hakimin Maigatari Alhaji Sani Alhassan Muhammad wanda ya sami wakilcin Sarkin Kasuwar Maigatari Alhaji Muhammadu Sarkin Kasuwa, ya bukaci sabon sakataren kungiyar Malam Muhammad Tajudeen ya kasance mai nuna gaskiya da adalci wajen huldar sa da ‘yan dako da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci, inda ya bayyana murnar samun wannan mukamin.
Cikin wadanda suka halarci taron sun hada da Sarkin hatsin Maigatari, Malam Mu’azu Bako da Shugaban leburorin Dingas na Jamhuriyar Nijar Malam Lawwali Hassan.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.
Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.
Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.
DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar NejaWannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.
A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.
Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.
Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.
A watan Yuli 2025 Gwamna Umar Namadi ya gudanar da bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.
Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma samar da tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da zubar da jini.