Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
Published: 13th, October 2025 GMT
Na farko, hada kai don samar da yanayi mai kyau ga ci gaban mata. Na biyu, a karfafa abubuwan da za su habaka ingancin ayyukan mata cikin hadin kai. Kana na uku, a gina tsarin kare hakkin mata tare. Sai na hudu, a bude sabon babin hadin gwiwa tsakanin mata a duniya.
Za a gudanar da taron kolin mata na duniya a yau da gobe Talata a birnin Beijing.
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Wadanda suka amfana da horon, an ba su horon ne a fannoni daban-daban da suka hada da yin noma da takin gargajiya da kuma yin noman kayan lambu da sauransu.
Kajin gidan gona da tare da kuma tallafa masu da kayan aikin noma.
Bisa tsarin wannan haron, kowace mace daya da ta amfana da horon, an ba su tallafin Naira Naira 50,000.
Kazalika, Adeleke ya danganta wannan tallafin kudin a matsayin mayar da hankalin gwamnatinsa na taimaka wa matan jihar.
Gwamnan ya kuma jaddada muhimmcin tallafa wa mata, wanda ya sanar da cewa; hakan na da muhimanci domin inganta gobensu.
Shi kuma shugaban gidauniyar, Dakta Deji Adeleke a nasa jawabin ya bayyana cewa, shirin wanda aka yi masa lakabi da ‘Beronica Adeleke’, manufarsa ita ce domin habaka tattalin arzikin mata don su zamo masu dogaro da kansu.
Shugaban, wanda mataimakinsa Banji Adesuyi, ya wakilce shi a wajen kammala bayar da horon ya bayyana cewa, shirin sabon aiki ne da aka kirkiro da shi a jihar.
Ya sanar da cewa, wadanda suka amfana an zabo su ne daga kananan hukumomin jihar 30, inda ya kara da cewa; mata 500 da suka amfana su ne rukunin farko, amma tun da farko gidauniyar ta tsara horar da mata 1,000 ne.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA