Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
Published: 12th, October 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.
A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.
“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.
Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.
Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.
Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.
Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.
Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.
“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.
Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargadi Gwamnatin tarayya Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa ci gaba da cin ganda da ake samu daga fatar shanu na barazana ga masana’antar fata ta Najeriya wadda darajarta ta kai kusan Dala biliyan biyar.
Yayin jawabi a taron ƙaddamar da yaƙi da cin ganda da aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja, Darakta-Janar na Hukumar Bincike da Ci gaban Kayan Masana’antu, Farfesa Nnanyelugo Ikemounso, ya ce wannan dabi’a tana hana masana’antu na cikin gida samun muhimman kayayyakin da ake buƙata wajen samar da fata da kuma fitar da ita ƙasashen waje.
Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030Ikemounso ya ce kasuwar kayan fata ta Najeriya ta kai darajar dala biliyan 2.79 a shekarar 2024, kuma ana hasashen za ta haura zuwa dala biliyan 4.96 nan da shekarar 2033.
Sai dai ya yi gargadin cewa ci gaba da karkatar da fata zuwa yin ganda na iya kawo cikas ga wannan ci gaban.
Ya ce, “Daga mahangar tattalin arziki da masana’antu, fatar shanu na ɗaya daga cikin muhimman kayan masarufi a Najeriya. Ƙasarmu na da masana’antar fata mai ƙarfi wadda ke da babbar damar samar da ayyukan yi, samun kuɗaɗen waje, da kuma ƙara gudummawa ga GDP.”
“A shekarar 2024, kasuwar kayan fata ta Najeriya ta kai darajar dala biliyan 2.79, tare da hasashen ta kai dala biliyan 4.96 nan da 2033.”
“Abin takaici, ci gaba da karkatar da fata zuwa cin ganda yana hana masana’antunmu samun ingantattun kayan masarufi, yana raunana sashen yin fata da sarrafa ta, kuma yana rage matsayin Najeriya a kasuwar fata ta duniya.”
A cewarsa, darajar sarkar fata ta duniya ana kiyasta ta tsakanin dala biliyan 420 zuwa dala tiriliyan 1, kuma idan aka yi kyakkyawan tsari sannan aka inganta kayan aiki, Najeriya na iya ƙara samun kaso mai yawa daga wannan kasuwa.
Shugaban ya ce amma wannan gangami ba ya nufin hana ’yan Najeriya cin ganda, sai dai don tabbatar da cewa fatar shanu da ta sauran dabbobi ana karkatar da su zuwa amfani na masana’antu domin amfanin ƙasa baki ɗaya.
Ana ɗaukar masana’antar fata ta Najeriya a matsayin ɗaya daga cikin manyan sassan tattalin arzikin da ba na man fetur ba, wadda ke da damar zama babbar hanyar samun kuɗaɗen fitar da kaya da kuma samar da ayyukan yi.