An bayyana katin zabe a matsayin sheda da za a iya amfani da shi a muhimman wurare, kamar yadda ake amfani da fasfo da katin dan kasa a manyan kasashen duniya.

Tsohon wakilin mazabar tarayya ta Birnin Kudu da Buji, Engineer Magaji Da’u Aliyu ya yi wannan tsokaci new a wata tattaunawa da manema labarai a Dutse.

Ya bayyana bukatar aiki tukuru a tsakanin masu ruwa da tsaki dan tabbatar da cewar dukkan wadanda su ka cancanta sun karbi katin zaben.

Engineer Magaji Da’u Aliyu ya yabawa gwamnatin Malam Umar Namadi bisa kafa kwamati na musamman a karkashin mai bada shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Lawan Garba Bullet, domin zaburar da kananan hukumomi su bada gudummawar da za ta taimaka wajen samun nasarar shirin.

Ya lura cewar akwai abin damuwa bisa karancin fitowa wajen karbar katin zabe a Arewa, idan an kwatanta da alkaluman karbar katin zaben a ikko da sauran jihohin kudu maso kudu da kudu maso gabashin kasar nan duk da cewar Arewa ta fi yawan jama’a.

Magaji Da’u Aliyu ya ce yana da cikakken bayani kan gudummawar da shugabannin kananan hukumomin Birnin Kudu da Buji su ke bayarwa ga aikin bada Katin Zabe amma duk da haka akwai bukatar rubanya kokari domin cimma gagarumar nasara.

Daga nan sai ya yi kira ga matasan da su ka cika shekarun yin zabe da wadanda su ka canja wurin zama da wadanda katin zaben su ya lalace ko ya bata, da su je domin sake karbar wani katin zaben.

A cewar sa, yin haka shine zai basu damar zaben dan takarar da ya kwanta musu a rai ko kuma fidda baragurbin ‘yan siyasa daga madafun iko.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Na farko, manufofi da ka’idojin kundin mulkin MDD su kasance tushen ka’idojin dangantakar kasa da kasa, kuma jigon tsarin shari’a na duniya.

Na biyu, dole ne dokokin duniya su mutunta bambancin al’adu da tsare-tsaren shari’a na kasashen duniya, tare da tabbatar da cewa dukkannin kasashe na da matsayi iri daya, kuma ya zama dole a karfafawa kasashe masu tasowa gwiwar yin magana.

Na uku, daidaiton ‘yancin kai ya kasance tushen shari’a ta zamani a duniya.

Na hudu, nuna biyayya ga yarjejeniyoyin kasa da kasa, wata babbar ka’ida ce wajen aiwatar da shari’a a duniya, kuma dole ne dukkannin kasashe su cika alkawuransu bisa aminci da gaskiya.

Na biyar, dole ne kasashe su gaggauta tsara dokoki a sabbin fannonin da sabbin bangarorin tsaro, don samar da tsarin hadin gwiwa da shugabancin duniya a wadannan bangarori, ta yadda za su biya bukatu da kuma magance matsalolin da suka dace da bukatun kasashe.

Na shida, warware rikice-rikice ta hanyar zaman lafiya wata babbar ka’ida ce ta shari’ar duniya, kuma neman sulhu daya ne daga cikin hanyoyin da kundin mulkin MDD ta kayyade na magance rikice-rikice. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa October 10, 2025 Daga Birnin Sin An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal October 9, 2025 Daga Birnin Sin Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025 October 9, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 
  • Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya.
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
  • 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe
  • Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya