2025-07-26@08:28:47 GMT
إجمالي نتائج البحث: 3552
«ya buga kwallo»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Shugaban kasar Korea ta Arewa ya bayyana goyon bayan sag a kasar Rasha a yakin da take fafatawa da kasar Ukraine. Kafafen yada labarai na Korea ta Arewa sun bayyana cewa Kim Jong Un ya fadawa ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Layrov, a cikin xiyarar kwanaki 3 da ya kai ziyara kasar. Kasar korea ta Areawa dai ta sha taimakawa kasar Rasha da sojoji da kuma makamai ma yakin da take fafatawa da kasar Ukraine fiye da shekaru uku da suka gabata. Kim ya hadu Lavrov ne a kan iyakokin kasashen biyu na ruwa da ke Wonsan . Kasashen bi yu sun tattauna karin taimakawa juna a bangaren tsaro. KCNA ya bayyanan cewa shuwagabannin biyu sun tattauna al-amura da...
Benyamin Natanyahu firai ministan HKI ya amince da cewa gwamnatinsa ta kashe masana fasahar Nukliya na kasar Iran da dama, don haka kasar ci gaba a wannan bangaren. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Natanyahu yana fadar haka a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Amurka mai sun a FOX NEWS. Wannan ikrarin dai ya fidda shakka da ake da shi ne cewa gwamnatin HKI ce take kashe masana fasahar Nikliyar kasar kuma wannan furucin ya zama shaida a kansa a duk lokacinda al-amarin ya zaman a shari’a. Har’ila yau furucin ya tabbatar da cewa HKI tana zagon kasa wa JMI wacce shirin makamashin nukliyar ta, ta zaman lafiya ce karkashin kula na hukumar IAEA. Banda...
A wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, Usman Dako ya bayyana yadda aka kori iyalinsa, aka rusa gidansu, aka kuma tsorata matarsa da ‘ya’yansa. Ya ce gida ne da aka ware wa mahaifinsa tun zamanin marigayi Sarki Ado Bayero, amma yanzu an rusa shi ba tare da haƙƙi ba. Dako ya dage da cewa zai ci gaba da nuna biyayya ga Aminu Ado Bayero, duk kuwa da korar da aka yi masa. Har yanzu dai Sarki Sanusi bai ce uffan ba game da lamarin, kuma ba a samu wani bayani daga majalisar Sarakunan ba. Ana sa ran za a ci gaba da sauraron shari’ar nan ba da jimawa ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun...
Kakakin ma’aikatar sharia a nan Iran ya bayyana cewa shi bai da wata masaniya dangeneda cewa HKI ta kai hare-hare kan gidan yarin Evin na Tehran ne don kashe ma’aikatanta da aka kama aka kuma tsare a gidan yarin. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin na ma’aikatar sharia yana fadar haka a nan Tehran ya kuma kara da cewa, a cikin yakin kwanaki 12 da ya gabata jami’an tsaron kasar Iran sun kama ma’aikatan leken asirin na HKI da dama a lokacin, suna aikawa Haramtacciyar kasar Rahotanni a cikin yakin. A lokacinda aka tambayeshi kan cewa kun gano cewa hare-haren ranar 22 ga watan Yunin da ya gabata a cikin yakin kwanaki 12, HKI ta kai...
Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana hukumar kula da shige da fice ta Najeriya a matsayin matakin farko na tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyi a kasar. Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin daliban jami’ar Immigration da ma’aikatan kwalejin Sokoto a ziyarar ban girma a fadarsa. Ya yi kira da a samar da jami’an shige-da-fice don duba bakin haure da ke barazana ga zamantakewa da ci gaban tattalin arzikin kasar. Ya kara da cewa galibin ‘yan kungiyoyin ta’addanci irin su Lakurawas da Boko Haram ba ’yan Najeriya ba ne. Jagoran ya bayyana cewa, hukumar shige da fice na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da tsaron...
Shugaban kasar Korea ta Arewa ya bayyana goyon bayan sag a kasar Rasha a yakin da take fafatawa da kasar Ukraine. Kafafen yada labarai na Korea ta Arewa sun bayyana cewa Kim Jong Un ya fadawa ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Layrov, a cikin xiyarar kwanaki 3 da ya kai ziyara kasar. Kasar korea ta Areawa dai ta sha taimakawa kasar Rasha da sojoji da kuma makamai ma yakin da take fafatawa da kasar Ukraine fiye da shekaru uku da suka gabata. Kim ya hadu Lavrov ne a kan iyakokin kasashen biyu na ruwa da ke Wonsan . Kasashen bi yu sun tattauna karin taimakawa juna a bangaren tsaro. KCNA ya bayyanan cewa shuwagabannin biyu sun tattauna al-amura da...
A cikin wannan mako dai an yi ta murna da farin ciki a fadin jihar Kano inda dubban ‘yan fansho suka fara karbar kudaden fansho da garatuti da aka dade ba su yi ba. Kudaden da aka fitar na ‘yan fansho na jihar Kano, sun kasance wani babban ci gaba a kokarin da gwamnan ke ci gaba da yi na biyan bashin zunzurutun kudi har naira biliyan 48 na kudaden alawus-alawus da kuma na mutuwa da ya gada daga gwamnatocin baya. ‘Yan fansho da suka karbi kudadensu sun nuna matukar godiya ga Gwamna Yusuf kan abin da mutane da yawa ke kira a matsayin hanyar rayuwa bayan shekaru da aka yi watsi da su. Daga cikin...
Shirin Samar da Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya sanar da dakatar da bayar da tallafin abinci a ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka da ke fama da rikici. Hakan dai na zuwa ne a sakamakon rage tallafin da Amurka ke bayarwa na kuɗi ƙarƙashin Hukumar USAID, wanda hakan ke kawo cikas ga ayyukan wannan ƙungiyar. Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanci An sanya dokar hana fita a Adamawa Duk da cewa lokaci ya bambanta daga ƙasa zuwa ƙasa, ana hasashen kayan abinci za su isa zuwa kusan watan Satumba a mafi yawan ƙasashen da abin ya shafa, wanda hakan zai bar miliyoyin mutane masu rauni cikin halin rashin tallafin gaggawa, a cewar WFP. “Muna...
‘Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta kama wasu da ake zargi da aikata laifuka, ta kwato bindigogi, da kuma kama sama da Naira miliyan 11 da ake zargin kudin fansa ne a cikin wannan lokaci. Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Adekimi Ojo ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Ilorin. A cewarsa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar kungiyoyin tsaro na cikin gida sun cafke wani kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Idirisu Sariki a Okuta, karamar hukumar Baruten. Ojo ya ce ana kyautata zaton Sariki na da alaka da sace-sacen mutane da dama a yankunan kan iyaka a jihar Ya bayyana cewa, a yayin samamen jami’an tsaro...
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Katagun ta tarayya a jihar Bauchi Alh. Awwalu Abdu Gwalabe, ya bayar da hujjar cewa tattalin arzikin Najeriya na da karfin da zai iya dorewar karin jihohi 12. Ya bayyana haka ne ga manema labarai a wajen taron jin ra’ayin jama’a kan sake duba kundin tsarin mulkin 1999 a Arewa maso Gabas a Gombe Alh. Awwalu Gwalabe, ya ci gaba da cewa, idan har Gwamnatin Tarayya za ta iya kashe Naira tiriliyan 17 wajen gina titin lagos-calabar kadai, hakan na nuni da cewa tattalin arzikin zai iya dorewar samar da karin jihohi. Ya ce sama da shekaru arba’in ne al’ummar shiyyar katagun a jihar Bauchi suke ta tada jijiyoyin wuya na ganin...
Shugaba Trump da abokansa sun ce sun gano cewa ana tafka almundahana da zamba a hukumar. Rahoton na zuwa ne yayin da gomman shugabannin duniya ke taro a Birnin Sabeilla na kasar Sifaniya cikin makon nan domin tattauna batun katse tallafin, wanda ya fi kowane bayar da agaji a duniya. Bayan nazarin bayanan alkaluman tallafin hukumar a kasashe 133 a duniya, binciken ya kiyasta cewa tallafin USAID ya rage mutuwar mutum miliyan 91 a kasashe masu tasowa tsakanin 2001 zuwa 2021. Sun kuma yi amfani da wani kiyasi wajen hasashen yadda rage tallafin da kashi 83% adadin da gwamnatin Amurka ta sanar a farkon wannan shekara na iya shafar adadin masu mutuwa. Rahoton ya ce katse tallafin zai haifar da...
3. Girman Lambar Yabo da Za a Baiwa Zakaran Gasar Kungiyar da ta lashe kofin za ta samu fam miliyan 97 daga hukumar FIFA. Hakanan, za ta sanya tambarin kofin na tsawon shekaru 4, sabanin shekara 1 da ake yi a baya. 4. Muhimmancin Wasan ga Duka Kungiyoyin Ga PSG, wannan kofi na iya zama jaddawalin nasarar su bayan barin Kylian Mbappé. Ga Chelsea kuma, nasarar na iya maido da su sahun gaba a turai da duniya gaba daya. 5. Kallon Duniya na Kan Wasan Wasan zai jawo hankalin masu sha’awar kwallon kafa a duniya, musamman ganin yadda kowanne bangare ke dauke da fitattun ‘yan wasa da kocin da ke kokarin kafa tarihi. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna...
An haifi Peter Rufa’i a ranar 24 ga watan Agusta, 1963, a Oshodi, Legas, a wani gidan sarautar gargajiya, Mahaifinsa shi ne sarkin kabilar Idimu a Jihar Legas, duk da hasashen da ake yi na cewa zai yi gadon sarautar gidansu, Rufa’i ya yi watsi da sarautar don ci gaba da fuskantar abin da yake sha’awa wato kwallon kafa. 2. Ya yi Wasa A Manyan Kungiyoyin Kwallon Kafa A Kasashen Turai Rufa’i ya fara sana’ar kwallon kafa a kungiyoyin gida Nijeriya kamar Storeery Stores da Femo Scorpions kafin ya tsallaka zuwa kasar waje, ya taka leda a kungiyoyi a kasar Benin (Dragons de l’Ouémé), Belgium (Lokeren, Beberen), Netherlands (Go Ahead Eagles), Portugal (Farense, Gil Bicente), da Spain (Hércules, Deportibo La...
Dakarun rundunar “Shahid Izzuddin al-kassam’ da kuma ” Sarayal Kuds” sun sanar da kai jerin hare-hare akan sansanonin ‘yan sahayoniya a yankuna mabanbanta na Gaza. A bayanin da dakarun ” Kassam” su ka fitar sun bayyana hare-hare masu yawa da su ka kai wa ‘yan mamaya, da su ka hada da tarwatsa motocin buldoza biyu samfurin D9 a unguwar Zaituna a cikin birnin Gaza. Haka nan kuma sun kai wani harin a ranar 6 ga watan Yuli wanda su ka rusa tankar yaki ta “Mirkava” ta hanyar amfani da wata nakiya mai tsananin fashewa. Bugu da kari , Kassam ta ce a ranar 9 ga watan Yuli din ta kai wani harin akan sansanin da kwamandoji masu bayar da umarnin...
Gwamnatin Adamawa ta ayyana dokar ta baci ta hana zirga-zirgar mutane na tsawon sa’o’i 24 a Karamar Hukumar Lamurde da ke Kudancin jihar. Bayanai sun ce wannan lamarin na zuwa ne bayan samun rahotannin mutuwar kimanin mutane hudu a wani sabon rikici na kabilanci da ya auku a yankin. Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC DW ta ruwaito kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje yana ba da shaidar matakan da suke dauka domin dakile rikicin. Kazalika Kwamishin ’yan sandan jihar, Dankombo Morris ya kaddamar da kwamitin bincike kan musabbabin afkuwar lamarin. Kana Kwamishinan ya ba da umarnin jibge ’yan sandan kwantar da tarzoma a yankin...
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dawo gida Najeriya bayan kwashe makonni biyu, inda ya ziyarci ƙasashen Saint Lucia da Brazil. Mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ne ya sanar da hakan a shafinsa na X. Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello Shugaba Tinubu ya bar Najeriya ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025 don ziyarar aiki a waɗannan ƙasashe biyu. Da farko ya je Saint Lucia domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da ƙasashen yankin Caribbean, da kuma ƙara haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen kudancin duniya. A ranar 4 ga watan Yuli, Tinubu ya tashi daga Saint Lucia zuwa Brazil, inda ya halarci taron BRICS...
Ko za ka iya fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka? An haife ni a Unguwar Adakawa cikin birnin Kano, na yi makarantar firamare a Adakawa, daga nan kuma na tafi zuwa makarantar sakandire (Gwammaja One), bayan na sauke Alkur’ani, daga baya na tafi sai na wuce zuwa ‘School of Health Technology’ ta Kano. Bayan nan, sai kuma na tsunduma harkokin kasuwanci da siyasa, kazalika ina da mata biyu da kuma ‘ya’ya goma a halin yanzu. Kamar wane irin kasuwanci kake yi? Ina harkar takalma ‘yan Kofar Wambai, wadda ita ce sana’ar dana fara koya, sannan kuma ita ce sana’ar da dangina suke yi. Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood? Tun ina yaro...
Har ila yau a wannan rana, Wang Yi ya gana da ministan harkokin wajen Sri Lanka Vijitha Herath a birnin na Kuala Lumpur. Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya mai da martani a yau Asabar game da furucin da Philippines ta yi kan sanarwa game da bikin cika shekaru 9 da fitar da hukuncin takkadamar “Philippines v. China”, inda ya bayyana cewa, “hukuncin” ya saba wa ka’idojin dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar MDD kan batun teku, kuma ya sabawa ainihin gaskiyar dake tattare da batun tekun kudancin kasar Sin, haka kuma ba shi da wata daraja ko amfani.(Safiyah Ma) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin...
Eh, wasu mata suna daukar lambar motar duk wanda ya yi musu kyau ko ya zo da motar alfarma, su kai wa malami ko boka domin a janyo hankalinsa ya zo neman aurensu. Hakan kuskure ne babba, ba daidai ba ne a nemi aure ta hanyar sihiri ko dabara marar tsarki. Duk wata riba da ke tattare da hakan ba ta da karko, kuma tana iya dawo da akasin abin da aka nema, kamar rashin samun auren kwarai da tsayayye, zama da mutumin da ba da gaske yake ba, daukewar albarka daga rayuwa, fushin Allah da rushewar aure cikin lokaci. Shawara ga masu haka; ku dogara da addu’a, tarbiyya da hakuri, idan aure naku ne, zai zo da sauki cikin...
Ya jaddada buƙatar samar da tsarin adalci da zai bai wa ƙasashe masu tasowa damar cin moriyar ci gaban fasaha da samun rance cikin sauƙi daga ƙasashen duniya. Ya kuma bayyana yadda Afirka ke fuskantar manyan matsalolin muhalli duk da cewa ba ta fitar da gurbataccen hayaƙi sosai. A gefe guda kuma, Tinubu ya bayyana shirye-shiryen gyaran da gwamnatinsa ke yi, ciki har da amfani da makamashi, yaƙi da sauyin yanayi, gina birane da kuma inganta harkar kiwon lafiya ga kowa. Ya ce Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da sauran ƙasashe masu tasowa. Jawabin Tinubu a taron BRICS na 2025 ya nuna matakin farko da Nijeriya ta taka a matsayin ƙasa mai ƙawance da BRICS. Nijeriya ta...

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: An mika fayil ɗin haɗin gwiwa tare da Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ga kwamitin koli na tsaron ƙasa Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a wata ganawa da jakadun kasashen waje da na kasa da kasa cewa: Iran bangare ce a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta “NPT” kuma tana yin aiki da tanade-tanaden da aka yi mata, amma idan aka yi la’akari da sabbin yanayi da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, hadin gwiwarta da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA za ta dauki wani sabon salo. Yayin da yake ishara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana ci gaba...

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kama ‘Yan Leken Asirin Isra’ila A Lardin Mazandaran Na Kasar Iran
Dakarun juyin jaya halin Musulunci ta Iran sun kama wani wakilin hukumar leken asirin Isra’ila Mossad a arewacin kasar Iran Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun sanar da kame wani jami’in hukumar leken asirin haramtacciyar kasar Isra’ila “Mossad” a lardin Mazandaran (arewacin kasar Iran), wanda ke shirin kai harin ta’addanci a cikin kasar. Sanarwar da dakarun kare juyin juya halin suka fitar ta bayyana cewa: wani ma’aikacin fage na makiya da ke shirin aiwatar da ayyukan ta’addanci ta hanya kai tsaye wajen jagorantar masu adawa da Iran a kasashen waje, an kama shi ne a wani gagarumin samame da jami’an leken asirin na Karbala suka kai, kafin ya aiwatar da duk wani aikin ta’addanci. Sanarwar ta kara da cewa:...
Gwamantin kasar Mauritaniya ta musanta cewa shugabanta ya gana da Netanyahu, ta yi kira ga tashar Al Arabiya da ta tabbatar da sahihancin rahoton kafin watsa shi Ministan al’adu da sadarwa na Mauritaniya kuma mai magana da yawun gwamnatin kasar Hussein Ould Maddou ya musanta sahihancin rahotannin ganawar da ake zargin shugaban kasar Mauritaniya da Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu. Kamfanin dillancin labaran Jamus ya nakalto ministan na cewa rahoton da tashar Al Arabiya ta watsa game da ganawar da ake zargin shugaba Mohamed Ould Ghazouani da Fira ministan Igwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ba shi da tushe balle makama. Ya yi nuni da cewa, labaran ba su da inganci, inda ya yi kira ga tashar Al-Arabiya da ta...
Sanata Ireti Kingibe, wacce ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, ta fice daga jam’iyyar LP zuwa ADC. Da ta ke magana da ’yan jarida a Abuja, ta ce wannan matakin nata wani shiri ne na tunkarar babban zaɓen 2027. Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano “Ni cikakkiyar mamba ce ta ADC yanzu,” inji ta. Da aka tambaye ta ko tana da ƙwarin gwiwa game da shugabancin ADC da haɗin gwiwar da suke ƙoƙarin ginawa, ta ce jam’iyyar na ci gaba da samun tagomashi. Tace kowace tafiya a sannu ake binta wanda daga bisani ta ke girma. Wasu sun nuna damuwa cewa wannan...
Sanata Ireti Kingibe, wacce ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, ta fice daga jam’iyyar LP zuwa ADC. Da ta ke magana da ’yan jarida a Abuja, ta ce wannan matakin nata wani shiri ne na tunkarar babban zaɓen 2027. Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano “Ni cikakkiyar mamba ce ta ADC yanzu,” inji ta. Da aka tambaye ta ko tana da ƙwarin gwiwa game da shugabancin ADC da haɗin gwiwar da suke ƙoƙarin ginawa, ta ce jam’iyyar na ci gaba da samun tagomashi. Tace kowace tafiya a sannu ake binta wanda daga bisani ta ke girma. Wasu sun nuna damuwa cewa wannan...
Ya tunatar da cewa a bara, Antoni-Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a ya nemi fassarar doka daga Kotun Ƙoli, inda kotun ta tabbatar da cewa kundin tsarin mulki ya tanadi ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi. “An samu hukunci daga babbar kotun ƙasa da ke nuna cewa kundin tsarin mulkin mu ya tanadi buƙatar ƙananan hukumomi su samu ’yancin kai – su kasance masu cikakken iko da damar aiki a fannoni daban-daban, ko siyasa ko kuma kuɗi,” inji shi. A cewar sa, bai wa ƙananan hukumomi dama za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya a matakin ƙasa da kuma samar da cigaba a cikin al’umma. Idris ya nuna damuwa kan yadda tsarin ƙananan hukumomi ya raunana a tsawon lokaci,...
Wasu da ake zargin Jami’an Hukumar Farin Kaya (DSS), sun kama fitaccen mai barkwancin nan a kafafen sada zumunta, Bello Habib Galadanci, wanda aka fi sani da Ɗan Bello, a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano. Sun kama shi ne bayan isowarsa filin jirgin saman, wanda hakan ya jawo hankalin mutane da dama, ciki har da fasinjoji da ma’aikatan filin jirgin. DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos Sai dai Ɗan Bello cikin wata hira ta wayar tarho da ya yi da kafar DCL, ya bayyana abin da ya faru, inda ya ce: “Dana sauko wasu mutane wanda kana ganinsu ka san hukumomi ne...
Mai da hankali sosai kan dabaru:Kara bada muhimmanci ga yadda za a inganta mu’amala da tuntuba tsakanin juna,hada kai domin ayi aiki tare, da kuma maganin matsala lamarin da shi ne ginshikin yadda ma’aikata za su cimma burinsu. Lamarin kimiyya,fasaha,da kuma ilimin injiniya (STEM) Yadda za a shirya ko tsara dalibai yadda zasu cimma burin abinda suke son su zama a gaba,manufa ayyukan da suke son yi,ko sun shafi kimiyya,fasaha,ko kuma abinda ya shafi injiniya ne da lisssafi,domin wadannan lamurran wasu bangarori ne da suke samr da ci gaan tattalin arziki Dabarun koyarwa:Wadanda suka hada da hanyar gargajiya da kuma,ta kafafen sadarwa na zamani,domin kuwa hakan ne kadai zai iya samar da hanyoyi ko dabarun koyarwa. Lamarin lafiyar da ya...
Ƙungiyar Malaman Jami’a ta Ƙasa (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Yobe (YSU), ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗaukar musu. Waɗannan alƙawura sun haɗa da ƙarin albashi, biyan bashin da suke bi, da kuma barin jami’ar ta riƙa gudanar da harkokinta da ƙashin kanta. Lakurawa sun kashe ’yan sanda 3 a Kebbi Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos Shugaban ASUU na Jami’ar Yobe, Dokta Ahmed Karage, ya bayyana hakan bayan kammala wani taro da suka gudanar. Ya ce sun fara yajin aikin ne bayan dogon lokaci da suka ɗauka suna tattaunawa da gwamnati, amma ba su cimma matsaya ba. “Mun kwashe watanni muna magana da gwamnati, amma abin...
Ƙungiyar Malaman Jami’a ta Ƙasa (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Yobe (YSU), ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗaukar musu. Waɗannan alƙawura sun haɗa da ƙarin albashi, biyan bashin da suke bi, da kuma barin jami’ar ta riƙa gudanar da harkokinta da ƙashin kanta. Lakurawa sun kashe ’yan sanda 3 a Kebbi Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos Shugaban ASUU na Jami’ar Yobe, Dokta Ahmed Karage, ya bayyana hakan bayan kammala wani taro da suka gudanar. Ya ce sun fara yajin aikin ne bayan dogon lokaci da suka ɗauka suna tattaunawa da gwamnati, amma ba su cimma matsaya ba. “Mun kwashe watanni muna magana da gwamnati, amma abin...
Mai bawa jagoran Juyin Juya halin musulunci Imam Sayyid Ali Khamina’i, shawara Dr Ali Larijani ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran tana nazarin sakon gwamnatin Amurka na bukatar a farfado da tattaunawar shirin makamashin Nukliyar kasar tsakaninsu. Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya nakalto Dr Larijana yana cewa gwamnatin kasar Iran tana shakkar Amurka a cikin duk abinda zai hada su musamman bayan yaki kwanaki 12 da ita Amurka da kuma HKI suka dora mata. Dr Larijana ya fadawa tashar talabijin ta Aljazeera na kasar Qatar kan cewa, HKI da Amurka sun farwa kasar Iran da yaki ba tare da wani dalili ba, tana ma cikin tattaunawa da Ita kan shirin ta na makamas suka yi hakan. Suka...
Jaridar NYT ta kasar Amurka ta bayyana cewa firai ministan HKI Benyamin Natanyaho da gangan yake tsawita yaki a Gaza don tsawaita zamansa a kan kujerar shugabancin kasar. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani binciken da Jaridar New York Times ta yi, inda take cewa Natanyahu ya san cewa matukar ya sauya matsayinsa na shugaban gwamnatin HKI to kuwa sammashin kamasi da kuma tuhume-tuhumen da ake masa zasu tashi wadanda zasu zama masa matsala, kuma a lokacin hatta gwamnatin Amurka ba zata iya yi masa wani taimako ba. An fara yaki a Gaza ne a ranar 07 ga watan octoban shekara ta 2023 . daga lokacin ya zuwa yanzu sojojin Natanyahu sun kashe falasdinawa kimani 57,000....
Ali Mohammad Sabeghi, tsohon jami’in bangaren al-adu na ofishin jakadancin kasar Iran a kasar China ya karbi kyautar ‘Jakadan Abota’ na kasar China a wannan shekara ta 2025M. A bikin bada irin wannan kyauta karo na biyu. Labarin ya kara da cewa dangantaka tsakanin JMI ta kuma China yana daga cikin abota mafi kyau tsakanin kasashen yankin da kasar China. Labarin ya kara da cewa girmama kasar Iran ta wannan kyautar yana daga cikin al-amuran da zasu kara dankon zumunci tsakaninta da Tehran. Hukumar al-adu na kasar China ta bayyana cewa ta samar da irin wannan kyautar ne don karfafa danganta kasar China da da sauran kasashen duniya musamman kasashen Asia. A shekarar da ta gabata dai wannan kyauta ta...
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya ja kunnen shuwagabannin kasashen yammacin Turai kan shiga yaki da kasar Rasha. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Lavrov yana fadar haka, a jiya Jumma’a. Ya kuma kara da cewa, labaran da suke isa kunnensa daga biranen Landan, Paris da kuma Berlin sun tabbatar masa da cewa, kasashen suna shirin yaki da kasar Rasha. Ya ce, Rasha ta sha fadawa kasashen yammacin Turai, ci gaba da goyon bayan kasar Ukrai zai jawosu zuwa yaki da kasar Rasha. Yaki wanda rabuwamma da irinsa tun bayan yakin duniya na II. Ya shay a sha fada masu kan cewa makaman da suke turawa Kiev daga karshe ba zai taba samar da zaman...
Ana zargin wani direban tirela ya gudu da buhunan masara 463 da aka aike shi da su, bayan da ya bai wa ɗan rakiyarsa guba a cikin shayi a yankin Maraban Jos da ke Jihar Kaduna. Wani ɗan kasuwa da ke safarar hatsi daga Jihar Kano zuwa kamfanoni a sassa daban-daban na Nijeriya, Injiniya Jamilu Haruna, ya shaida wa Aminiya cewa direban da ya ɗora wa masara buhu 463 domin kaiwa kamfanin Olam da ke Ilorin a Jihar Kwara, ya gudu da kayan. “Kuɗin kayan sun kama Naira miliyan miliyan ashirin da ɗaya da dubu ɗari shida da tamanin da shida da ɗari huɗu. “Wallahi jarin nawa ke nan ɗungurungum na dora a motar,” in ji ɗan kasuwar, wanda ya...
Ya kara da cewa, Asusun ya kuma gano fannonin aikin noman kasar da ya kamata a kara bunkasa su, wanda hakan ya sanya Asusun ya dauki wannan mataki. Ya ci gaba da cewa, duba da irin amfanin gonar da manoma ke nomawa a kasar, musamman kananan manoma da kuma ribar da suke samu daga fannin, wani abu ne da Asusun ya dauka da ke da matukar muhimmanci, wanda kuma hakan ne ya kara bai wa Asusun kwarin guiwar shirin fara kaddamar da aikin. Shi kuwa a nasa jawabin, Lanre Wilton-Wadell, mai taimaka wa Babban Sakataren a Asusun, ya yi bayani kan yadda za a gudanar da aikin. Ya bayyana cewa, Asusun zai bayar da kashi 100 na Irin noma da...
Sojoji sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane ɗauke da tsabar kuɗi Naira miliyan 13 a kan hanyar Kaduna zuwa Jos a Jihar Kaduna. Dakarun Rundunar Operation Safe Haven sun kuma ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai 30 a hannun ɗan ta’addan a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna. Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya ce dubun ɗan ta’addan ta cika ne a wani shingen bincike da ke yankin Agameti a kan babbar hanyar Wamba zuwa Jos. Manjo Zhakom ya ce a ranar Laraba, sojoji suka tsayar da wata mota ƙirar Volkswagen Golf da ke ɗauke da mutum uku, amma kafin ta ƙaraso inda za ta tsaya, biyu daga cikin mutanen suka fice suka tsere. Sojoji sun...
Sojoji sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane ɗauke da tsabar kuɗi Naira miliyan 13 a kan hanyar Kaduna zuwa Jos a Jihar Kaduna. Dakarun Rundunar Operation Safe Haven sun kuma ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai 30 a hannun ɗan ta’addan a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna. Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya ce dubun ɗan ta’addan ta cika ne a wani shingen bincike da ke yankin Agameti a kan babbar hanyar Wamba zuwa Jos. Manjo Zhakom ya ce a ranar Laraba, sojoji suka tsayar da wata mota ƙirar Volkswagen Golf da ke ɗauke da mutum uku, amma kafin ta ƙaraso inda za ta tsaya, biyu daga cikin mutanen suka fice suka tsere. Sojoji sun...
Ana zargin wani ɗalibi da ke shekarar ƙarshe a jami’a da ƙona budurwarsa mai ɗauke da tsohon ciki a Jami’ar Fatakwal da ke Jihar Ribas. Wanda ake zargin da budurwar tasa mai suna Cynthia Chukwundah, dukkansu ɗaliban ajin ƙarshe ne a jami’ar. Ana zargin matashin ya ƙona Cynthia mai shekara 32 ne ta hanyar wata mata ruwan batir, daga bisani ta ce ga garinku nan. Cynthia ta gamu da ajalinta ne bayan saurayinta Sunny Amadi ya yi mata wannan aika-aika a gidansu da ke layin Okoro unguwar China da ke Birnin Fatakwal. Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL Wani ganau da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida...
Rahotanin sun bayyana cewa Shettima ya ziyarci Kano ne don yin ta’aziyyar rasuwar hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu kwanan nan, da kuma jajanta wa mutanen Kano kan wannan rashi. Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa a irin wadannan manyan taruka a Nijeriya, an saba ganin shugabannin jam’iyya da goyon baya su tarbi manyan jami’ai kamar mataimakin shugaban kasa, amma lamarin ya bambanta yayin ziyarar Shettima, wanda ya haifar da zazzafar muhawara. Da yake musanta cewa akwai rikice-rikice na cikin gida a jam’iyyar, sakataren APC a Kano, Ibrahim Zakari Sarina, ya shaida cewa rashin halartar shugabannin jam’iyyar a ziyarar ta’aziyya da mataimakin shugaban kasa ya kawo Kano ya faru ne sakamakon rashin sadarwa. “Mun san cewa ziyarar...
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen jamhuriyar musulunci ta Iran Dr. Isma’ila Baka’i ya ce; Amincewa da aikata zalunci, ya yi daidai da hada baki da mai aikata shi.” Kamfanin dillancin labarun “Mehr” ya nakalto Dr. Baka’i wanda ya wallafa sako a shafinsa na X cewa; Shugaban gwamnatin kasar Jamus yana ci gaba da nuna goyon baya ga munanan ayyukan da HKI take aikatawa wanda yake cin karo da yarjeniyoyin MDD da kuma dokokin kasa da kasa.” Haka nan kuma Dr. Baka’i ya ce; Abinda Jamus din ta aikata zai mayar da ita wacce za ta amsa tambayoyi a matsayin wacce take yin zuga a aikata laifi. A lokacin da HKI ta fara kawo wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran hare-hare dai shugaban...
Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), ya ce ya fara tunanin yiwuwar sayar da matatun man ƙasar nan. Shugaban kamfanin, Bayo Ojulari ne, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da Bloomberg. Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ya ce yanzu haka kamfanin yana sake duba yadda ake gudanar da matatun, kuma ana sa ran kammala wannan nazari kafin ƙarshen shekara. Da yake magana a taron OPEC karo na tara da aka yi a Birnin Vienna, na ƙasar Austria, Ojulari ya ce gyaran tsofaffin matatun gwamnati ya wuce yadda ake tsammani. Najeriya na da matatu huɗu;...
An dai yi ta tsokaci kan cewa ko Obi zai amince da mukamin mataimakin shugaban kasa tare da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, kamar yadda ya yi a 2019. Obi ya ce, “Takarar shugaban kasan Nijeriya zan yi a 2027, kuma na tabbatar da cancanta.” A kan ko zai hakura ya zama mataimakin takarar Atiku a 2027, Obi ya bayyana cewa, “Wannan abun wasa ba ne, babu wanta ya tattauna hakan. Mutane ne kawai yin irin wannan tunani. Amma a zahirin gaskiya babu wanda ya bayyana hakan.” Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya kuma jaddada cewa har yanzu yana shi mamba ne a jam’iyyar LP. LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi yana daga cikin shahararrun mutane a cikin hadakar ADC da...
Kwanan baya, jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te ya gabatar da jawabai masu taken wai “jawabai 10 game da hadin kan al’umma”, da nufin ba da ingantacciyar hujja ga ra’ayinsa na shirme game da ballewar Taiwan daga kasar Sin, tare da yaudarar jama’ar yankin da kuma sauran al’ummun duniya. Kowa ya san yankin Taiwan wani bangare ne da ba za a iya raba shi da kasar Sin ba, kuma wannan shi ne matsaya daya da al’ummun Sinawa da yawansu ya kai biliyan 1.4 ciki har da jama’ar yankin Taiwan da yawansu ya kai miliyan 23 suka dauka, wanda kuma ra’ayi ne daya tilo da kasashen duniya suka cimma matsaya a kai. Sanawar Alkahira da sanarwar Potsdam da dai sauran takardun shari’a sun aza ingantaccen tubali ga dokar kasa...
A dokar hukumar zabe ta 2010 sashe na 124, biyan kudi ga wani a matsayin cin hanci a kowane irin zabe ko karbar kudi ko kyauta domin jefa kuri’a ko hana jefa kuri’a a kowane zabe babban laifi ne da ke da hukuncin tarar naira dubu 500, 000 ko daurin watanni 12 a gidan gyaran hali ko kuma duka biyu. A kowane zabe kama daga na shugaban kasa zuwa kansila, Hukumar Zabe da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa na fuskantar kalubale daga masu sayen kuri’a da ke canzawa masu zabe zaben ra’ayin kan su zuwa zaben wanda aka ba su kudi ko ma kin yin zaben. Duk da kama masu sayen kuri’a da hukumomin yaki da cin hanci...
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta bayyana dalilin da ya sa ta gayyaci malamin addini Sheikh Lawal Triumph. A wata sanarwa da ta fitar, ’yan sanda sun ce sun sani cewa wasu daga cikin wa’azozin da Sheikh Triumph ke yi suna haddasa rashin jituwa a tsakanin al’ummar jihar. Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote Rundunar ta ce kowa na da ’yancin faɗin albarkacin bakinsa, amma dole ne komai ya kasance bisa doka. Saboda haka ne Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, ya gayyaci Sheikh Lawal Triumph don tattaunawa da jami’an gwamnati, shugabannin addini da na al’umma. Manufar...
Tashar talabijin din “Cane” ta HKI ta bukaci Amurka da ta kafa kawance mai fadi na kasashe domin fuskantar kasar Yemen. A yayin ziyarar da Fira ministan HKI, Benjamin Netanyahu a Amurka ne dai ya bijiro da wannan bukatar, kamar yadda rahoton tashar talabijin din ta “Cane” ya ambata. Rahoton ya kuma ce, Jami’an HKI sun sanar da Amurka cewa, ci gaba da hare-haren Yemen, ya tashi daga zama matsalarta ita kadai, don haka da akwai bukatar kai hare-hare na hadin gwiwa da Amurka da kuma shigar da kasashen wannan yankin da kuma wasu na duniya.” Tun daga 2023 ne sojojin Yemen suke kai wa jiragen ruwa na HKI hare-hare a cikin tekun “Red Sea” ko kuma wadanda su ka...
Rundunar sojan mamaya ta sanar da kashe daya daga cikin jami’an sojojinta dake karkashin rundunar “Golani” a yankin Khan-Yunus dake Gaza. Da safiyar yau Juma’a ne dai sojojin mamayar HKI su ka snar da cewa wani daga cikin mayakansu mai mukamin Captain ya halaka a Gaza, kuma tuni sun bude bincike akan abinda ya faru. Rahoton tashar talabijin din ” Cane” ta HKI ya ambaci cewa, sojan da aka kashe yana cikin wadanda su ka kai hari a garin Khan-Yunus a jiya Alhamis. Sojojin mamaya sun kai hari ne a cikin wani gida a ci gaba da kashe ‘yan gwgawarmaya da suke yi, sai dai ginin gidan ya rufta da su, bayan da nakiyar da take cikinsa ta fashe. Tun...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Ministar Raya Al’adu, Hannatu Musawa, ta ce ya kamata shugabancin ƙasar nan ya ci gaba da kasancewa a hannun ’yan Kudu domin a samu adalci da daidaito. Ko da yake kundin tsarin mulkin Najeriya bai tilasta tsarin karɓa-karɓa ba, manyan jam’iyyun siyasa suna bin tsarin sauya mulki tsakanin Arewa da Kudu. An tsare mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote A wata hira da ta yi da gidan talabijin na Channels a ranar Juma’a, Hannatu Musawa ta ce tun da an samu Shugaba daga Arewa (Muhammadu Buhari) na tsawon shekaru takwas, to ya dace yanzu kuma a bar ’yan Kudu...
Wata Kotu a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, ta tura mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Jihar Filato zuwa gidan yari. Ana zarginsu da kashe wasu ’yan ɗaurin aure a ƙauyen Mangun da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a jihar. Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki Mutanen da aka kashe suna cikin wata motar haya da ta taso daga Basawa a Karamar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna. Baƙin suna kan hanyarsu ta zuwa ƙauyen Kwa a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure. Wasu ɓata-gari ne suka...
Amurka ta bayyana dalilin sabunta manufofin, tare da lura da cewa “an tsara sharuddan bizar Amurka da ka’idoji domin kare tsarin shige da fice na Amurka.” Ofishin jakadancin ya kara da cewa “wadannan ka’idoji sun dogara ne kan ma’aunin fasaha da tsaro na duniya.” A cewar ofishin jakadancin Amurka yana aiki tare da hukumomin Nijeriya domin cimma wadannan matakan. Sanarwar ta ce “Tawagar Amurka tana aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin tabbatar da cewa Nijeriya za ta iya cika sharuddan.” Misalin wannan sabon tsari ya hada da “Takardun tafiye-tafiye masu aminci: tabbatar da cewa kasashe suna ba da amintattun takaddun balaguro tare da ingantattun bayanan matafiyi, Kada aikin gudanar da Bisa ya wuce lokacin da aka dauka:.” Duk da sabbin...
Kididdigar ta nuna cewa maimakon amfani da wannan kudaden shigar don rage basussuka, wasu jihohi suna kara amso bashin. Jihar Ribas ta zama ta farko a jerin jihohin da adadin bashin cikin gida na naira biliyan 364.39 a wata uku na farkon 2025, mafi girma tsakanin jihohi 10. Basukan Jihar Inugu sun tashi daga naira biliyan 82.48 a farkon wata uku na 2024 zuwa naira biliyan 188.42 a farkon wata uku na 2025, wanda ke nuna karuwa na naira biliyan 105.95 ko kashi 128.4 cikin dari. Jihar Neja ta biyo baya da karuwar naira biliyan 57.68 a kowanne shekara, daga naira biliyan 86.07 zuwa naira biliyan 143.75, wanda shi ne karuwa na kashi 67 cikin 100. Jihar Taraba ta nunka...
Wata Kotu a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, ta tura mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Jihar Filato zuwa gidan yari. Ana zarginsu da kashe wasu ’yan ɗaurin aure a ƙauyen Mangun da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a jihar. Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki Mutanen da aka kashe suna cikin wata motar haya da ta taso daga Basawa a Karamar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna. Baƙin suna kan hanyarsu ta zuwa ƙauyen Kwa a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure. Wasu ɓata-gari ne suka...
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ce yana da shakku a kan ko matatun mai mallakin gwamnatin Najeriya za su ƙara aiki a nan gaba. Najeriya dai na da matatun mai guda hudu mallakinta a biranen Fatakwal da Warri da Kaduna. Amma attajirin ya ce matatun man waɗanda ke ƙarƙashin kulawar Kamfanin Mai na Najeriya (NNPCL), sun laƙume sama da Dalar Amurka biliyan 18 wajen gyaransu, amma har yanzu sun ƙi aiki. Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC Ɗangote ya bayyana hakan ne ranar Alhamis lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin shugabannin kamfanoni wadanda ke Karatu a Lagos...
“A wajen jahilai, tsagaggen lebe lahani ne a kan makogwaro da lebe, amma idan akwai shinge tsakanin hanci da baki, ana kiran sa da suna handa. Wani abu ne da ba a san abin da yake kawo shi ba, amma kuma ana danganta shi da abubuwa da dama kamar karancin rashin sinadarin bitamin B.” “Don haka, muna shawartar mata masu juna biyu da su mayar da hankali wajen yawan zuwa awon ciki, sannan kuma su rika shan magungunan da ake ba su na yau da kullum, ta yadda za a rage haihuwar masu dauke da wannan cuta. “Hakika wannan babban abin takaici ne a cikin al’umma, shi yasa kwararrun likitoci, ma’aikatan jinya, jami’an jin dadin al’umma da likitocin makogwaro, hanci...
“An tsara kungiyar ne domin hada kan Arewa da magance matsalar rashin aikin yi Wanda hakan ya sanya aka tattaro manyan hafsoshin soja da suka yi ritaya, da tsaffin gwamnoni, da masu rike da sarautun gargajiya, da masu fafutukar kare hakkin jama’a, da kungiyoyin matasa, da kwararrun a fannin ci gaban kasa wadanda da yawa daga cikinsu sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake gudanar da mulki da kuma mayar da muradun Arewa saniyar ware a ‘yan shekarun nan” “Yankin arewa na iya shawo kan kalubalen da suke fuskanta ta hanyar hadin kai da kuma sabunta kudurin samar da ci gaba,” Bafarawa ya kuma tabbatar da cewa ba an kafa kungiyar bace a matsayin dandalin siyasa ba, kuma...

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Jagora Da Kansa Ya Shiga Dakin Ba Da Umarnin Sojin Lokacin Yaki
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya bayyana cewa: Jagoran juyin juya halin Musulunci ya ba da umarninsa ga sabbin kwamandojin da kansu a lokacin yakin baya-bayan nan Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf, yayin da yake ishara da umarnin da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayar a yakin kwanaki 12 da aka kakabawa Iran, ya ce Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya kasance a dakin kwamandoji sau biyu a lokacin yakin tare da bayar da umarninsa ga sabbin kwamandojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran. A wata hira da aka yi da shi ta gidan telebijin, Qalibaf ya kara da cewa kwamandojin da aka nada sa’o’i bayan fara kai hare-hare kan kasar Iran,...

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran yayi tsokaci kan takunkumin Amurka ta kakaba kan jami’ar Majalisar Dinkin Duniya da cewa: Ba za a iya murkushe gaskiya ba Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya yi tsokaci kan takunkumin da Amurka ta kakaba wa wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil’adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, Francesca Albanese. A cikin wani rubutu a dandalin “X” a ranar Juma’a, Baqa’i ya bayyana cewa: “Ba za a iya murkushe gaskiya ba.” Wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan halin da ake ciki na kare hakkin bil’adama a yankin Falasdinu, Francesca Albanese, ta fuskanci takunkumi da girman kai saboda fallasa gaskiya da kuma tsayin...
Mataimakin shugaban kasar na farko ya jaddada cewa: Kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Iran Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: kalmar mika wuya ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron kasar. Arif ya ce: Kamar yadda kuke gani kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa, su mutane ne masu wayewa, tare da ingantaccen tarihin al’adu wanda ya wuce dubban shekaru. Ba su neman yaki, kuma ba su fara shi ba. Sun yi imani da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma a shirye suke don tattaunawa, amma ba za su mika wuya a...
A daya bangaren kuma Fita zuwa wani yanki daban da ba naka a halin yanzu, yana da nasa fa’idar. Domin kuwa, na ziyarci wasu jihohi uku kwanan nan; wadanda labarai a kansu babu dadin ji. Jihohin su ne, Delta, Inugu da kuma Zamfara, wadanda galibi labaransu marasa dadi ne ta fuskar siyasa, ta’addanci da sauran munanan laifuka. Daga labarun da ake samu yau da kullum, za ka yi tsammanin cewa; wadannan jihohi tuni sun tashi daga aiki, amma daga ziyarar da na kai musu; na ga abubuwan ban mamaki, tsoratarwa da kuma hadari duk da ke dauke cikin wannan labari. Duk da cewa, kowace jiha akwai abubuwan da ta fi bai wa muhimmanci, su ma kamar sauran jihohin; suna...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Matasan Najeriya da dama suna son yin arziki amma ba tare da sun sha wahala ba. Sau da yawa matasa sun fi neman hanya mafi sauki da za ta basu arziki ba tare da sun sha wahala ba. NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu matasa bin yanke don tara abin duniya. Domin sauke shirin, latsa nan
shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibof ya bayyana cewa asarorin da HKI ta yi a yakin kwanaki 12 da JMI suna da yawa. Kuma babu shakka ya fi abinda ta bayyana. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a lokacinda yake hira da wata tashar talabijin a nan Tehran . Ya kuma kara da cewa. Maganar cewa uahudawa 3500 kawai suka ji rauni a yakim gaba daya karya ce. Qalibof ya ce yana da tabbacin cewa yahudawa akalla 500 suna halaka sanadiyyar hare-haren da sojojin Iran suka kai a kan HKI a yankin kwamaki 12. . Ya ce sojojin yahudawan sun saba boye yawan mutanen...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa kofar tattaunawa da Amurka kan shirinta na makamashin Nukliya a bude take, amma kafin haka sai gwamnatin kasar Amurka ta biya diyyar kura kuran da ta yi a bayan. A wata hirar da yayi da Jaridar Le Monde na kasar Faransa Aragchi ya kara da cewa da farko Amurka yakamata ta canza halayenta, na rashin kaiwa kasar Iran hare-hare a lokacin tattaunawa. Ya ce diblomasiyya hanyace mai tituna biyu na zuwa da komawa, amma Trump ya zo ya rufe dayar. Kuma tattaunawar diblomasiyya a wajen Iran a ko yauce a bude yake, Hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Iran a cikin yakin kwanaki 12 keta hurumin diblomasiyya...
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya fadawa shugaban majalisar tarayyar Turai Antonio Costa, kan cewa huldar kasar Iran da hukumar makamashin Nukliya ta duniya IAEA zai kasance tare da sharudda. Saboda hukumar ta yi watsi da ayyukanta na asali ta koma siyasa. Ta fita daga bangaren kwararru ta zama tana bin bukatun wasu. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dangantakar Iran da hukumar ta IAEA a da can ta zuciya guda ce, bata boyewa hukumar wani abu a cikin ayyukanta na makamashin Nukliya. Amma a halin yanzu mun gano cewa hukumar ce take bawa HKI bayanai dangane da ayyukammu na Nikliya ta kuma bada sunaye dadireshin masana fasahar Nukliya na kasar HKI ta zo ta kashesu...
Rahotanni na cewa ’yan fashin daji masu yawan gaske ne aka tabbatar da kashewa a wani kwanton ɓauna da sojoji suka yi musu a ranar Laraba a jihohin Zamfara da Kebbi. Sojojin ƙasa da na sama sun yi amfanin da bayanan sirri wajen buɗe wuta kan ayarin ’yan fashin da ke kan ɗaruruwan babura suna zirga-zirga a yankin Yarbuga da ke Karamar Hukumar Maru a Jihar Zamfara. Kakakin Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya, Ehimen Ejodame, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da maraicen Alhamis, inda ya ce wasu daga cikin ’yan ta’addan sun rika kokarin guduwa a kafa da kuma kan baburan, amma sojojin suka ci gaba da yi musu ruwan wuta ta ko ina. Muna so a...
Ƙwallon da Chinwendu Ihezuo ta zura a minti na 89 ya isa ya kai babbar tawagar mata ta Nijeriya da akeyiwa lakabi da Super Falcons zuwa matakin Kwata Fainal na gasar cin kofin Afrika ta mata da hukumar CAF ke shiryawa ta shekarar 2025, Super Falcons ta doke kasar Botswana da ci 1-0 a wasan da suka buga yau Alhamis da karfe 8 na dare agogon Nijeriya a Casablanca. A fafatawar da aka yi a filin wasa na Stade Larbi Zaouli, Ihezuo ce gwarzuwar wasan, sakamakon kwallo daya tilo da ta jefa a ragar kasar Botswana dake Kudancin Afirika, Nijeriya ta lallasa Tunisia da ci 3-0 a wasan farko da suka buga, duk da cewa an tafi hutun rabin lokaci...
Mataimakin babban magatakardan MDD, kana sakataren zartarwa na kwamitin tattalin arzikin Afirka Claver Gatete, ya bayyana cewa, kasar Sin aminiya ce da kasashen Afirka za su iya dogaro da ita. Gatete ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin da ya karbi takardar wakilcin kasa daga sabon wakilin kasar Sin a kwamitin tattalin arzikin Afirka na MDD, kana shugaban tawagar jakadun kasar Sin dake kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU Jiang Feng a birnin Addis Ababan kasar Habasha, mazaunin kwamitin na tattalin arzikin Afirka na MDD. A yayin ganawarsu, Claver Gatete ya taya Jiang Feng murnar gudanar da sabbin ayyuka, ya kuma yi fatan karfafa hadin gwiwa da kasar Sin, domin ba da taimako ga bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasashen...
Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati a Nijeriya ta buƙaci Majalisar Tarayyar da ta amince da ƙudirin dokar da zai ba ta damar bincikar ɗaiɗaikun ’yan Najeriya game da yadda suka tara dukiyarsu. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito Shugaban EFCC, Ola Olukayode yana cewa ƙudirin mai suna “Unexplained Wealth Bill” ya je gaban ’yan majalisar tun a majalisa ta tara, wanda suka yi watsi da shi. Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba “Akwai alaƙa mai ƙarfi tsakanin ɓarnar da ake yi arzikin ƙasarmu da kuma matsalar tsaro,” a cewarsa yayin wani taro da kwamatocin majalisar...
Dakarun rundunar Operation Haɗin Kai sun yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram da ISWAP 24 a wasu sabbin hare-hare da suka ƙaddamar a maɓoyar ’yan ta’addan a yankunan daban-daban a Arewa maso Gabashin Nijeriya. Kwamandan haɗakar rundunar Operation Haɗin Kai a Arewa Maso Gabas, Janar Abdulsalam Abubakar ya ce an kai samamen ne bayan tattara bayanan sirri. A cewarsa, an kuma kashe mutum biyar da suke samar wa ’yan ta’addan kayayyakin amfani, a wani kwanton ɓauna da aka yi musu da daddare. An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu An gudanar da waɗannan ayyuka ne a tsakanin ranakun 4 zuwa 9 ga watan Yuli a...
An tabbatar da mutuwar mutum ɗaya, tare da ƙona gidaje sama da 100, wanda ake zargin wasu makiyaya ne a unguwannin manoma da ke Ƙaramar hukumar Karim Lamido a Jihar Taraba suka yi. An kai wa mazauna unguwar Bandawa Gwenzu, waɗanda suka haɗa da: Gwenzu da Langwanshin da Danzhan hari a daren Laraba. Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno Da yake magana da tashar Talabijin na Channels TV ta wayar tarho a ranar Alhamis, shugaban matasan Uunguwar yankin, Ishaya Peter ne ya bayyana harin a matsayin rashin gaskiya da abu mai muni kuma ya yi Allah-wadai da harin. A cewarsa, mazauna garin na zaune suna...
Shugaban yahudawan Iran Rabbi Younes Hamami Lalezar ya ce, Isra’ila tana amfani da addini yahudanci domin cimma manufofinta, tana kuma bayyana Iran a matsayin wacce take fada da addinin yahudanci,alhali a cikin iran da akwai zaman lafiya tsakanin Mabiya dukkanin addinai. Haka nan kuma ya ce, kiyayyar da Isra’ila take da shi akan Iran ne, yake sa take jinginawa Iran din kin jinin yahduawa,wanda aikin ‘yan sahayoniya ne su samar da rabuwar kawuna a tsakanin al’ummar Iran bisa addini da kuma kabila. Isra’ila tana bayyana kanta a matsayin mai bai wa yahudawa kariya, sai dai da dama daga cikin Mabiya addinin yahudanci, wadanda ba ‘yan sahayoniya ba, suna zarginta da amfani da addini saboda manufofi na siyasa. Fiye da shekaru ...
Kungiyar al-shabab mai alaka da alka’ida ta kai harin kunar bakin wake a wani barikin soja da yake birnin Magadishu a jiya Laraba da marece. Shaidun ganin ido sun ce, harin ya yi kara mai tsanani wacce ta girgiza babban birnin kasar Magadishu, sannan kuma harbe-harbe su ka biyo baya. Kungiyar al-shabab mai alaka da alka’ida ce ta dauki alhakin kai harin. Sai dai kuma babu wani cikakken bayani akan ko harin ya yi sanadin jikkata ko rasa rayuka. Ita dai kungiyar al-shabab ta dade tana kai hare-hare a cikin kasar Somalia da hakan ya sa gwamnatin kasar take daukar ta a matsayin kungiyar ta’addanci. A shekarar 2023 ma dai kungiyar ta al-shabab ta kai wani harin kunar bakin wake...

Bafarawa Ya Kaddamar Da Wata Kungiya Mai Suna “Arewa Cohesion Initiative” Don Maganin Kalubalen Da Yankin Arewa Ke Fuskanta
Ganin irin yawan kalubalen tattalin arziki da siyasa a Arewacin kasan nan ya sanya Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya kaddamar da wata sabuwar kungiya mai taken Arewa Cohesion for Peace, Unity and Development Initiative. An kaddamar da wannan kungiyoyi ce a wajen wani babban taro da aka gudanar a Arewa House, Kaduna, inda manyan baki da mahalarta daga sassa daban-daban na Arewa suka halarta. A yayin taron, Bafarawa wanda shi ne Shugaban Kwamitin Amintattu na tafiyar, ya bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanyar da za ta yi maganin baraka da inganta fahimtar juna da kuma karfafa ci gaban mai dorewa a yankin Arewa. Ya ce Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da...
Ban da haka, bayan da aka tsara “shirin shekaru 5”, yana da muhimmanci a aiwatar da shi. A kasar Sin, bayan da aka gabatar da wani “shiri na shekaru 5”, dole ne a aiwatar da shi yadda ake bukata. Kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da majalisar gudanarwar kasar za su tsara salon aiwatar da dukkan ayyuka, da raba su ga sassa da yankuna daban-daban, don a aiwatar da su a matakai daban daban. Bayan haka, hukumomi daban daban su kan gudanar da ayyukan sa ido a tsakiyar wa’adin shirin, kuma za a tantance ainihin sakamakon da aka samu bayan karewar shirin. Ta wadannan halayen musamman, za a iya ganin abubuwan da za su tabbatar da aiwatar da...
Dakarun sojojin Nijeriya na rundunar sojojin sama tare da haɗin gwiwar Operation Haɗin Kai sun kai farmaki kan wasu muhimman wuraren da ’yan ta’adda suka mamaye a tsaunin Mandara da ke Jihar Borno. An samu labarin cewa rundunar sojin sama ta gudanar da samamen ta ne a wani wuri da aka san shi da tudu mai tsauni, wanda ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru, bayan samun bayanan sirri. An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano Daily Trust ta ruwaito cewa, samamen share fagen ya zo ne ƙasa da sa’o’i 24 da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umurci sojoji da su kawar da...
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato a ranar Alhamis ta gurfanar da wasu mutane 22 da ake zargi da kashe matafiya bikin aure da a unguwar Mangun da ke Ƙaramar hukumar Mangu ta Jihar Filato. An kashe mutum 13 daga cikin matafiyan, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon harin da wasu da ake zargin ’yan daba ne suka kai lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa unguwar Qua da ke ƙaramar hukumar Qua’an Pan ta Jihar Filato. ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa Adadin waɗanda aka kashe mutum 32 da suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara suna cikin...
Wannan sabon birni na da ganuwa mai tsawon kilomita 8.5 da zai kare Legas daga ambaliyar ruwa, kuma yana da gidaje, ofisoshi da wuraren kasuwanci da na nishaɗi. Dangote ya ce wannan aiki yana daga cikin manyan abubuwan tarihin da Shugaba Tinubu zai bari. Hakazalika, ya nuna godiyarsa bisa fara aikin titin gaɓar teku daga Legas zuwa Kalaba da kuma aikin titin Sakkwato zuwa Badagry, waɗanda za su inganta sufuri da tattalin arziƙi a faɗin ƙasar. Ya kwatanta hangen nesan Tinubu da yadda ƙasar Netherlands ta kasance wajen samar da muhallai a cikin ruwa don raya birane. Dangote ya ƙara da cewa kamfaninsa na jin daɗin irin goyon bayan da gwamnati ke ba shi wajen sauƙaƙa kasuwanci da bunƙasa tattalin...
Gwamna Malam Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar kasuwanci mara shinge a Maigatari, wanda ya bayyana a matsayin muhimmin ginshikin bunkasar tattalin arziki, kasuwanci da masana’antu a jihar. Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Kwamandan Yankin K da Jigawa na Hukumar Kwastam ta Najeriya, Kwamanda Dalhat Abubakar, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a Fadar Gwamnati da ke Dutse. Gwamna Namadi ya taya Kwamanda Abubakar murnar nadin nasa, tare da yaba wa hukumar Kwastam bisa goyon bayan manufofin cigaban jihar Jigawa, musamman wajen farfado da aikin Maigatari da aka yi watsi da shi. Ya nuna godiya bisa goyon bayan Kwamandan ya bayar, tare da yabawa da rahotannin da ke...

Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
Ministan Tsaron Iran ya bayyana cewa: Hare-haren da Iran ta kai ne suka tilasta wa gwamnatin mamayar Isra’ila daukan matakin tsagaita bude wuta Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh ya bayyana cewa: Munanan hare-haren da sojojin kasar Iran suka kaddamar a matsayin mayar da martani ga yahudawan sahayoniyya ne suka kai ga neman tsagaita bude wuta. A wata tattaunawa ta wayar tarho guda biyu da ya yi da ministocin tsaron Venezuela da Armeniya, Birgediya Janar Nasirzadeh na rundunar sojin sama ya jaddada cewa: Hare-haren da sojojin Iran suka kaddamar kan yahudawan sahayoniyya ne suka kai ga neman tsagaita wuta. Ministan tsaron na Iran ya kara da cewa: Sojojin kasar Iran sun shirya tsaf domin mayar da martani ga...
Kwamandan sojojin kasa na sojojin Iran ya jaddada wajabcin Karin daukan matakan kare iyakokin Jamhuriyar Musulunci ta Iran Kwamandan sojojin kasa na kasar Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya jaddada wajibcin kare cikakken kan iyakokin kasar akida, al’adu, da yanki, yana mai cewa: Dole ne dukkanmu al\umma su zama masu kare wannan kasa da kuma samun kwarin gwiwa daga tafarkin shahidai. A yayin wata ganawa da iyalan shahidan kwanaki 12 da gwamnatin sahayoniyawa ta kakaba wa Iran a birnin Sarpol-e Zahab na lardin Kermanshah a ranar Larabar da ta gabata, Birgediya Janar Heidari ya bayyana cewa: Sojojin kasar suna kan gaba wajen kare ‘yancin kai da yankinsu na kasar, kuma a kodayaushe suna nuna godiya da irin hakurin da iyalan...

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Mayar da martanin Iran ga ‘yan sahayoniyya sun murkushe girman kan makiya Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya jaddada cewa: Martanin da Iran ta mayar wa yahudawan sahayoniyya a lokacin arangamar da suka yi a baya-bayan nan abin nuni ne, domin kuwa a duk tsawon tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta taba samun irin wannan martanin mai gauni ba. Ghalibaf, wanda ya karbi bakwancin jakadan Belarus a birnin Tehran, Dmitry Kaltsov, a jiya Laraba, ya yaba da matakin da gwamnatin Belarus ta dauka dangane da hare-haren da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauika na kai wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran hare-haren wuce gona da iri. Yana mai...
Manjo Janar Hatami: Nasarar da gwamnatin Musulunci ta samu kan makiya yahudawan sahayoniyya wata babbar nasara ce ga al’ummar Iran Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Dakarun tsaron sama na sojojin Iran sun cimma wani gagarumar nasara a yakin da suka yi da makiya yahudawan sahayoniyya. A wata ganawa da iyalan shahidi Kanar Bostan Afrouz, Manjo Janar Hatami ya kara da cewa: Makiya sun kasa cimma tsare-tsare da shirye-shiryensu da suka rigaya sukaaniyar cimmawa, kuma sun fuskanci mummunar martani da shan kashi. Ya ci gaba da cewa: Nasarar da gwamnatin Musulunci ta samu kan makiya yahudawan sahayoniyya duk da karfin soja da kudi da suke da su, baya ga bayanan sirri da suke tabbatar...
Ya ce: “Ba mu kai inda muke so ba a fannin tattalin arziki, amma muna iya gani cewa abubuwa suna tafiya a hankali. Shugaban Ƙasa ya faɗa sau da dama cewa mun fara fitowa daga ƙunci. “Na san mutane da yawa za su ce ba mu kai ga cikakken cigaba da jin daɗin tattalin arziki ba tukuna. Gaskiya ne! Ni ma na yarda. Amma ba za mu ce babu cigaba ko kaɗan ba.” Ya ƙara da cewa: “Ko hukumomin ƙididdiga na duniya suna fara ba Nijeriya kyakykyawan matsayi. Muna ganin alamu na ɗagawa a hanyar da ake tafiyar da tattalin arzikin mu.” Idris ya ce manyan matakan sauyi kamar cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar...
Hadimin Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, kan Harkokin Yaɗa Labarai, Temitope Ajayi, ya mayar wa tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha martani, kan cewa Tinubu bai taimaka wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ba wajen zama shugaban ƙasa a 2015. Ajayi, ya ce Buhari yana da ƙarfi sosai a Arewa amma hakan bai hana shi faɗuwa zaɓukan 2003, 2007 da 2011 ba. Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata Ya bayyana cewa a zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC da aka yi a 2014, Tinubu ne, ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin Buhari ya lashe. Ya ce Tinubu ne ya shawo kan gwamnonin APC da...
Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, ciki har da ɗan sanda da ’yan sa-kai guda uku, a wani hari da ’yan bindiga suka kai garin Mongoro da ke Ƙaramar Hukumar Mariga, a Jihar Neja. Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Laraba. Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo Mazauna garin Wamba, sun ce har yanzu suna cikin fargaba saboda ‘yan bindigar ba su bar yankin ba. A ranar 24 ga watan Yuni, maharan sun kai hari wani sansanin sojoji da ke Kwanan-Dutse, inda suka kashe sojoji 17, tare da jikkata wasu 10. A cewar...
Gwamana Charles Soludo na Jihar Anambra ya ce mafi rinjayen kaso na waɗanda jami’an tsaro ke kamawa da aikata laifuka tsawon shekara uku da suka gabata ’yan kabilar Ibo ne. BBC ya ruwaito Soludo yana bayyana hakan a yayin wani taro da ’yan asalin jihar mazauna ƙetare suka gudanar a Amurka. Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya Soludo wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya yi watsi da zargin da ake yi wa Fulani makiyaya na aikata satar mutane a jihar. “Yanzu shekara uku da wata uku ke nan ina kan mulki. Idan muka kama masu laifi 100 to kashi 99 cikin 100 matasan ƙabilar...

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Game da koma bayan tattalin arziki da duniya ke fuskanta, ana matukar bukatar bullo da sabbin hanyoyin samun bunkasa. Shi ya sa, yin kirkire-kirkire da habaka hanyoyin samun bunkasa, ya zama mataki mafi jawo hankula daga cikin tsarin hadin gwiwar mambobin BRICS. Sin ta sanar a wannan taro cewa, za ta kafa cibiyar nazarin sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko ta Sin da kasashen mambobin BRICS. Kazalika, game da babakeren da Amurka ke nunawa, mambobin BRICS sun yi kira da a kiyaye ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori a duniya da gaggauta kafa kyakkyawan tsari da dokar tattalin arziki da cinikin duniya mai adalci da bude kofa. Albarkacin cika shekaru 10 da kafuwar bankin NDB na BRICS, Sin...
Tsohon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgediya Muhsin Rizai, ya sanar da cewa; Dakarun IRGC sun yi nasarar harbo jirage manya da marasa matuki na HKI har guda 80, kuma da akwai baraguzai 32 daga cikinsu da ake rike da su. Birgediya Rizai ya kuma kara da cewa; Daga cikin wadanda aka harbo din da akwai samfurin “Hermes” da “Hermon” da sune kira ta karshe da ‘yan sahayoniya suke takama da su. Birgediya Muhsin Rizai wanda memba ne a majalisar fayyace maslahar tsarin musulinci ta Iran, wanda tashar talbijin ta yi hira da shi da marecen jiya Talata, ya yi Magana akan bangarori da dama na kallafaffen yakin kwanaki 12 inda ya ce:” Gabanin mu yi...
Shugaban kungiyar Kurdawa ta kasar Turkiya ( PKK) Abdullah Ojlan ya sanar da kawo karshen amfani da makamai a fafutukar da kungiyarsu take yi na kare hakkokinsu a kasar Turkiya. Shugaban kungiyar Kurdawan na Turkiya wanda yake tsare a kurkuku na shekaru masu tsawo, ya aiko da sako na bidiyo da a cikin ya ce; Har yanzu ina kan kiran da na yi a ranar 27 ga watan Febrairu na ajiye makamai”. Ojlan ya kara da cewa; Muna sanar da kawo karshen amfani da makamai ne bisa radin kanmu, haka na kuma ya ce; Mun shiga Zangon aiki da doka da kuma siyasa da tsarin demokradiyya, wanda shi kanshi nasara ce mai dimbin tarihi ba asara ba.” Kuniyar PKK ta...
Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ziyarci iyalin marigayi, Alhaji Aminu Dantata a Jihar Kano, don yi musu ta’aziyya. Obi, ya bayyana cewa ya yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar Alhaji Ɗantata, inda ya bayyana shi a matsayin “uba ga kowa.” An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo Ya yaba yadda Ɗantata ya zama babban attajiri kuma ya taimaka wa mutane da dama suka samu nasara a rayuwarsu. Ya ce Ɗantata ya taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Najeriya. “Mun zo nan yau don jimami tare da iyalinsa da kuma ɗaukacin ‘yan Najeriya, saboda...
Sanarwar ta ƙara da cewa mutane 3,824 da suka yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin jiha sun samu N7,960,162,598.64, yayin da 4,833 daga ƙarananan hukumomi aka tantance kuma an biya su N5,983,876,606 a matsayin garatuti. A jimlace, an biya N13,944,039,204.64 a matsayin kuɗaɗen garatuti. Gwamna Lawal bayan ya karbi rahoton ya ce gwamnatinsa ta ba da fifiko wajen daidaita biyan haƙƙoƙin ma’aikatan gwamnati, musamman waɗanda suka yi ritaya bayan shekaru 35 suna aiki kuma suka kai shekaru 60. “Gwamnatinmu ta gaji sama da Naira Biliyan 13 a matsayin bashin kuɗaɗen garatuti na waɗanda suka yi ritaya daga Jiha da Ƙananan Hukumomin daga 2011 zuwa 2023, jinkirin ya jawo wahalhalu, kuma wasu da suka yi ritaya sun mutu su na...
Karuwar tasirin da kasar Sin ke yi a fagen ci gaban kimiyya da fasaha a duniya ba barazana ba ce, sai dai wata dama ce ta kawo ci gaba mai gamewa. Diamond ya kara da cewa, “Kasancewar na yi aiki kafada da kafada da wasu jami’o’i da cibiyoyin kasar Sin na tsawon shekaru masu yawa, na yi amanna da yadda kasar Sin ta dukufa ga samar da kimiyya da fasaha mai bude kofa ga duk duniya bisa adalci.” Kazalika, masanin kimiyya, mamba a makarantar nazarin kimiyya da fasaha ta Afirka, Farfesa Felix Dapare Dakora, ya nuna yadda kasar Sin ke karfafa shigar kasashe masu tasowa cikin harkokin kimiyya a duniya. Yana mai cewa, “A halin yanzu, an gode da samuwar...
Firaministan Sin Li Qiang ya bayyana a yau Laraba cewa, a matsayinsu na muhimman membobin kasashe masu tasowa, ya kamata Sin da Masar su karfafa hadin gwiwarsu bisa manyan tsare-tsare, domin kare muradunsu na bai daya. Li Qiang ya bayyana haka ne bayan isarsa birnin Alkahira, a ziyarar aiki da yake yi a kasar bisa gayyatar takwaransa na Masar din, Mostafa Kamal Madbouly. Firaministan Masar da sauran manyan jami’an gwamnatin kasar ne suka tarbi Li Qiang tare da shirya biki domin yi masa maraba. Kafin isarsa, Li Qiang ya halarci taron kungiyar BRICS karo na 17 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu...
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), ta ƙara sanya wa ’yan Najeriya da ke son ziyartar Dubai sabbin sharuɗa. Haka kuma, ta dakatar da bayar da bizar wucin gadi ga ’yan Najeriya. Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista Aminiya ta samu labarin cewa hukumomin shige da fice na Dubai ne suka bayar da umarnin sabbin matakan ga ofishin jakadancin ƙasar da ke Najeriya. Daga cikin sabbin dokokin, duk ɗan Najeriyar da ke tsakanin shekaru 18 zuwa 45 ba zai samu bizar yawon buɗe ido ba sai idan zai yi tafiya tare da wani. Wannan na nufin cewa yawan ’yan Najeriya...
Kungiyar bayar da agaji ta kasa da kasa ta Red Cross ta ce akwai yara akalla miliyan biyar da dubu 400 da ke fama da matsalar karancin abinci a jihohi tara na arewacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro. A cewar kungiyar, jihohin su ne Borno, Adamawa, Yobe, Sokoto, Katsina, Zamfara, Neja, Binuwai da kuma Kano. Mai rikon mukamin Darktan Lafiya da Kula na kungiyar Dr Aminu Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a yayin taron gangamin neman tallafi kan karancin abinci na kungiyar na shiyyar Arewa maso Yamma da ya gudanar a Kano ranar Talata. Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja...

Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta sanar da cewa: Iran ba ta gabatar da wata bukatu na ganawa ga bangaren Amurka ba Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya musanta kalaman shugaban Amurka dangane da muradin Iran na gudanar da tattaunawa, yana mai jaddada cewa: A bangaren Iran ba a gabatar da wata bukata ta yin wata ganawa da bangaren Amurka ba. Da yake mayar da martani ga kalaman Donald Trump, Ismail Baqa’i ya ce: Iran tana musanta abin da Trump ya fada game da bukatar Iran na gudanar da tattaunawa, kuma ba ta gabatar da wata bukata ta ganawa da Amurkawa ba. Yayin ganawarsa da Fira ministan gwamnatin Isra’ila Benjamin Netanyahu da yammacin ranar Litinin, Trump ya yi ikirarin cewa an...

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Shi ma Uban taro mai masaukin baki, shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya bayyana a jawabinsa na taron kolin cewa, “Idan har ba a samu sauyi a tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa a wannan karni na 21 ba, to ya zama wajibi kasashen BRICS su taimaka wajen ganin an sabunta shi.” BRICS taska ce ta hadin kai, daidaito da kuma kokarin tafiya tare don samun ci gaba da tsira tare, da kuma karfafawa kasashe masu neman ‘yancin fadin albarkacin bakinsu a harkokin tsare-tsare na hadin kan kasashen duniya. Taron kolin kungiyar na bana, na zuwa ne a daidai lokacin da kasuwannin duniya ke cike da firgici biyo bayan yakin cinikayya da kasar Amurka ta kaddamar,...
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Gaza ba za ta mika wuya ba don haka ‘yan gwagwarmaya ne zasu gindaya sharudda Izzat al-Rishq mamba a ofishin yada labarai na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya bayyana cewa: Kalaman fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu na sakin dukkan fursunonin da suke hannun ‘yan gwagwarmaya da kuma mika wuyar Hamas sun sabawa matakin hankali da hakikanin abin da ke gudana a fagen yaki. Al-Rashq ya tabbatar a cikin wani takaitaccen bayani a shafinsa na Telegram da sanyin safiyar Larabar nan cewa: Bayan da shugabannin ‘yan mamaya makiya suka amince da gazawar da suka yi wajen kwato fursunoninsu ta hanyar karfin soja; Ya bayyana cewa babu yadda za a...