Leadership News Hausa:
2025-11-02@12:28:51 GMT

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Published: 2nd, November 2025 GMT

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.

 

Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.

 

Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.

 

Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.

 

“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.

 

“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.

 

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.

 

“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.

 

Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.

 

“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.

 

“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.

 

Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.

 

Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.

 

“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.

 

Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.

 

“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.

 

Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.

 

Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya October 18, 2025 Noma Da Kiwo Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul October 18, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da taraktocin noma noma na jihar gwamna Bassey noman jihar

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Oguntala ta bayyana cewa, ana sa ran babban ministan ma’aiktar bunkasa tattalin arziki na teku Mista Adegboyega Oyetola, zai halarci taron, wanda aka tsara za a gudanar a watan Disambar wannan shekarar a garin Ibadan.

Ta bukaci hukumar ta Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, da ta yi hadaka da kungiyar domin gudanar da taron wanda ta sanar da cewa, Shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ne, zai kasance babban mai gabatar da jawabi, a wajen taron kungiyar.

Kazalika, ta yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta dauki nauyin manyan kasidun da za a gabatar da wajen taron tare da samar da ilimi kan batun da ya shafi fannin na bunkasa tattalin arziki na teku.

Shugabar ta kuma bai wa hukumar ta NPA damar da ta yi bajin koli a yayin gudnar da taron, inda kuma ta sanar wa da hukumar ta NPA cewa, ta zabo wasu daga cikin injiniyoyin NPA da ta sanya a cikin kwamtin shiye-shiyen gudanar da taron.

Ta kuma shedawa Dantsoho cewa, wasu masu masana’antu da wasu daga bangaren gwamnati da kuma wasu daga bangaren manyan makarantun kasar nan, na da burin yin hadaka da hukumar ta NPA.

“Mun sa irin kokarin da shugaban hukumar ta NPA key i, musaman wajen kara bunkasa tattalin azrikin da ke a fannin ayyukan Tashoshin Jitagen Ruwan kasar” .

“Muna sane da cewa, ba za mu iya gudanar da gagarumin atron namu, matukar ba mu samu guduanmwar da za ku iya bamu ba, domin shirya taron a acikin nasara, musamman duba da irin gudunmawar da za ku iya bayarwa,” Inji ta.

“Ba wai muna neman hukumar ta dauki nauyin mu bane, muna kawai bukatar yin hadaka da hukumar ta NPA ne , musamman duba da irin gawaurtaccen taron da muke yin yi,” A cewar shugabar.

“Fannin na bunkasa tattalin arzikin teku, abu ne da yake ci gaba da kara tumbatsa kuma abu ne, da ke da makoma mai kyau, haka fannin ne, da har yanzu, mutane ba su gama fahimtarsa ba,” Inji ta.

Ta kara da cewa, idan aka ba za daukacin bangarorin injiniyoyin zuwa rassa guda 93 da ake da su a kasar nan da kuma sauran wadanda suke a kasar waje, hakan zai kara taimaka wa, wajen kara bunkasa kasar nan.

Shugabar ta kuma bijro da batun shigar wadanda suka samu shedar kammala karatun injiniya wadanda suka samu horo daga gun kwararrun injiniyoyi suke kuma yin aiki a hukumar ta NPA.

Ta kara da cewa, bisa matakan bin ka’ida da bangaren gudanar da mulki da kungiyar ta dauka su ne, na tabbatar da duk wanda ya karaci ilimin injiniya dole ne ya kasance ya kai mataki na goma

A na sa jawabin shugaban hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da cewa, kashi 70 zuwa 80 na ma’ikatan da ke aiki a hukumar ta NPA injiniyoyi ne.

Dantsoho ya kuma bai wa shugabar kungiyar tabbacin cewa, za ta yi hadaka da kungiyar ta NSE, musamman domin a kara ciyar da kasar nan gaba, inda ya buga misali da sauran kasashen duniya da suka yi hadaka da kungiyoyin injiniyoyi wanda hakan ya ba su damar samun nasara, musamam ta hanyar yin hadaka.

Shugaban ya sanar da cewa, idan aka yi hadakar da hukum

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025 Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON