Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024
Published: 8th, March 2025 GMT
Wasu kwararru a fannin na aikin noman, sun alakanta samun wannan karuwar, saboda dauki daban-daban da gwamnatin tarayya ta samar ga fannin, musamman wajen kokarinta na rage kalubalen rashin tsaro.
Daga cikin wannan daukin na gwamnati, sun hada da kirkiro da shirin jami’an tsaro na sintiri sama da 1,000 da aka tura zuwa kanannan hukumomi 19 a 2024, don bai wa manoma da amfanin noma da aka shuka kariya, inda shirin ya taimaka wajen kara bunkasa aikin noma.
A cewar Hukumar ta ‘NBS’, fannin aikin noma ya samar da kashi 25.59 wajen habaka fannin tattalin arzikin kasar, wato ma’ana, a zango na uku na 2023, gudunmawar da fannin ya samar ga tattalin arzikin kasar, ya tsaya ne a kashi 26.11, idan aka kwatanta da gudunmawar da fannin ya samar ga tattalin arzikin kasar a 2024, wacce ta kai kashi 26.11.
Fannin aikin noman kasar, ya ci gaba da kasancewa kan gaba, musamman a bangaren day a shafi tattalin arzikin Nijeriya, duba da yadda daukacin fannin ya samar karuwar da ta kai kashi 90.70 cikin 100.
Haka zalika, a 2023, an samu raguwa da kshi biyu tare kuma da samun wata raguwar da ta kai kashi 3.86 a zango na hudu na 2023.
Daga shekara zuwa shekara, tattalin arzikin Nijeriya ya karu da kashi 3.84, wato a zango na hudu na 2024, wanda ya dara da kasshi 3.46 da aka samu a 2023.
“Kokarin da aka samu a fannin habaka tattalin arzikin kasar a zango na hudu na 2024, ya samu ne saboda garanbawul da aka yi wa fannin, inda aka samu karuwar da ta kai kashi 5.37, wanda hakan ya kara tallafawa fannin bunkasa tattalin arzikin kasar”, in ji rahoton.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin kasar
এছাড়াও পড়ুন:
An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
An dawo da wutar lantarki a safiyar Talatar nan a Sifaniya da Portugal bayan katsewar da aka samu ta sa’o’i wadda ita ce mafi muni da aka gani a Turai.
A jiya Litinin ce dai miliyoyin mutane suka auka cikin duhu bayan ɗaukewar wutar lantarkin a ƙasashen biyu wadda ke ci gaba da ɗiga ayar tambaya kan abin da ya haifar da ita.
Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a ChibokKafofin watsa labarai sun ruwaito cewa ɗaukewar wutar lantarkin ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama da na ƙasa da katse hanyoyin sadarwa ta wayar hannu da kuma rufe na’urorin cire kuɗi na ATM a duk faɗin ƙasashen biyu.
Wata sanarwa da hukumar samar da wutar lantarki a Spain ta Red Electrica ta fitar, ta ce da misalin ƙarfe 7 na safiya agogon ƙasar, an samu nasarar dawo da sama da kashi 99 na wutar lantarki a ƙasar.
Haka nan ita ma takwararta ta Portugal ta ce tun cikin daren jiya Litinin, aka dawo da wutar lantarkin da dukkanin tashoshin wutar ƙasar guda 89.
Bayan ɗauke wutar da aka samu a Spain, jami’an ba da agajin gaggawa sun sanar da nasarar kuɓutar da mutane dubu 35 da suka maƙale a jiragen ƙasa na ƙarƙashin ƙasa.
Har yanzu dai hukumomi ba su bayyana dalilin da ya sa aka samu ɗaukewar wutar lantarkin ba, wanda shi ne karo na biyu da irin wannan mummunar katsewar wutar lantarki ta faru a Turai cikin watanni