Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
Published: 1st, August 2025 GMT
A daren Juma’a ne dab da wayewar gari wata motar tirela ɗauke da awaki da kaji wadda ta taso daga Gwauron Dutse a Jihar Kano ta yi haɗari.
Motar tirelar wadda take ɗauke da dakon awaki da kuma kwandunan kaji mai yawa a samanta baya ga mutane da ta ɗauko ta yi haɗarin a kusa da kasuwar Ɗan Magaji saman gadar da ke kan hanyar Zariya zuwa Kaduna.
Awaki kusan sama da 100 suka mutu da kuma kaji kusan ɗari 500 ne aka ƙeyasta sun mutu.
Sai dai ba a sami asarar rai ko ɗaya ba, sai dai akasarin mutanen da suke motar sun sami raunuka cikinsu har da direban motar, kuma an garzaya da su zuwa Asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika Zariya don samun kulawar likitoci.
Wasu daga cikin matasan da suka kai ɗauki wurin sun kwashe matattun awakin da kajin inda suka watsa cikin wani kududdufi da ake kiwon kifi a kusa da inda motar ta yi hatsarin dan gudun kada wasu bɓata gari su kwashe dan sayarwa al’umma da mushen matattaun dabbobin.
Wani ganau da ke zaune a wurin da hatsarin ya faru ya ce yana zaton kamar barci ne ya kama direban motar.
A cewar ganau ɗin an tafka asarar sosai na dukiya a hatsarin motar sai dai shugabannin mazauna wurin sun sa ido domin ganin cewa ba a kwashi matattaun dabbobin ayi wani wuri da su ba.
An yi ƙokarin tuntuɓar mai magana da yawu hukumar kula da haɗɗura ta ƙasa reshen Zariya tare da tura masa saƙon kar ta kwana domin jin dalilin faruwar lamarin, amma har zuwa lokacin haɗa rahoton bai ɗauki waya ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin tirela Zaria
এছাড়াও পড়ুন:
’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.
A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.
’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.
Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.
Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.
Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.
Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp