HausaTv:
2025-11-08@17:21:11 GMT

An Dakatar Da Ayyukan Jam’iyyun Siyasa A Kasar Mali

Published: 9th, May 2025 GMT

Majalisar koli ta sojojin kasar Mali ta sanar da dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa da duk wasu kungiyoyi masu alaka da su.

A ranar Larabar da ta gabata ne dai majalisar sojan kasar ta Mali ta fitar da dokar wacce shugabanta janar Assimi Goita ya rattaba wa hannu, wanda kuma aka sanar ta kafafen watsa labarun kasar.

Sanarwar ta ce, an dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar har illa masha Allahu.

Dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar bai shammaci ‘yan siyasar kasar ta Mali ba, bayan da a baya a taron kasa da aka yi, aka gabatarwa da gwamnatin sojan shawarar dakatar da jam’iyyun siyasar da kuma nada shugaban majalisar koli ta sojan kasar a matsayin shugaban rikon kwarya na tsawon shekaru biyu, da kuma za a iya sabuntawa.

A karon farko, daruruwan mutanen kasar sun fito wani gangami a makon da ya shude domin yin kiran a mayar da kasar kan turbar demokradiyya.

Wani daga cikin  wadanda su ka tsara gangamin Sheikh Umar Dombiya ya fada wa kamfanin dillancin labarun AP cewa; “Ban yi mamakin wannan matakin ba, na tsammaci farwuarsa, domin wannan shi ne tunaninsu,amma za mu ci gaba da aiki tukuru domin kare tsarinmu na demokradiyya a Mali.

Masu Zanga-zangar dai sun rika bayar da taken nuni kin jinin mulkin soja.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an November 6, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST November 6, 2025 Daga Birnin Sin Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
  • A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Shugaban Kasar Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi