HausaTv:
2025-05-09@12:58:49 GMT

An Dakatar Da Ayyukan Jam’iyyun Siyasa A Kasar Mali

Published: 9th, May 2025 GMT

Majalisar koli ta sojojin kasar Mali ta sanar da dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa da duk wasu kungiyoyi masu alaka da su.

A ranar Larabar da ta gabata ne dai majalisar sojan kasar ta Mali ta fitar da dokar wacce shugabanta janar Assimi Goita ya rattaba wa hannu, wanda kuma aka sanar ta kafafen watsa labarun kasar.

Sanarwar ta ce, an dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar har illa masha Allahu.

Dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar bai shammaci ‘yan siyasar kasar ta Mali ba, bayan da a baya a taron kasa da aka yi, aka gabatarwa da gwamnatin sojan shawarar dakatar da jam’iyyun siyasar da kuma nada shugaban majalisar koli ta sojan kasar a matsayin shugaban rikon kwarya na tsawon shekaru biyu, da kuma za a iya sabuntawa.

A karon farko, daruruwan mutanen kasar sun fito wani gangami a makon da ya shude domin yin kiran a mayar da kasar kan turbar demokradiyya.

Wani daga cikin  wadanda su ka tsara gangamin Sheikh Umar Dombiya ya fada wa kamfanin dillancin labarun AP cewa; “Ban yi mamakin wannan matakin ba, na tsammaci farwuarsa, domin wannan shi ne tunaninsu,amma za mu ci gaba da aiki tukuru domin kare tsarinmu na demokradiyya a Mali.

Masu Zanga-zangar dai sun rika bayar da taken nuni kin jinin mulkin soja.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci – Ganduje

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da shawarar yin amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan fashi a Nijeriya.

Shugaban ya bayar da shawarar ne a ranar Larabar da ta gabata a lokacin da ya jagoranci mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na ƙasa a ziyarar jaje ga gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a kan harin da aka kai wa rundunar sojijin barikin soja da ke Buni Gari.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’

Ganduje ya ce dole ne yaƙi da ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi da makami su tafi tare da haƙiƙanin lokaci domin samun nasara.

Ya bayyana cewa abin takaici ne irin yadda ’yan tada ƙayar baya da ’yan fashi suke aikata munanan ayyuka a faɗin ƙasar nan.

“A yanzu za a yi amfani da albarkatun da ake da su don maye gurbin irin kayan aikin da aka lalata.”

Da yake jawabi, gwamna Buni ya ce gwamnati a matakai daban-daban na duba yadda ake amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da ‘yan ta’adda.

“Mu, a matakin ƙasa da gwamnonin yankin Tafkin Chadi, muna yin nazari sosai kan yadda maƙiya ke amfani da jirage marasa matuƙa aikata ta’assar wadda dole mu haɗa kai da jami’an tsaro don duba matsalar,” in ji Buni.

Ya ba da tabbacin cewa za a tattauna hakan a mataki mafi girma musamman da shugaban ƙasa domin daƙile ayyukan tada ƙayar baya da ’yan bindiga.

“Wannan matsala ce ta ƙasa domin a lokacin da suka kai hari a sansanin soji da kuma ƙwace makamai, ba za a iya sanin inda za a yi amfani da su ba, don haka ya kamata a ɗauki waɗannan hare-hare a matsayin hare-hare ga al’ummar ƙasa baki ɗaya ba wai Jihar Yobe kaɗai ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka
  • Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
  • Almundahana: Jamiyar LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
  • A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci – Ganduje
  • Gwamnatin Siriya Tana Neman Tattaunawa Da Gwamnatin Mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Tattaunawar Cinikayya Da Za A Yi Tsakanin Babban Jami’inta Da Na Amurka
  • Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen Ta Sanar Da Cewa Ayyukan Yemen Na Tallafawa Gaza Ba Zai Tsayawa Ba
  • Kawancen Jam’iyyun Adawa A Kasar Ivory Coast Ya Bukaci Gyara Wa Tsarin Zabe Kasar