HausaTv:
2025-09-24@12:41:08 GMT

An Dakatar Da Ayyukan Jam’iyyun Siyasa A Kasar Mali

Published: 9th, May 2025 GMT

Majalisar koli ta sojojin kasar Mali ta sanar da dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa da duk wasu kungiyoyi masu alaka da su.

A ranar Larabar da ta gabata ne dai majalisar sojan kasar ta Mali ta fitar da dokar wacce shugabanta janar Assimi Goita ya rattaba wa hannu, wanda kuma aka sanar ta kafafen watsa labarun kasar.

Sanarwar ta ce, an dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar har illa masha Allahu.

Dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasar bai shammaci ‘yan siyasar kasar ta Mali ba, bayan da a baya a taron kasa da aka yi, aka gabatarwa da gwamnatin sojan shawarar dakatar da jam’iyyun siyasar da kuma nada shugaban majalisar koli ta sojan kasar a matsayin shugaban rikon kwarya na tsawon shekaru biyu, da kuma za a iya sabuntawa.

A karon farko, daruruwan mutanen kasar sun fito wani gangami a makon da ya shude domin yin kiran a mayar da kasar kan turbar demokradiyya.

Wani daga cikin  wadanda su ka tsara gangamin Sheikh Umar Dombiya ya fada wa kamfanin dillancin labarun AP cewa; “Ban yi mamakin wannan matakin ba, na tsammaci farwuarsa, domin wannan shi ne tunaninsu,amma za mu ci gaba da aiki tukuru domin kare tsarinmu na demokradiyya a Mali.

Masu Zanga-zangar dai sun rika bayar da taken nuni kin jinin mulkin soja.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC
  • Hindi: Amurka Da Kasashen Yamma Ba Sa Son A Dakatar Da Bude Wuta A Gaza.
  • Iran : Dakatar da kisan kiyashi a Gaza, ‘’zakaran gwajin dafi ‘’ne ga  MDD”
  • Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu
  • Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila