Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da hadin gwiwar gwamnatin jihar Jigawa, sun fara horas da mata 600 kan inganta muhalli ta hanyar bola jari.

Shugaban Hukumar Kare Muhalli ta Jihar Jigawa JISEPA, Alhaji Adamu Sabo ya bayyana haka a wajen taron tunawa da ranar mata ta duniya da kuma fara horaswar da aka gudanar a Dutse.

Alhaji Adamu Sabo ya ce, baya ga  jajircewa, da juriya, da nasarorin da mata suke da, bikin ya yi duba kan irin rawar da mata suke takawa wajen dorewar muhalli da bunkasar tattalin arziki.

Ya jaddada cewa ta hanyar shirin bola jari, watiWaste to Wealth Initiative, za su iya baiwa mata damar kare muhalli da kuma samar da kyakkyawan yanayi ga iyalansu.

Shugaban hukumar ya bayyana cewa, duk da kalubalen da ake fuskanta a duniya a fannin sarrafa shara, da kuma yadda ake zubar da shara ba bisa ka’ida ba,  da ke barazana ga muhalli, har yanzu akwai damar da za a iya maida sharar da aka tara a gida zuwa dukiya.

Ya ce horon zai koyar da mata yadda za su yi kasuwanci da sharar da suka tara a gida, tare da tabbatar da karfafa tattalin arziki da kuma inganta muhalli.

Ya kara da cewa, hakan zai baiwa mata matasa damar ba da gudumawa wajen samun kudaden shiga a gida da kuma ci gaban tattalin arzikin kasa.

Bugu da ƙari, shugaban na JISEPA  ya bayyana cewa horaswar za ta yi amfani da shirin da UNICEF ta fara na “Samun Damarar Kasuwanci ga Matasa” (YOMA), wani sabon tsarin na dandali ta yanar gizo, da ke haɗa matasa daga ko’ina a fadin duniya  don koyon kasuwanci,  da samun kuɗi, da tasirin zamantakewa.

Adamu Sabo ya yabawa masu ruwa da tsaki da suka goyi bayan wannan shiri da suka hada da kungiyar jari bola  ta Najeriya WAPAN, da gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi bisa goyon bayan da suka bayar.

A jawabinta lokacin da take bayyana bude horaswar, uwargidan gwamnan jihar Jigawa, Hajiya Amina Umar Namadi, ta yaba da kokarin hukumar da sauran masu ruwa da tsaki da suka taimata wajan samun nasarar horon.

Ta ce shigar da mata cikin shirin inganta  muhalli ba shakka zai samar da wani tasiri, ba a Jigawa kadai ba har ma a duniya baki daya.

Ta yi kira ga mahalarta taron da su yi amfani da damar da suka samu wajen inganta rayuwarsu, baya ga ba da gudummawa wajen tsaftace muhallinsu.

Taken ranar Mata ta Duniya ta 2025 shi ne, “Bayar Da Dama ga Mata da ‘Yan Mata: Hakkoki, Daidaito, da  Ƙarfafawa, “wanda ke kira ga bai wa mata hakkokinsu, da samar musu da damarmaki,  ba tare da an bar su a baya ba.”

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Ranar Mata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar

Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kulla haɗin gwiwa mai muhimmanci da Jami’ar Azman domin faɗaɗa damar ilimi da inganta ci gaban al’ummar jihar.

An bayyana hakan ne lokacin da shugabannin Jami’ar Azman, karkashin jagorancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Fatima Batul Mukhtar, suka kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Wannan haɗin gwiwa yana da nufin tallafawa sabbin hanyoyin koyarwa, da daukar nauyin dalibai a wasu shirye-shirye na musamman, da kuma inganta basirar matasa a muhimman fannoni kamar lissafi da kwamfuta, da kimiyyar bayanai, da sarrafa harkokin jiragen sama, da sauransu.

Yayin da take jawabi, Shugabar Jami’ar ta nuna godiya ga jajircewar gwamnatin jihar wajen bunkasa ilimi, tare da jaddada aniyar jami’ar wajen samar da inganci da kirkire-kirkire.

Ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta hada kai da jami’ar wajen shirye-shiryen horar da matasa da ba su takardun shaidar ƙwarewa, musamman a bangaren shirye-shiryen kwamfuta, tare da manyan kamfanoni irin su Cisco, Huawei, da Oracle Academy.

“Mai Girma Gwamna, Jami’ar Azman ta riga ta samu ci gaba a shirye-shiryen kwamfuta, domin mun yi rijista da Cisco, Huawei, da Oracle Academy, kuma muna da malamai da ke da takardar shaidar koyarwa daga Huawei. Saboda haka, muna rokon ku da ku duba yiwuwar yin haɗin gwiwa da mu a shirye-shiryen takardun shaidar ƙwarewa a bangaren shirye-shiryen kwamfuta.”

Shugabar Jami’ar ta kuma yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta a fannin ilimi, musamman ware kaso 32 bisa dari na kasafin kudin 2024 ga bangaren ilimi da kuma ƙarin naira biliyan uku da aka ƙara wa Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Jigawa.

A nasa martanin, Gwamna Namadi ya nuna matuƙar godiya ga ƙoƙarin Jami’ar Azman tare da yabawa shugabancin Farfesa Fatima Batul Mukhtar.

Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin shirye-shiryen musamman da jami’ar ke bayarwa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana da shirin daukar nauyin wasu dalibanta domin su yi karantu a bangarorin da babu a sauran makarantu a jihar.

“Sabbin kwasa-kwasan da kuka kirkiro suna da kyau, kuma hakan zai jawo hankalin dalibai da malamai zuwa jami’ar.

Wannan na daga cikin dalilan da suka sa na ga babbar dama a wannan jami’a. Kwasa-kwasan da kuka ambata suna da matukar muhimmanci, musamman a yankunan da basu dawannan taarin karatu.”

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Birnin Beijing Ya Shirya Yiwa ‘Yan Mata Rigakafin Cutar HPV Kyauta
  • Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas
  • Gwamnatin Jigawa Da Bankin Duniya Sun Dauki Nauyin Dalibai 500 A Fannin Fasahar Zamani
  • Sama da ‘Yan Mata 74,000 Suka Amfana Shirin AGILE Cash A Kano
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
  • Fiye Da Yara Mata 74,000 Sun Amfana Da Shirin Tallafin Kudi Na AGILE A Kano
  • Uwargidan Tinubu Ta Bai Wa Mata Manoma Tallafin Naira Miliyan 26 A Nasarawa
  • Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto