Mahukuntan kasar Sin sun gudanar da taron koli, na tattauna aikin raya tattalin arzikin kasar, don tsara abubuwan da za a aiwatar a shekarar 2026 dake tafe. An gudanar da taron ne a jiya Laraba da yau Alhamis, inda shugabannin kasar suka tantance abubuwa mafiya muhimmanci, wadanda za a aiwatar, dangane da raya tattalin arzikin kasar a shekara mai kamawa.

Cikin muhimmin jawabi da ya gabatar yayin taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya waiwayi aikin raya tattalin arziki da Sin ta aiwatar a shekarar nan ta 2025, tare da fayyace halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, da ma aikin da aka tsara gudanarwa a shekara mai zuwa.

Yayin taron, an yi amannar cewa shekarar 2025 ta fita daban, kuma za a kai ga cimma nasarar muradun raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar Sin na shekarar ta bana.

ADVERTISEMENT

Taron ya kuma tabbatar da cewa, aikin raya tattalin arzikin Sin na shekara mai zuwa, zai karkata ne ga ayyuka irinsu bunkasa sayayya a cikin gida, da ci gaba wanda kirkire-kirkire ke ingizawa, da kara bude kofar kasar Sin ga sassan waje, da cikakken salon sauyi zuwa ci gaba marar dumama yanayi, da kyautata rayuwar al’umma. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria December 11, 2025 Daga Birnin Sin Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa December 11, 2025 Daga Birnin Sin Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana December 11, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin kasar aikin raya tattalin

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Jigawa ta bayyana damuwa kan jinkirin shari’a wajen gurfanar da masu laifin rashawa, inda ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 479 da suka shafi cin hanci, amana da sauran laifuka makamanta a wannan shekarar ta 2025.

Shugaban Hukumar, Barista Salisu Abdul ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai kan nasarorin da hukumar ta samu da ƙalubalen da ta fuskanta a shekarar

Taron manema labaran wani ɓangare ne na shirye-shiryen hukumar na bikin Ranar Yaƙi da Cin Hanci ta Duniya.

Barista Salisu Abdul ya ƙara da cewa, cin hanci babban abin da ke janyo koma-baya ne ga Najeriya a fannoni daban-daban na rayuwar jama’a da tattalin arzikin ƙasa.

A cewarsa, babban burin hukumar wacce aka kafa a watan Fabrairun 2024 shi ne ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa a jihar, tare da inganta gaskiya, ɗabi’a, da amana a harkokin gwamnati da na kamfanoni masu zaman kansu, da al’amuran zamantakewa da tattalin arziki.

 

Shugaban ya ce, a wannan shekarar hukumar ta shirya horo ga manyan ma’aikatan gwamnati da jami’anta, tare da wayar da kan jama’a kan rawar da kowa ya kamata ya taka wajen yaƙi da cin hanci.

“Yayin da muke ci gaba da wayar da kai sosai, za mu ƙara haɗa kai da sauran hukumomin yaƙi da cin hanci, da hukumomin gwamnati da masu zaman kansu, da jama’a domin mu fi mai da hankali wajen dakile cin hanci fiye da magance shi bayan ya faru,” in ji shi.

Ya kuma ce, hukumar za ta rungumi fasahar zamani a ayyukanta don samun ingantaccen sakamako.

Barista Salisu Abdul ya bayyana cewa, daga cikin shari’o’in 479, guda 110 sun shafi cin hanci da damfarar kuɗi, yayin da 375 suka shafi rikicin kadarori, sabanin iyali, da ma’amalar kasuwanci da ta ci tura, inda aka warware shari’o’i 107 cikin sulhu.

Ya kara da cewa an dawo da fiye da Naira miliyan 385 da kadarorin da darajarsu ta kai daruruwan miliyoyi, aka kuma mika su ga masu su.

Sai dai ya nuna damuwa kan yadda alkalai ke tafiyar da shari’o’in a hankali, wanda ya bayyana a matsayin babban ƙalubale da ke kawo cikas ga yaƙi da cin hanci a jihar.

Shugaban Hukumar ya kuma nemi goyon bayan kafafen yaɗa labarai a yaƙin da ake yi da cin hanci, tare da yabawa Gwamna Umar Namadi bisa goyon bayan da yake bai wa hukumar na yin aiki bisa cikakken ‘yanci ba tare da tsoma baki ba.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi