Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda
Published: 9th, December 2025 GMT
Kwamandan sojan kasar Pakitsan Asim Munir ya ce; Dole ne Taliban ta zabi wanda za ta yi mu’amala da hulda da su, ko dai gwamnatin Pakistan din, ko kuma ‘yan ta’adda.
Asim Munir wanda a makon da ya shude aka sake tabbatar da shi akan mukaminsa na shugaban sojojin kasar, ya kara da cewa sun isar da wannan sakon zuwa ga gwamnatin Taliban ta Afghanistan.
Haka nan kuma ya ce; Pakistan kasa ce mai son zaman lafiya,amma kuma a lokaci daya ba a shirye take ba, ta bari a tsokane ta akan abinda ta shafi zaman lafiya da kare hurumin kasarta.
A gefe daya, Asim Munir ya kuma gargadi makwabtansu na gabas, wato India yana mai cewa s fito daga cikin rudani, domin anan gaba idan wani abu ya faru, to martanin da Pakistan za ta mayar zai zama cikin sauri kuma da tsanani fiye da baya.
Ministan tsaron na Pakistan ya kuma ce, sojojin kasar sun sami gagarumin ci gaba wajen bunkasa ayyukansu, da kara zama cikin shiri, da kuma hanyoyin aiki tare a tsakanin dukkanin bangarorin tsaro.
A cikin watannin bayan nan dai an sami rashin jituwa a tsakanin kasashen Pakitsan da Afghanistan wanda ya kai ga musayar wuta na kwanani masu yawa. Kasashen Turkiya da Katar ne su ka shiga tsakani da ya kai ga tsagaita wutar yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa har yanzu Amurka ba ta nuna sha’awarta ta shiga “tattaunawa mai ma’ana ba,” yana mai sake nanata cewa dole ne Washington ta fara amincewa da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya na zaman lafiya a karkashin Yarjejeniyar hana yaduwar Makaman Nukiliya ta (NPT).
A wata hira ta musamman da aka yi da kamfanin dillancin labarai na Japan Kyodo a ranar Asabar, ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa an kaiwa cibiyoyin nukiliya na Jamhuriyar Musuluncihari da bama-bamai, wanda ya lalata su sosai” a lokacin harin Isra’ila da Amurka a watan Yuni.
Araghchi ya jaddada cewa wadannan hare-haren sun kasance “wataƙila mafi girman keta dokokin kasa da kasa” da aka taba yi wa wata cibiya da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ke sa ido a kai.
Ministan harkokin wajen na Iran ya ce Jamhuriyar Musulunci da IAEA sun cimma yarjejeniya a birnin Alkahira a farkon wannan shekarar da zata duba wuraren da suka lalata.
Duk da haka, wannan tsari ya shiga cikin matsala lokacin da Amurka da kasashen Turai uku da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar nukiliya ta 2015 suka nemi a dawo da takunkumin da Majalisar Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ta sanya wa Iran a baya.
Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya kara da cewa babbar matsalar ita ce rashin amincewar Washington da ‘yancin Iran na mallakr fasahar nukiliya ta zaman lafiya, gami da wadatarwa, a karkashin NPT.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci