DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
Published: 13th, December 2025 GMT
Kungiyar ‘yan tawayen kasar DRC ta M23 ta kwace iko da wani gari mai muhimmanci bayan rushewar batun zaman lafiya
A jiya Juma’a ne dai kasar Amurka ta zargi kasar Rwanda da cewa ta keta yarjejeniyar sulhu da zaman lafita da ta kulla da DRC, tare da cewa, abinda Kigalin take yi shi ne jefa yankin zuwa yaki.
Mako daya da ya gabata ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu wacce shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa; Ta tarihi ce.” Tare da nuna fatan ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin wanda ya dade cikin fadace-fadace.
Sai dai a ranar Larabar da ta gabata da yamma mayakan kungiyar M23 wacce Rwanda take goyawa baya sun sanar da kama garin Uvira wanda daya daga cikin muhimman wuraren da suke a hannun sojojin gwamnatin kasar a gabashin kasar.
Dama dai tun a baya wasu kwararru na MDD sun zargi Kigali da cewa, ita ce mai iko da akan dukkanin hare-haren da ‘yan tawayen suke kai wa a gabashin DRC.
Jakadan Amurka a MDD Mike Waltz ya ce; Amurka ba ta ji dadin abinda ya faru ba ko kadan, domin ya rusa yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla.
Su dai ‘yan tawayen ba su cikin yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla da Amurka kai tsaye, amma da suna cikin tattaunawar da ake yi da kasar Qatar.
Amurka dai ta shiga cikin Shirin zaman lafiya a cikin DRC, domin ta sami damar dibar ma’adanai da Allah ya huwacewa wannan kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi December 13, 2025 Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
Rahotanni sun bayyana cewa shugaban kasar Iran Mas’ud pezeshkiyan ya jaddada game da mihummanci sanya hannun jari da kuma hadin guiwa a iyakoki, a matsayin abubuwan da ya fi mayar da hanakli akai a lokacin ganawarsa da shugaban kasar iraki Abdul latif rashid a gefen taron kasa da kasa na zaman lafiya a kasar Turkmenistan
Tehran da Bagadaza sun dauki hadin guiwa a matsayin babban ginshikin zaman lafiya a yankin da kuma kariya daga tsangwama daga kasashen ketare musamman Amurka da Isra’ila wadanda ke neman raba kan kasashen musulmi da kuma kawo cikas ga hadin guiwar tattalin arziki da siysa.
Ana shi bangaren shugaban kasar Iraqi ya fadi cewa iran itace makwabciya mafi muhimmanci don muna da alakar tsaro mai karfi, don haka iraki ba za ta taba mantawa da irin goyon bayan da iran take bata ba.
Gwamantin sahyuniya itace tushen haifar da rashin tsaro a yanki ba wai a bangaren hare-haren soji ba kawai , har ma a bangaren kawo cikas din tattalin arziki tsakanin kasashen makwabta. Daga karshe yayi kira da akara fadada dangantakar tsaro da tattalin arziki, manasa’antu, domin duk wani nuna kiyayya ga iran kamar nuna kiyayya ce ga Iraki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025 Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci