ACReSAL ya tallafa wa manoma da buhunan iri 6,220 a Gombe
Published: 27th, August 2025 GMT
Shirin Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL) ya raba wa ƙungiyoyin manoma 47 a Jihar Gombe, buhunan iri na zamani 6,220 don bunƙasa harkar noma.
An gudanar da rabon ne yayin taron kwanaki biyar na masu ruwa da tsaki kan kula da manyan koguna na Gongola, Gali-Lamurde da Hawal-Kilunga, wanda yake ɗaya daga cikin muhimman ayyukan ACReSAL a Najeriya.
Shugaban shirin a Jihar Gombe, Dokta Sani Adamu Jauro, ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya nuna jajircewa wajen tallafa wa manoma ta hanyar shirin.
Ya ƙara da cewa an samu nasarori kamar shuka bishiyoyi a dukkanin ƙananan hukumomi 11, rage zaizayar ƙasa da kuma kare muhalli.
Kwamishinan Noma da Kiwo na jihar, Barnabas Malle, wanda Ibrahim Sajo ya wakilta, ya yaba wa shirin tare da shawartar manoma da su yi amfani da irin wajen noma.
Ya ce gwamnati ta riga ta fara sayar da taki mai rangwame don sauƙaƙa wa manoma.
Shugaban Kungiyar Manoma (AFAN) a Jihar, Alhaji Ahmed Modibbo Nafada, ya bayyana tallafin a matsayin babban taimako musamman ga shirin noman rani.
Ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnati wajen rage rikicin manoma da makiyaya a jihar.
A nata ɓangaren, Sakatariyar Ƙungiyar Mata Manoma (SWOFON) reshen Gombe, Hannatu Iliya Yila, ta ce mambobinsu sama da 5,000 za su amfana da shirin.
Ta kuma roƙi gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su ƙara tallafa wa mata manoma da taki da magungunan kashe ƙwari.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.