ACReSAL ya tallafa wa manoma da buhunan iri 6,220 a Gombe
Published: 27th, August 2025 GMT
Shirin Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL) ya raba wa ƙungiyoyin manoma 47 a Jihar Gombe, buhunan iri na zamani 6,220 don bunƙasa harkar noma.
An gudanar da rabon ne yayin taron kwanaki biyar na masu ruwa da tsaki kan kula da manyan koguna na Gongola, Gali-Lamurde da Hawal-Kilunga, wanda yake ɗaya daga cikin muhimman ayyukan ACReSAL a Najeriya.
Shugaban shirin a Jihar Gombe, Dokta Sani Adamu Jauro, ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya nuna jajircewa wajen tallafa wa manoma ta hanyar shirin.
Ya ƙara da cewa an samu nasarori kamar shuka bishiyoyi a dukkanin ƙananan hukumomi 11, rage zaizayar ƙasa da kuma kare muhalli.
Kwamishinan Noma da Kiwo na jihar, Barnabas Malle, wanda Ibrahim Sajo ya wakilta, ya yaba wa shirin tare da shawartar manoma da su yi amfani da irin wajen noma.
Ya ce gwamnati ta riga ta fara sayar da taki mai rangwame don sauƙaƙa wa manoma.
Shugaban Kungiyar Manoma (AFAN) a Jihar, Alhaji Ahmed Modibbo Nafada, ya bayyana tallafin a matsayin babban taimako musamman ga shirin noman rani.
Ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnati wajen rage rikicin manoma da makiyaya a jihar.
A nata ɓangaren, Sakatariyar Ƙungiyar Mata Manoma (SWOFON) reshen Gombe, Hannatu Iliya Yila, ta ce mambobinsu sama da 5,000 za su amfana da shirin.
Ta kuma roƙi gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su ƙara tallafa wa mata manoma da taki da magungunan kashe ƙwari.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA