Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu
Published: 9th, December 2025 GMT
Iran, China, da Saudiyya sun kammala taronsu na uku na Kwamitin Kasashen, inda Beijing ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da karfafa dangantaka tsakanin Tehran da Riyadh.
Zaman, wanda mataimakin ministan harkokin wajen Iran Majid Takht-Ravanchi da takwarorinsa na Saudiyya Walid al-Kharaji da na China Miao Deo suka jagoranta aTehran yau Talata, a yayinsa jami’an uku sun sanya hannu kan wata sanarwa ta hadin gwiwa da ta bayyana muhimman alkawarai.
Sanarwar ta sake jaddada kudirin Iran da Saudiyya na bin dukkan tanade-tanaden Yarjejeniyar Beijing ta 2023, wanda ya sauwaka wajen dawo da huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu a shiga tsakani na China.
Dukkan kasashen biyu sun kuma jaddada muhimmancin girmama ‘yanci da hurumin kasa kamar yadda Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya, da ta Kungiyar Hadin Kan Musulunci (OIC), da dokokin kasa da kasa suka tanada.
Sanarwar ta yaba da “rawar da China ke takawa” wajen saukake tattaunawar da kuma sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar.
A nata bangaren, kasar Sin ta sake nanata shirinta na tallafawa da karfafa matakan da Tehran da Riyadh suka ɗauka don haɓaka hadin gwiwa a fannonin siyasa, tattalin arziki, al’adu, da tsaro.
Sanarwar haɗin gwiwa ta nuna ci gaba a fannin haɗin gwiwa a ofishin jakadancin, wanda ya ba da damar yin tafiya lafiya ga mahajjatan alhazan Iran sama da 85,000 da kuma mahajjatan Umrah sama da 210,000 a shekarar 2025.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha
Ministan ilimi da kere-kere na Iran Husain Simayi, wanda ya gana da jakadan kasar Turkiya anan Iran Hijabi Kalanjik ya bayyana azamar kasashen biyu domin yin aiki a wannan fagen.
Ministan ilimin da kuma fasahar kere-kere na Iran ya kuma ya kuma ce; Iran tana bayar da muhimmanci ga jami’o’in Turkiya wadanda a bisa ma’aunin duniya suke da matsayi na koli, suna kuma gabatar da su ga daliban kasar da suke son yin karatu a waje.
A nashi gefen, jakadan kasar Turkiya a Iran ya bayyana cewa; Kasashen biyu sun yi tarayya akan abubuwan da dama, tare da cewa Ankara tana bayar da muhimmanci ga alakar ilimi da al’adu da Iran.
A yayin wannan ganawar, bangarorin biyu sun yi musayar ra’ayi akan kafa tsangayoyin ilimi na hadin gwiwa domin yin nazari da bincike da kuma warware matsalolin daliban da suke karatu a kasashen biyu.
Daga cikin abubuwan da bangarorin biyu su ka tattauna da akwai yadda za a kara saukakewa daliban kasashen biyu kai da komowa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci