Aminiya:
2025-12-10@22:24:18 GMT

Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky

Published: 11th, December 2025 GMT

Shugaban mabiya Shi’a a Najeriya, Sheikh Ibraheem El-Zakzaky, ya ce zai yi hisabi da tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a gaban Allah kan abin da ya faru a Zariya a 2015.

Rikicin ya fara ne bayan da mambobin IMN sun tare wa tsohon Hafsan Soji, Tukur Buratai, hanya.

Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025 Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa

Lamarin fara a matsayin ƙaramin rikici daga baya ya rikiɗe zuwa babban al’amari, lamarin da ya sanya sojoji buɗe wa mabiyan wuta.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da kwamitin bincike na jihar, sun bayyana cewa an kashe tare binne ɗaruruwan mambobin IMN a asirce bayan faruwar lamarin.

Daga baya an kama Zakzaky da matarsa, an tsare su har zuwa 2021, kafin daga baya kotu ta wanke su.

Bayan cikar lamarin da shekara 10, Zakzaky ya ce gwamnati ta kasa ɗaukar alhakin abin da ya faru.

Ya ce: “Babu abin da aka yi. Ba su yadda cewa wani abu ya faru ba, duk da cewa kwamitin bincike ya miƙa rahotonsa tun 2016.”

Zakzaky, ya kuma zargi gwamnatin yanzu da yin shiru a kan lamarin, duk da alƙawarin da ta yi na duba rahoton da kuma biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ya ce: “Sun tabbatar mana cewa za su magance batun, amma tun daga lokacin shiru kake ji.”

Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a hannun Allah, kuma zai masa hisabi da shi ranar gobe ƙiyama.

Zakzaky ya ce: “Game da Buhari, za mu gana a Ranar Alƙiyama. Lissafin Buhari ya ƙare.”

Ya ƙara da cewa harin bai yi nasarar daƙile IMN ba, sai ma ƙara ɗaukaka sunan ƙungiyar inda ta yi fice a duniya.

Zakzaky, ya ce sun kai ƙarar lamarin kotun ƙasa da ƙasa, sannan ƙofarsu a buɗe ta ke domin tattaunawa da gwamnati.

Ya ce: “Ko ba sa son ganinmu, za su gan mu. Ko ba sa son jinmu, za su ji mu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari hari Sheikh Ibrahim El Zakzaky Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka

Marubuci kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya ce kamata ya yi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya tura ɗansa, Seyi Tinubu, zuwa Jamhuriyar Benin domin “kwantar da” yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba.

Soyinka ya soki matakin Tinubu na tura dakarun rundunar Sojojin Sama ta Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi domin kifar da Shugaba Patrice Talon daga mulki.

Ya yi wannan jawabi ne a bikin bayar da kyaututtuka na shekara karo na 20 da Cibiyar Binciken Kwakwaf ta Wole Soyinka (WSCIJ) ta shirya a Legas ranar Litinin.

Fitaccen marubucin ya tuna yadda ya ga jami’an tsaro masu makamai sosai suna gadin Seyi Tinubu a Legas.

Ya ce: “Shugaba Tinubu bai kamata ya tura Sojojin Sama da na ƙasa ba domin shawo kan wannan tayar da hankali da ke barazana ga tsaronmu da daidaituwarmu; a’a akwai hanyoyi mafi sauƙi na yin hakan.

“Bari in gaya muku inda Tinubu ya kamata ya nemi rundunar da za ta shawo kan wannan tayar da hankali, na nan a Legas ko ma a Abuja, amma babu buƙatar kiran sojojin ƙasa ko na sama.

“Zan gaya muku abin da ya faru a ɗaya daga cikin ziyarata zuwa gida watanni biyu da suka gabata, ina fita daga wani otel sai na ga abin da ya yi kama da wurin yin fim, wani matashi ya rabu da ’yan wasan ya zo ya gaishe ni cikin ladabi.

“Na kalli wurin sai na ga kusan rundunar sojoji ce gaba ɗaya sun mamaye filin otel ɗin a Ikoyi. Na koma cikin motata na tambaya wanene wannan matashin, sai aka gaya min.

“Na ga sojoji, haɗin jami’an tsaro masu makamai sosai, akalla 15 suna ɗauke da manyan makamai, abin da ya isa ya tsare karamar makwabciya kamar Benin.

“Na yi tunanin cewa a gaba mai girma shugaban ƙasa ya kamata kawai ya kira ya ce ‘Seyi je ka kwantar da fitina a can’. Na yi matuƙar mamaki har na fara neman Mashawaracin Shugaban Kasa a fannin tsaro,” in ji Soyinka.

Soyinka ya kuma ce ba Tinubu ne shugaban da ya fara mulkar Najeriya yana da ’ya’ya ba, don haka bai ga dalilin da zai sa a girke tarin jami’an tsaro kawai don su rika gadin dansa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma