Aminiya:
2025-12-13@02:45:11 GMT

Mun bai wa Akpabio sa’o’i 48 ya dawo da Sanata Natasha — SERAP

Published: 10th, March 2025 GMT

Ƙungiyar SERAP, mai fafutukar haƙƙin ɗan Adam da yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya, ta buƙaci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalisar ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

SERAP ta ce dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha ba komai ba ne illa tauye mata ’yancinta na faɗin alabarkacin baki, wanda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba ta.

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

Cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ta fitar a ranar 8 ga watan Maris, SERAP ta ce muddin ba a kiyaye wannan gargaɗi ba za ta ɗauki matakin shari’a nan da sa’o’i 48.

Wasiƙar mai ɗauke da sa hannun matamaikin shugabanta, Kolawole Oluwadare, SERAP ta ce kasancewar Natasha a matsayin Sanata ba zai haramta mata ’yancinta na faɗin albarkacin baki ba

SERAP ta nanata cewa dakatar da Sanata Natasha ya saɓa wa duk wasu tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma Dokokin Duniya da suka sahale mata ’yanci a matsayinta na bil Adama.

Ƙungiyar ta kafa hujja da sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma sashe na 9 na Kundin Kare Haƙƙoƙin ɗan Adam na Afirka, inda ta ce matakin da Majalisar Dattawan ta ɗauka ba bisa ƙa’ida ba ne kuma ya saɓa doka.

Ƙungiyar ta kuma yi Allah wadai da take haƙƙin da aka yi wa Sanata Natasha ta hanyar haramta mata wakilcin al’ummar mazaɓar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawan ƙasar.

A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawa ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.

Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.

Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa SERAP wa Sanata Natasha a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya

Aƙalla ’yan Najeriya 32 ne aka koro su daga Indiya kan zargin su da hannu a kasuwancin miyagun ƙwayoyi.

A ƙarshen watan da ya gabata, ’yan sandan Delhi da na Telangana, sun kama ’yan Najeriya 50 biyo bayan samamen da suma kai wa wata ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi mai alaƙa da ƙasashen waje.

Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC

Ana zargin mutanen da rarraba ƙwayoyi a birane da dama a Indiya, inda suke amfani da kamfanonin bayar da kaya don ɓoye ƙwayoyin da suke safara.

An gano mutanen suna da alaƙa da wani ɗan Najeriya mai suna “Nick,” wanda ake nema ruwa a jallo, kuma ana zargin yana jagorantar wannan ƙungiyar daga Najeriya.

Wasu majoyi sun bayyana cewa yana da abokan aiki aƙalla 100 a Delhi.

Masu bincike sun ce ƙungiyar tana da waɗanda ke aiki a ƙarƙashinta sama da 3,000 a Indiya kuma tana aika manyan kuɗaɗe zuwa Najeriya.

Daga cikin waɗanda aka kama, an koro ’yan Najeriya 32, yayin da wasu bakwai ke fuskantar tuhumar shari’a.

Hukumomi a ƙasar sun ana ci gaba da ce bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin