Aminiya:
2025-11-16@18:12:58 GMT

Mun bai wa Akpabio sa’o’i 48 ya dawo da Sanata Natasha — SERAP

Published: 10th, March 2025 GMT

Ƙungiyar SERAP, mai fafutukar haƙƙin ɗan Adam da yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya, ta buƙaci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalisar ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

SERAP ta ce dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha ba komai ba ne illa tauye mata ’yancinta na faɗin alabarkacin baki, wanda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba ta.

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

Cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ta fitar a ranar 8 ga watan Maris, SERAP ta ce muddin ba a kiyaye wannan gargaɗi ba za ta ɗauki matakin shari’a nan da sa’o’i 48.

Wasiƙar mai ɗauke da sa hannun matamaikin shugabanta, Kolawole Oluwadare, SERAP ta ce kasancewar Natasha a matsayin Sanata ba zai haramta mata ’yancinta na faɗin albarkacin baki ba

SERAP ta nanata cewa dakatar da Sanata Natasha ya saɓa wa duk wasu tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma Dokokin Duniya da suka sahale mata ’yanci a matsayinta na bil Adama.

Ƙungiyar ta kafa hujja da sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma sashe na 9 na Kundin Kare Haƙƙoƙin ɗan Adam na Afirka, inda ta ce matakin da Majalisar Dattawan ta ɗauka ba bisa ƙa’ida ba ne kuma ya saɓa doka.

Ƙungiyar ta kuma yi Allah wadai da take haƙƙin da aka yi wa Sanata Natasha ta hanyar haramta mata wakilcin al’ummar mazaɓar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawan ƙasar.

A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawa ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.

Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.

Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa SERAP wa Sanata Natasha a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya musanta zargin cewa yana da wani saɓani da rundunar sojin Najeriya, yana mai cewa batun rikicin fili ne ya haɗa jami’ansa da wasu sojoji sa-in-sa da a yanzu ake faman cece-kuce a kai.

Wike ya bayyana hakan ne a yayin da yake magana da manema labarai a ranar Alhamis, inda ya nanata cikakkiyar girmamawar da ya ce yana yi wa sojoji, kuma babu wata gaba a tsakaninsu.

Bebejin Katsina, Alhaji Nuhu Yashe ya rasu Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya

Ya ce abin da ya faru dai rikici ne da ya shafi wani mutum ɗaya mai fili da ake rigima a kai saboda mallakarsa ba bisa ka’ida ba, saboda ba rikici ba ne tsakaninsa da rundunar sojin gaba ɗaya ba.

Ya kuma yi watsi da rahotannin da ke cewa wai yana amfani da batun filin ne don yaƙi da rundunar soji, yana mai cewa: “Ina girmama sojoji, kuma ba ni da wata matsala da su. Duk wanda yake ƙoƙarin kawo rikici tsakanina da su, kawai yana neman a rikita jama’a ne.”

A hirarsa da manema labaran, Ministan ya kuma koka kan yadda ake cin zarafin ma’aikata idan an tura su duba irin waɗannan filayen da ake zargin an mallaka ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙuri na karya ƙa’idojin amfani da filaye ko kuma hana jami’an gwamnati gudanar da ayyukansu da ke kan ka’ida ba.

A cewar sa, babu yadda za a yi ya zauna ya yi shiru a matsayinsa na Minista alhali ana kai wa ma’aikatan gwamnati hari, “Ana dukan manyan jami’an gwamnati da suka kai matsayin darakta, ta ya za a yi su yi aikinsu bayan sun san ni ina can zaune a ofis ba zan iya kare su ba,” in ji shi.

Wike ya kuma bayar da misalin yadda wasu manyan sojoji da suka yi ritaya kamar tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo, suka samu matsalar fili, kuma su ka kira shi ya warware musu matsalar ba tare da sun tura sojoji su yi barazana ba.

Sai dai ya ce bai kamata wani ɗan ƙasa, da ya san ya yi ba daidai ba, saboda ya na da alaka da sojoji, ya hana gwamnati yin aikinta.

Rahoton ya zo ne a lokacin da ake ta tofa albarkacin baki kan takaddamar da ta barke tsakaninsa da wani matashin soja, lokacin da Wike ya je duba filin da ake zargin an mallake shi ba bisa ƙa’ida ba, inda sojan ya hana shi shiga wajen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
  • Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
  • Ma’aikatan lafiya sun tsunduma yajin aiki
  • Ma’aukatan lafiya sun tsunduma yajin aiki
  • Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika
  • Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
  • Gwamnati na jefa makomar ilimi cikin hatsari — ASUU
  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
  • Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike