Mun bai wa Akpabio sa’o’i 48 ya dawo da Sanata Natasha — SERAP
Published: 10th, March 2025 GMT
Ƙungiyar SERAP, mai fafutukar haƙƙin ɗan Adam da yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya, ta buƙaci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalisar ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.
SERAP ta ce dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha ba komai ba ne illa tauye mata ’yancinta na faɗin alabarkacin baki, wanda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba ta.
Cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ta fitar a ranar 8 ga watan Maris, SERAP ta ce muddin ba a kiyaye wannan gargaɗi ba za ta ɗauki matakin shari’a nan da sa’o’i 48.
Wasiƙar mai ɗauke da sa hannun matamaikin shugabanta, Kolawole Oluwadare, SERAP ta ce kasancewar Natasha a matsayin Sanata ba zai haramta mata ’yancinta na faɗin albarkacin baki ba
SERAP ta nanata cewa dakatar da Sanata Natasha ya saɓa wa duk wasu tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma Dokokin Duniya da suka sahale mata ’yanci a matsayinta na bil Adama.
Ƙungiyar ta kafa hujja da sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma sashe na 9 na Kundin Kare Haƙƙoƙin ɗan Adam na Afirka, inda ta ce matakin da Majalisar Dattawan ta ɗauka ba bisa ƙa’ida ba ne kuma ya saɓa doka.
Ƙungiyar ta kuma yi Allah wadai da take haƙƙin da aka yi wa Sanata Natasha ta hanyar haramta mata wakilcin al’ummar mazaɓar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawan ƙasar.
A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawa ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.
Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.
Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa SERAP wa Sanata Natasha a Majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya Antonio Guterres, ya ce za su gana da bangarorin da ke rikici da juna a Sudan a birnin Geneva, sai dai shugaban bai bayyana ranar da za a yi wannan tattaunawar ba.
Guterres ya bayyana hakan ne a lokacin zantawarsa da kafar talabijin ta Al Arabiya da ke Saudiyya wadda ta tattauna da shi game da yunkurin da majalisar ke yi ba ganin an sasanta rikicin na Sudan.
Sai dai Tattaunawar na zuwa ne a dai dai lokacin da mayakan RSF ke ci gaba da kwace yankuna a cikin kasar tare da kisan fararen hula da dama, da kuma tilastawa miliyoyin barin matsugunansu.
Tun a tsakiyar watan Afrilun shekarar 2023 ne yaki ya barke tsakanin dakarun Sojin Sudan karkashin Janar Abdelfattah al-Burhan da kuma dakarun kai daukin gaggawa na RSF karkashin Muhmmad Hamdan Dagalo ,rikicin da ya juye zuwa yaki mafi muni da kasar ta gani a tarihi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Birtaniya Ta yi Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci