Leadership News Hausa:
2025-12-11@17:11:14 GMT

Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce

Published: 11th, December 2025 GMT

Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce

Zuwa karfe 5:41 na daren ranar 7 ga watan Disamba, fim din Amurka “Zootopia 2” wanda aka fara nuna wa kwanaki 12 da suka wuce (tun daga ranar 26 ga Nuwamba), ya samu kudaden shiga a cikin kasar Sin da yawansa ya wuce yuan biliyan 30 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 424.8, adadin da ya zarce kudaden shiga da ya samu a kasashen Arewacin Amurka, har ya sa kasar Sin ta zama kasa mafi taka rawa wajen samar da kudin shiga ga wannan fim a duniya.

Hakan kuma ya nuna yadda Sin ke da babbar kasuwar fina-finai.

Ibrahim Akopari Ahmed, jami’in kula da harkokin cinikayya a Najeriya, a zantawarsa da dan jarida a baya, ya taba bayyana cewa, “Najeriya na daya daga cikin manyan kasashe mafiya karfin tattalin arziki a Afirka, kuma sana’o’i masu alaka da samar da hidimomi ne ke ba da gudunmawa mafi yawa ga GDPn kasar, wanda ya zarce kashi 50 cikin 100 na GDP. Saboda haka, Najeriya tana da karfi a bangaren sana’o’in samar da hidimomi, musamman a fagen nishadantarwa, kamar masana’antun samar da fina-finai ta Najeriya (Nollywood). A wannan fage, muna kan gaba a Afirka.”

Najeriya babbar kasa ce ta samar da fina-finai a Afirka, yayin da Sin ke da babbar kasuwar kallon fina-finai. Hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ta fannin fina-finai yana da makoma mai haske, kuma a hakika Sin da Najeriya na karfafa hadin gwiwa a wannan fanni. Alal misali, an gudanar da bikin fina-finai na kasa da kasa na Zuma karo na 15 a farkon wannan watan a babban birnin Najeriya Abuja, inda aka nuna fina-finai biyu daga Sin: wato “Rooting” da “Shen Zhou 13”. Babban manajan kamfanin samar da fina-finai ta Najeriya Ali Nuhu ya bayyana cewa, yana fatan ta wannan taron, za a kara zurfafa hadin gwiwar sana’o’in samar da fina-finai tsakanin Sin da Najeriya. Muna fatan a karkashin tsarin “dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka” da ma sauran irin dandalin hadin gwiwa, Sin da Najeriya za su kara karfafa huldar al’adunsu, ta yadda a nan gaba za a samu karuwar shigowar kyawawan fina-finai daga Najeriya zuwa nan kasar Sin, don baiwa masu kallo na kasar Sin karin damammaki na fahimtar Afirka, musamman Najeriya.(Mai zane da rubutu: MINA)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya December 4, 2025 Ra'ayi Riga Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi December 4, 2025 Ra'ayi Riga Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu November 29, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da fina finai hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya yi wata waqa da ya yi wa laqabi da suna ‘Arewa’.

Muhsin wanda ya fi qwarewa a fagen waqoqin ‘Gambara’, da aka fi sani da Hip Hop, bayyana wa Aminiya cewa, halin da Arewacin Nijeriya ya shiga na rashin tsaro shi ne jigon waqarsa.

A cikin waqar haziqin mawaqin, ya yi tsokaci a kan yadda shugabanni a Arewa suka yi biris da halin da talakawa suka tsinci kansu a ciki na barazanar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro. Inda yake qoqarin ganin ya jawo hankalin masu muli da ma talakawa don su farka daga barci.

Matashi mawaqin ya ce, “waqata mai taken ‘Arewa’, waqa ce da zan ce na yi ta ne saboda in tayar da shugabanni da kuma talakawan Arewacin Nijeriya daga barci. Domin kuwa ga gobara nan ta tunkaro mu daga kogi amma kuma da alamu babu wanda ya damu da ita.”

Da yake amsa tambayar ko me ya sa ya zavi yin amfani da waqa don wayar da kan jama’a kan muhimmancin haxin kai don tunkarar wannan matsala? Mawaqin zamanin sai ya ce, “ka san kowa da dutsen da ke hannunsa zai yi jifa. Don haka tunda yake ina da fasahar waqa, shi ya sa na ga wannan ita ce, kawai hanya xaya tilo da tafi sauqi wajena in isar da wannan muhimmin saqo.”

Matashin ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu akwai fitattun mawaqan da suka yi waqoqi kan abin da ya shafi tavarvarewar tsaro a qasa. Amma duk da haka, ya dace manya fitattun mawaqa na zamani da duniya ta san su, su qara qaimi wajen wayar da kan matasa don su guji shiga ayyukan laifi da ke jefa qasa cikin rashin tabbas.

SKD Arewa, ya kuma shawarci matasan mawaqa da su rungumi karatu, domin a cewarsa, ilimi ne zai taimaka musu wajen inganta sana’o’insu kuma ya basu damar amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata fasahohinsu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba