Fiye da fursunoni 40 na Isra’ila da ke hannun kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa ne suka mutu a hare-haren da sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka yi ta kaddamarwa kan al’ummar yankin tun  daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, kamar yadda wani rahoton baya-bayan nan na jaridar New York Times ya bayyana.

Binciken, wanda jaridar ta New York Times ta buga a wannan  Asabar, ya ce fursunoni 41 daga cikin fursunoni 251 na Isra’ila da ake tsare da su a Gaza, an kashe su ne ta hanyar bama-bamai da Isra’ila ta yi ta jefawa kan yankin.

Binciken ya dogara ne akan rahotanni da kuma binciken soji kan mutuwar fursunonin, da hirarraki da sojoji da jami’an Isra’ila, da kuma wasu daga cikin dangin wadanda aka kama.

Jaridar ta yi nuni da dagewar da Netanyahu ya yi na ci gaba da yakin Gaza domin kubutar da wadanda ake tsare da su ta hanyar daukar matakan soji maimakon daukar matakin kawo karshen fadan ta hanyar tattaunawa da kuma musayar fursunoni, wanda kuma bayan kisan dubun-dubatar mutanen Gaza, da ma wasu daga cikin fursunonin Isra’ila, Netanyahu ya dawo ya amince da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha

Hukumar EFCC ta tsare tsohon Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami, saboda binciken da ya shafi dawo da wani ɓangare na kuɗaɗen Abacha.

Hukumar ta kira Malami a makon da ya gabata, inda ta yi masa tambayoyi kan wani bincike da ta ke inda ta sake shi daga bisani, amma yanzu ta tsare shi.

Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Malami ya ce bai aikata komai ba, kuma ba shi da alaƙa da abin da ake zargi.

A cikin wata sanarwa, ya ce: “Ba a taɓa zargina, gayyata ko bincikena game da tallafa wa ta’addanci ba. Duk wani yunƙuri na danganta ni da irin wannan laifi ƙarya ne.”

Ya ƙara da cewa rahotannin kafofin yaɗa labarai ke watsawa sun yi masa mummunar fassara.

“Ba daidai ba ne a ce aikina na gwamnati ya zama hujja ta tallafa wa ta’addanci. A lokacin aikina, na yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, ba goyon bayansa ba.”

EFCC ba ta fitar da wata sanarwa kan tsare Malami ba.

Haka kuma bai wallafa komai a shafukan sada zumunta ba tsawon kwanaki huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya