Fiye da fursunoni 40 na Isra’ila da ke hannun kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa ne suka mutu a hare-haren da sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka yi ta kaddamarwa kan al’ummar yankin tun  daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, kamar yadda wani rahoton baya-bayan nan na jaridar New York Times ya bayyana.

Binciken, wanda jaridar ta New York Times ta buga a wannan  Asabar, ya ce fursunoni 41 daga cikin fursunoni 251 na Isra’ila da ake tsare da su a Gaza, an kashe su ne ta hanyar bama-bamai da Isra’ila ta yi ta jefawa kan yankin.

Binciken ya dogara ne akan rahotanni da kuma binciken soji kan mutuwar fursunonin, da hirarraki da sojoji da jami’an Isra’ila, da kuma wasu daga cikin dangin wadanda aka kama.

Jaridar ta yi nuni da dagewar da Netanyahu ya yi na ci gaba da yakin Gaza domin kubutar da wadanda ake tsare da su ta hanyar daukar matakan soji maimakon daukar matakin kawo karshen fadan ta hanyar tattaunawa da kuma musayar fursunoni, wanda kuma bayan kisan dubun-dubatar mutanen Gaza, da ma wasu daga cikin fursunonin Isra’ila, Netanyahu ya dawo ya amince da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000