Fiye da fursunoni 40 na Isra’ila da ke hannun kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa ne suka mutu a hare-haren da sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka yi ta kaddamarwa kan al’ummar yankin tun  daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, kamar yadda wani rahoton baya-bayan nan na jaridar New York Times ya bayyana.

Binciken, wanda jaridar ta New York Times ta buga a wannan  Asabar, ya ce fursunoni 41 daga cikin fursunoni 251 na Isra’ila da ake tsare da su a Gaza, an kashe su ne ta hanyar bama-bamai da Isra’ila ta yi ta jefawa kan yankin.

Binciken ya dogara ne akan rahotanni da kuma binciken soji kan mutuwar fursunonin, da hirarraki da sojoji da jami’an Isra’ila, da kuma wasu daga cikin dangin wadanda aka kama.

Jaridar ta yi nuni da dagewar da Netanyahu ya yi na ci gaba da yakin Gaza domin kubutar da wadanda ake tsare da su ta hanyar daukar matakan soji maimakon daukar matakin kawo karshen fadan ta hanyar tattaunawa da kuma musayar fursunoni, wanda kuma bayan kisan dubun-dubatar mutanen Gaza, da ma wasu daga cikin fursunonin Isra’ila, Netanyahu ya dawo ya amince da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kasashen Larabawa da musulmi 8 ne suka gamu suka ki amincewa da shirin HKI na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran tanakalto ministocin harkokin kasashen waje na kasashen Saudia, Masar, Jordan, da UAE Pakisatan Turkey da kuma Qatar sun bada bayanin hadin giwa daga kasashen Saudiya kan cewa shirin HKI na bude Kofar Rafah ta fcewar Falasdinawa Kawai ba tare da shigowa ba, baa bin amincewa bane.

Bayanin ya kara da cewa, wannan shirin yana da hatsari, kuma shiri ne wanda zai hana kafuwar kasar Falasdinu idan har duk wanda ya fit aba zai sake shigowa ba.  

Jami’an diblomasiyyar sun bayyana cewa, shirin ya sabawadokokin kasa da kasa, kuma  barazana ce ga samuwar kasar Falasdinu nan gaba. Dama HKI ta dade tana neman damar korar Falasdinawa daga Gaza, har abada, don hana su kokarin kafa kasar Falasdinu a kasarsu da aka mamaye.

Kasashen 8 sun bukaci a kawo karshen hare-haren da sojojin HKI suke kaiwa kan yankuna Falasdinawa a Gaza, ta kyale kayakin agaji su shiga sannan su bada dama a sake gina yankin. Sun bukaci a sake maida gwamnatin Hamas a gaza saboda ta ci gaba a harkokin gudanarwa.

Daga karshe sun bayyana cewa a shirye suke yi aiki don aiwatar da kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2803.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabi Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi
  •   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba
  • Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi
  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya
  • MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
  • Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin  Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Yankin Gaza