Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
Published: 13th, December 2025 GMT
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Karamar Hukumar Birnin Kudu ta bada tabbacin hada hannu da bankin ajiya na Savings and Loan na Jihar Jigawa domin habaka tattalin arziki.
Shugaban Karamar hukumar, Dr. Builder Muhammad Uba ya bada wannan tabbaci a lokacin da Manajan bankin, Babandi Isah Gumel ya kai masa ziyara.
Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta ci gaba da mu’amulla da bankin wajen ganin ma’aikatan wucin gadi na bude asusun ajiya a bankin.
Ya kuma bayyana farin cikinsa kan wannan ziyara da kuma karrama shi da aka yi.
A jawabinsa, Manajan bankin Savings and Loan na Jihar Jigawa, Babandi Isa Gumel, ya ce sun karrama shugaban Karamar hukumar ne bisa daukar ma’aikatan wucin gadi a karamar hukumar ta birnin kudu.
Yace Dr Muhammad Uba ya dauki ma’aikatan da dama a fannin kiwon lafiya da ilimi wato B-health da B-teach da kuma amincewa da yin mu’amulla da bankin.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Karramawa Karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025
Labarai Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani December 13, 2025
Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025