Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Karamar Hukumar Birnin Kudu ta bada tabbacin hada hannu da bankin ajiya na Savings and Loan na Jihar Jigawa domin habaka tattalin arziki.

Shugaban Karamar hukumar, Dr. Builder Muhammad Uba ya bada wannan tabbaci a lokacin da Manajan bankin, Babandi Isah Gumel ya kai masa ziyara.

Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta ci gaba da mu’amulla da bankin wajen ganin ma’aikatan wucin gadi na bude asusun ajiya a bankin.

Ya kuma bayyana farin cikinsa kan wannan ziyara da kuma karrama shi da aka yi.

A jawabinsa, Manajan bankin Savings and Loan na Jihar Jigawa, Babandi Isa Gumel, ya ce sun karrama shugaban Karamar hukumar ne bisa daukar ma’aikatan wucin gadi a karamar hukumar ta birnin kudu.

Yace Dr Muhammad Uba ya dauki ma’aikatan da dama a fannin kiwon lafiya da ilimi wato B-health da B-teach da kuma amincewa da yin mu’amulla da bankin.

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karramawa Karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Labarai Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a