Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Jigawa ta bayyana damuwa kan jinkirin shari’a wajen gurfanar da masu laifin rashawa, inda ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 479 da suka shafi cin hanci, amana da sauran laifuka makamanta a wannan shekarar ta 2025.

Shugaban Hukumar, Barista Salisu Abdul ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai kan nasarorin da hukumar ta samu da ƙalubalen da ta fuskanta a shekarar

Taron manema labaran wani ɓangare ne na shirye-shiryen hukumar na bikin Ranar Yaƙi da Cin Hanci ta Duniya.

Barista Salisu Abdul ya ƙara da cewa, cin hanci babban abin da ke janyo koma-baya ne ga Najeriya a fannoni daban-daban na rayuwar jama’a da tattalin arzikin ƙasa.

A cewarsa, babban burin hukumar wacce aka kafa a watan Fabrairun 2024 shi ne ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa a jihar, tare da inganta gaskiya, ɗabi’a, da amana a harkokin gwamnati da na kamfanoni masu zaman kansu, da al’amuran zamantakewa da tattalin arziki.

 

Shugaban ya ce, a wannan shekarar hukumar ta shirya horo ga manyan ma’aikatan gwamnati da jami’anta, tare da wayar da kan jama’a kan rawar da kowa ya kamata ya taka wajen yaƙi da cin hanci.

“Yayin da muke ci gaba da wayar da kai sosai, za mu ƙara haɗa kai da sauran hukumomin yaƙi da cin hanci, da hukumomin gwamnati da masu zaman kansu, da jama’a domin mu fi mai da hankali wajen dakile cin hanci fiye da magance shi bayan ya faru,” in ji shi.

Ya kuma ce, hukumar za ta rungumi fasahar zamani a ayyukanta don samun ingantaccen sakamako.

Barista Salisu Abdul ya bayyana cewa, daga cikin shari’o’in 479, guda 110 sun shafi cin hanci da damfarar kuɗi, yayin da 375 suka shafi rikicin kadarori, sabanin iyali, da ma’amalar kasuwanci da ta ci tura, inda aka warware shari’o’i 107 cikin sulhu.

Ya kara da cewa an dawo da fiye da Naira miliyan 385 da kadarorin da darajarsu ta kai daruruwan miliyoyi, aka kuma mika su ga masu su.

Sai dai ya nuna damuwa kan yadda alkalai ke tafiyar da shari’o’in a hankali, wanda ya bayyana a matsayin babban ƙalubale da ke kawo cikas ga yaƙi da cin hanci a jihar.

Shugaban Hukumar ya kuma nemi goyon bayan kafafen yaɗa labarai a yaƙin da ake yi da cin hanci, tare da yabawa Gwamna Umar Namadi bisa goyon bayan da yake bai wa hukumar na yin aiki bisa cikakken ‘yanci ba tare da tsoma baki ba.

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Ƙorafe ƙorafe Jigawa Shari a yaƙi da cin hanci

এছাড়াও পড়ুন:

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya ce yawan yara marasa zuwa makaranta a Najeriya a barazana ce da ke buƙatar haɗin gwiwa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki.

Shettima ya yi wannan bayani a taron Zauren Ilimin Najeriya na 2025 da aka gudanar a Abuja, wanda Kungiyar Gwamnonin Najeriya tare da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da abokan hulɗa suka shirya.

Ya ce matsalar ilimi ba za ta iya warwarewa da ƙoƙarin gwamnati kaɗai ba, yana mai jaddada cewa: “Yawan yaran da ba sa zuwa makaranta bukatar gaggawa ce ta ƙasa da ke buƙatar haɗin kai tsakanin Gwamnatin Tarayya, jihohi, kananan hukumomi da al’umma.”

Shettima, wanda mai ba shi shawara na musamman Aliyu Modibbo Umar ya wakilta, ya ce dole malamai su samu horo mai kyau, kulawa da kuma kima a matsayinsu na ƙwararru domin a samu ingantaccen ilimi.

An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba

Ya kuma yi kira da a faɗaɗa ilimin sana’o’i da fasaha domin matasa su samu ƙwarewar da za ta taimaka musu a kasuwa. Ya ce hakan na buƙatar kuɗi masu dorewa da aka tsara yadda ya kamata.

Mataimakin Shugaban Kasa ya bayyana cewa duk da ƙarin kuɗin da gwamnati ta ware wa ilimi daga Naira tiriliyan 1.54 a 2023 zuwa Naira tiriliyan 3.52 a 2025, gibin kuɗi ya yi yawa fiye da abin da gwamnati za ta iya ɗauka ita kaɗai.

Ya ambaci ƙarin kuɗin da aka ware wa hukumar TETFUND, UBEC da asusun tallafin ilimi na NELFUND, ciki har da Naira biliyan 86.3 da aka raba wa ɗaliban jami’a sama da 450,000 a ƙarƙashin tsarin lamunin ɗalibai.

Sai dai ya jaddada cewa gina tsarin ilimi mai ɗorewa na buƙatar haɗin gwiwa daga kamfanoni masu zaman kansu, shugabannin masana’antu, ƙungiyoyin tsoffin ɗalibai, masu bayar da tallafi da al’umma.

Shettima ya ce: “Dole mu wuce tsarin gwamnati kaɗai wajen bayar da kuɗi, mu rungumi haɗin gwiwa da zai tallafa wa dakunan gwaje-gwaje, cibiyoyin bincike, cibiyoyin sana’o’i, ƙungiyoyin kirkire-kirkire da asusun tallafi.”

Ya kuma bukaci kananan hukumomi da masarautu su ɗauki nauyin gine-ginen makarantu, gyara, tsaro da kuma kulawa da malamai.

Shettima ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a taron da su jajirce wajen samar da kuɗin ilimi mai dorewa, yana mai cewa haɗin kai ne kaɗai zai iya sauya tsarin ilimi a Najeriya tare da shirya matasa domin fuskantar duniyar zamani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Za a Yi wa Yara 194,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso