Shugaba Masoud Pezeshkian ya ce manufar Iran ta ginu ne kan  samar da hadin kai a yammacin Asiya, kamar yadda kuma ta yi imanin cewa duk wani rikici da tashin hankali a yankin to zai illata kowa.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da Firaministan Norway Jonas Gahr Støre a yammacin waannan Lahadi, inda suka tattauna kan muhimman batutuwa ad suka shafi alaka tsakanin kasashen biyu, da kuma sauran batutuwa na yankin da kuma na kasa da kasa.

Shugaban na Iran ya kara da cewa, Haramtacciyar Kasar Isra’ila na neman yada karya dangane da batun ayyukan nukiliyar Iran  a matsayin tushen rashin tsaro a yankin.

Har ila yau ya jaddada cewa Iran ba ta taba neman kera makaman nukiliya ba.

Shugaba Pezeshkian ya ce Iran ta ba da hadin kai kuma za ta ci gaba da hada kai da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA domin kara tabbatar wa duniya da cewa shirinta na ayyukan farar hula ne, sabanin abin da makiyanta suke yadawa..

A nasa bangaren Firaministan Norway ya ce, kasarsa a shirye take ta ba da duk wani taimako da nufin warware matsalolin da ke faruwa a yankin yammacin Asiya a cikin lumana, tare da kara karfafa alakarta da kasar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum

Jami’an tsaro da ke rakiyar tawagar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun daƙile wani harin Boko Haram a kusa da garin Gujba a Jihar Yobe.

Gwamnan da tawagarsa na kan hanyarsu ta komawa Maiduguri daga Biu lokacin da suka haɗu da ’yan ta’addan, wanda hakan ya tilasta musu tserewa bayan musayar wuta.

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike

Bayanai sun ce dakarun tawagar sun ƙwato bindigogi, harsasai, babur, tare da ceto wasu fasinjoji da aka sace.

Wani direba da aka ceto, Malum Ari, ya bayyana yadda maharan suka tare hanyar: “Sun karɓe motata suka tilasta mana kwanciya a ƙasa.

“Amma da suka hango tawagar gwamna, sai suka firgita suka tsere. Wani daga cikinsu ya faɗi a kasa sau biyu kafin ya tsere saboda tsananin firgici.”

Wani fasinja da aka ceto ya koka kan yadda hare-haren suka zama ruwan dare: “Boko Haram na tare hanya da tsakar rana. Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.”

Wannan na zuwa ne kwana uku bayan da ’yan ta’adda suka kai hari gari Gujba, inda suka kashe wani ɗan sa-kai mai suna Modu Bulama, tare da ƙone gidaje da shaguna.

Wani jami’in tsaro da ya shaida lamarin ya ce, “Waɗannan ’yan ta’adda sun ƙara samun ƙarfi sosai. Suna kai hare-hare ba tare da tsoro ba. Dole a ɗauki ƙwararan matakai don tabbatar da tsaro.”

A baya-bayan nan ne mayaƙan Boko Haram suka sace wani Farfesan Jami’ar Soji ta BIU da ke Jihar Borno (NAUB) da wasu fasinjoji.

Haka kuma sun sace wani alƙalin kotun Borno, wanda daga baya suka sako shi bayan biyan kuɗin fansa mai yawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  • Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci
  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • ’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio
  • Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare
  • Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum
  • Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne