Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”

Masana a Taron Abuja na Tattaunawa kan Tattalin Arziki Kasa da ake wa lakabi da Abuja Economic Dialogue 2025 da Kamfanin Ignite Capital ke shiryawa duk shekara da haxin gwiwar Kamfanin Innovision Global Consulting sun yi hasashen cewa, za a samu saukar kayan masarufi da Karuwar samar da ayyukan yi a faxin kasa a shekara mai zuwa ta 2026.

Masana tattalin arzikin da suka yi fashin baki kan yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a cikin watanni tara da suka gabata, a taro sun haxa da Dakta Paul Arinze, Shugaban Kamfanin Bincike da Nazari kan harkokin tattalin arziki mai suna Pedestal Africa da Dakta Umar Kwairanga Kwararre kan harkokin tattalin arziki da ayyukan banki da Dakta Sara Alade tsohuwar Mataimakiyar Gwamnan Babban Banki na Kasa kuma Kwararriya a fagen tattalin arziki da kuma Dakta Nuruddeen Zauru wani masanin tattalin arziki.

A cikin sakonsa na fatan alheri tsohon Mataimaki Shugaban Kasa kuma Sardaunan Zazzau, Alhaji Namadi Sambo ya yi tsokaci kan bukatar cewa, lokaci ya yi da gwamnati za ta xauke cigaban da take ikirarin samu a fannin tattalin arziki daga alkalumma a takarda zuwa aiwatarwa a aikace. Ta yadda talakawa za su ga sauKin da ci gaban da aka samu kasa ba labari ba.

Da yake tofa albarkacin bakinsa a taron tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ta Qasa, Alhaji Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu ya dace shugabanni a Nijeriya su san cewa, ba tare da samar da cikakken tsaro da dauwamammiyar wutar lantarki ba tattalin arzikin Nigeriya zai ci gaba da yin kwan gaba-kwan baya.

Saraki ya kuma yi kira da gwamnati da rinka karfafa gwiwar kamfanonin cikin kasa ta hanyar sayen kayayyakin da suke samarwa.

Mai masaukin baki kuma Shugaban Kamfani Ignite Capital, Bukar Abba Kyari ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu, kan irin matakan da yake xauka don inganta tattalin arzikin kasa tare da tallafa wa matasa kan harkokin da suka shafi kasuwancin zamani na yanar gizo.

 

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin tattalin arziki

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya zargi ‘yan siyasan Nijeriya da zagon kasa ga ci gaban kasar ta hanyar daukar mukaman gwamnati a matsayin gadon gidansu a maimakon amanar jama’a. Da yake jawabi a ranar Laraba a yayin taro karo na 15 mai taken, “ya Isa haka” da ya gudana a jihar Legas, Sanusi II ya ce manyan ‘yan siyasa a fadin Nijeriya, suna ci gaba da yin zagon kasa ga ci gaban kasa saboda suna fifita kansu, iyalansu da abokan huldarsu fiye da kasar da ‘yan kasarta. Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara Ya yi takaicin cewa, gazawar Nijeriya a wasu wurare ba haka nan take ba, face sakamakon shugabanci na son kai. A cewarsa, “mukaman gwamnati na su ne, da iyalansu, da mutanen da ke kusa da su, babu ruwansu da ‘yan kasar. Amma mukaman gwamnati na ‘yan kasa ne.” Sarki Sanusi na II ya yi kira ga matasan Nijeriya da su yi watsi da tsarin da ‘yan siyasa marasa kishin kasa suka kafa na amfani da “kabilanci, rikice-rikicen addini, da kuma son kai,” a maimakon haka, su hada kai don gina kasa da za ta cika mafarkanta. Ya jaddada cewa, ikon kasa yana hannun ‘yan kasa ne, ba ‘yan siyasa ba, ya kara da cewa, kowane mutum yana da rawar da zai taka a hakkinsa don tallafawa Nijeriya. ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano December 11, 2025 Labarai Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto December 11, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima