Daga Usman Muhammad Zaria 

Aikin rigakafin watan Disamba a karamar hukumar Sule-Tankarkar ta jihar Jigawa ya samu gagarumar nasara, yayin da iyaye suka fito kwansu da kwarkwata domin tabbatar da cewa an yi wa ’ya’yansu cikakken rigakafi.

Wasu daga cikin iyayen da suka kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna sun bayyana jin dadinsu kan yadda aka gudanar da aikin cikin kwanciyar hankali.

 

Daya daga cikinsu, Malama Ummahani Danbala, ta ce an wayar da kan jama’a sosai ta hannun mata ’yan sa-kai a unguwarsu, inda aka karfafa gwiwar iyaye mata su kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna.

Malam Yunusa, wani mai sa ido a karamar hukumar, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da aikin rigakafin a yankin.

A cewarsa, aikin wayar da kan jama’a ya yi matukar tasiri, domin mutane na kawo ’ya’yansu da kansu ba tare da kin amincewa da rigakafin ba.

Yunusa ya bayyana cewa duk da kasancewar karamar hukumar tana kan iyaka, aikin ya gudana cikin nasara, sakamakon hadin gwiwar da aka samu daga dukkan masu ruwa da tsaki.

Ya kara da cewa ana sa ran rigakafin yara kusan 45,221, inda aka yi niyyar kai rigakafin makarantu da wuraren ibada domin gano yaran da ba a musu ba.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa karamar hukumar na da cibiyoyin lafiya guda 28, kuma aikin rigakafin ya gudana cikin kwanciyar hankali a al’ummomin Ablasu, Kings, Amanda, Togai, Nagwamatse da Hannun Giwa.

Ana sa ran kammala zagayen rigakafin shan inna na watan Disamba a ranar Juma’a a fadin kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Sule Tankarkar karamar hukumar rigakafin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar bunkasa ilimin manya ta jihar Jigawa tace za ta kashe naira milyan 400 wajen gudanar da harkokin ta a sabuwar shekara ta 2026.

Shugaban hukumar. Dr. Abbas Abubakar Abbas, ya bayyana haka lokacin kare kiyasin kasafin kudin hukumar a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Dr Abbas Abubakar Abbas ya ce hukumar za ta yi amfani da kudaden wajen inganta shirye shiryen koyon karatu da rubutu ga manya maza da mata da na ci gaba da karatu don kammala karatun sakandare da na masu son sake jarrabawar sakandire da koyon karatu ta Rediyo da cibiyoyi daban daban da ke fadin jihar.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumarsa , shugaban hukumar makarantun Tsangaya, Dr. Hamisu Maje, ya ce sun yi kiyasin naira milyan dubu 3 da milyan 500 tare da kudurin kammala aikin ginin makarantun Tsangaya guda 3 da ke Ringim da Kafin Hausa da Dutse.

Ya ce an yi tanadi domin kafa cibiyar koyar da sana’oi da gidajen alarammomi da masallaci tare da samar da ruwan sha da wutar lantarki a kowacce makaranta.

Dr. Hamisu Maje ya kuma bayyana cewar hukumar za ta gyara makarantun Tsangaya guda 7 da aka gada daga gwamnatin tarayya da ke sashen jihar domin karfafa tsarin ilimin makarantun Tsangaya na zamani.

A daya bangaren kuma, kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse da Kuma hukumar bada tallafin karatu ta jihar sun kare kiyasin kasafin kudadensu a gaban kwamatin kula da manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Da ya ke kare kiyasin kasafin kudin, shugaban kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse, Dr. Ahmad Badayi, ya ce sun yi kiyasin fiye da naira milyan 700 wadda daga ciki an kebe naira milyan 330 domin sayo kayayyakin aiki a dakin gwaje-gwaje da koyon aikin hannu da gyaran ofisoshi, yayin da za a yi amfani da ragowar kudaden wajen kammala manyan ayyuka.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumar sa, shugaban hukumar bada tallafin karatu ta jihar Malam Sa’idu Magaji, ya ce sun yi kiyasin kashe naira milyan dubu 10 domin bada tallafin karatu na cikin gida da na kasashen waje.

A nasa jawabin, shugaban kwamatin kula da ilimin manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Sule Tankarkar Alhaji Muhammad Abubakar Sa’id, ya jaddada bukatar ganin masu ruwa da tsaki a bangaren manyan makarantu sun yi dukkan mai yiwuwa domin inganta harkokin ilimi mai zurfi a sabuwar shekara.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin