Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau
Published: 14th, December 2025 GMT
Sanarwar ta Sulaiman ta ƙara da cewa, asusun cibiyar ya mayar da hankali ne wajen ingantawa tare da samar da isassun kuɗaɗe don ƙarfafa wa jihohi 36 wajen samar da kula da lafiya a matakin farko mai aminci da inganci.
Sanarwar ta ce, “Jihar Zamfara ta sami kyautar Dalar Amurka 500,000 a matsayin wacce ta zama zakara a yankin Arewa maso Yamma wajen kula da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko.
“Wannan karramawa da aka miƙa wa Gwamna Dauda Lawal, tallafi ne na haɗin gwiwa tsakanin ‘Bill and Melinda Gates Foundation, United Nations International Children’s Emergency Fund (UNICEF), Dangote Foundation da National Primary Healthcare Development Agency (NPHCDA).’
“Wannan karramawa, ta nuna a fili cewa ayyana dokar ta-baci da Gwamna Lawal ya yi wa fannin kula da lafiya, abin yana haifar da makamako mai kyau da aka tsammata.
“Zamfara da sauran jihohin da suka yi zarra a wannan fanni daga yankunan Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, Kudu maso Yamma, Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu, duk sum raba kuɗi Dalar Amurka Miliyan 6.1 a karo na uku na wannan karramawa.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Hukuncin Kisa Kan Maryam Sanda December 12, 2025
Manyan Labarai Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja December 12, 2025
Manyan Labarai NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba December 12, 2025