Aminiya:
2025-12-09@17:55:03 GMT

Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi

Published: 9th, December 2025 GMT

An kori direban Kamfanin Simintin Mangal bayan jami’an tsaro sun kama shi da motar kamfanin dauke da yara 21 da ake zargin an yi safarar su ne daga jihohin Arewa.

Gwamnatin jihar ta ce yaran da ke tsakanin shekaru 6 zuwa 17 an kama su ne bisa sahihan bayanan sirri.

Sanawar da Kwamishinan Yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya fitar bayan kama yaran a cikin motar ta yi zargin za a yi amfani da su wajen horar da ’yan ta’adda.

Kamfanin ya nesanta kansa daga lamarin, ya ce direban ya karya dokokin aiki, kuma ya jefa al’umma cikin haɗari.

Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Babban Manajan sashin kula da mulki na kamfanin, Musa Umar, ya ce ba da izininsa direban da aka kama ya fita da motar ba, domin iya jigilar siminta kaɗai suke yi ba ɗaukar fasinja ko yara ba.

Gwamnatin Kogi ta ce za a mika yaran ga gwamnatocin jihohinsu bayan tantancewa, yayin da duk wanda aka samu da hannu a safarar zai fuskanci shari’a bisa dokokin hana safarar yara da kare haƙƙin yara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yara

এছাড়াও পড়ুন:

Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki

Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta bayyana cewa ta dakile wani yunkurin juyin mulki, bayan da wasu sojojin ƙasar suka sanar da cewa sun hambarar da shugaba Patrice Talon a gidan talabijin na kasar.

Talon, mai shekaru 67, tsohon dan kasuwa ne wanda aka yiwa lakabi da “Sarkin Auduga na Cotonou”, zai mika mulki a watan Afrilun shekara ta 2025 dake ƙaratowa, bayan shafe shekaru 10 a kan karagar mulki wanda ke nuna samun ci gaban tattalin arziki mai inganci.

Da sanyin safiyar Lahadi ne sojojin da ke kiran kansu da suna “Kwamitin Soji na sake farfado da ƙasa” (CMR), suka gabatar da wata sanarwa a gidan talabijin na kasar cewa sun gana kuma sun yanke shawarar cewa “An tsige shugaba Patrice Talon daga mukamin shugaban jamhuriyar”.

Sai dai jim kadan bayan sanarwar, wata majiya da ke kusa da Talon ta shaida wa kamfanin dillacin labaru na AFP cewa shugaban yana cikin koshin lafiya tare da yin Allah wadai da masu yunkurin juyin mulkin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  •  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba
  • Kungiyar AU Ta yi Tir Da Harin Da RSF  Takai A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
  • Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi