Aminiya:
2025-12-11@17:11:49 GMT

NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa

Published: 11th, December 2025 GMT

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta Najeriya (NAFDAC) ta lalata kayayyaki marasa inganci da suka kai sama da Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa.

Kayayyakin da aka ƙwato daga jihohin Arewa ta Tsakiya da suka haɗa da Nasarawa, Benuwe da Kogi da Filato, an lalata su ne a wurin zuba shara a Angwan Rere da ke Lafiya.

Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe

Darakta Janar ta Hukumar NAFDAC, Farfesa Christianah Adeyeye, wanda Daraktan shiyyar Arewa ta Tsakiya, Mista Kenneth Azikiwe ya wakilta, ya bayyana cewa an ƙwace kayayyakin ne a lokacin gudanar da aikin sa ido.

Ta kuma jaddada cewa hukumar na da burin hana waɗannan kayayyaki masu hatsarin gaske su sake shiga kasuwa tare da haifar da illa ga jama’a.

“Wasu daga cikin waɗannan kayayyakin an ɓoye su ne da gangan, an kuma sake sabunta su da gangan bayan ƙarewar wa’adin amfanin da su, an ajiye su da mugun nufi, wasu marasa kishi ne suke sayar da su ga ‘yan Najeriya.

“Har ila yau, lalata kayayyakin da wa’adinsu suka ƙare don son rai ga wasu ’yan kasuwa maza da mata, inda wasu masu kishi da tsoron Allah suka miƙa mana rahoton.”

Kayayyakin da aka lalata sun haɗa da abinci mara kyau, magunguna na jabu, na’urorin likitanci na jabu, ƙayatattun kayan kwalliya da sinadarai da wa’adinsu suka ƙare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Jigawa ta bayyana damuwa kan jinkirin shari’a wajen gurfanar da masu laifin rashawa, inda ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 479 da suka shafi cin hanci, amana da sauran laifuka makamanta a wannan shekarar ta 2025.

Shugaban Hukumar, Barista Salisu Abdul ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai kan nasarorin da hukumar ta samu da ƙalubalen da ta fuskanta a shekarar

Taron manema labaran wani ɓangare ne na shirye-shiryen hukumar na bikin Ranar Yaƙi da Cin Hanci ta Duniya.

Barista Salisu Abdul ya ƙara da cewa, cin hanci babban abin da ke janyo koma-baya ne ga Najeriya a fannoni daban-daban na rayuwar jama’a da tattalin arzikin ƙasa.

A cewarsa, babban burin hukumar wacce aka kafa a watan Fabrairun 2024 shi ne ƙarfafa yaƙi da cin hanci da rashawa a jihar, tare da inganta gaskiya, ɗabi’a, da amana a harkokin gwamnati da na kamfanoni masu zaman kansu, da al’amuran zamantakewa da tattalin arziki.

 

Shugaban ya ce, a wannan shekarar hukumar ta shirya horo ga manyan ma’aikatan gwamnati da jami’anta, tare da wayar da kan jama’a kan rawar da kowa ya kamata ya taka wajen yaƙi da cin hanci.

“Yayin da muke ci gaba da wayar da kai sosai, za mu ƙara haɗa kai da sauran hukumomin yaƙi da cin hanci, da hukumomin gwamnati da masu zaman kansu, da jama’a domin mu fi mai da hankali wajen dakile cin hanci fiye da magance shi bayan ya faru,” in ji shi.

Ya kuma ce, hukumar za ta rungumi fasahar zamani a ayyukanta don samun ingantaccen sakamako.

Barista Salisu Abdul ya bayyana cewa, daga cikin shari’o’in 479, guda 110 sun shafi cin hanci da damfarar kuɗi, yayin da 375 suka shafi rikicin kadarori, sabanin iyali, da ma’amalar kasuwanci da ta ci tura, inda aka warware shari’o’i 107 cikin sulhu.

Ya kara da cewa an dawo da fiye da Naira miliyan 385 da kadarorin da darajarsu ta kai daruruwan miliyoyi, aka kuma mika su ga masu su.

Sai dai ya nuna damuwa kan yadda alkalai ke tafiyar da shari’o’in a hankali, wanda ya bayyana a matsayin babban ƙalubale da ke kawo cikas ga yaƙi da cin hanci a jihar.

Shugaban Hukumar ya kuma nemi goyon bayan kafafen yaɗa labarai a yaƙin da ake yi da cin hanci, tare da yabawa Gwamna Umar Namadi bisa goyon bayan da yake bai wa hukumar na yin aiki bisa cikakken ‘yanci ba tare da tsoma baki ba.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato