Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
Published: 12th, December 2025 GMT
A nan za mu iya cewa, wannan zunzurutun kudaden da za su tara har Naira biliyan 19 a wata daya, ya zama wajibi alummar yankin su sauya, na dakile matsalar domin kuwa, ‘yan Nijeriya, sun gaji batun ana tara dimbin kudade, domin magance wata matsala a kasar, amma daga, a karkatar da su, zuwa wata sabga, ta da ban.
Kazalika, batun ba wai kawai na tara wadannan zunzurutun kudaden ba ne, amma babbar ahaure’yan ambayar a nan ita ce, shin wa zai tafiyar da wadanda kudaden ? kuma shin, takamai-mai, wacce daga cikin matsalar ta tsaron, za a tunkarar? ta yaya za a kashe kudaden tare da fayyace yadda aka kashe su?
Matukar gwamonin, ba su bayar da wata gamsasshiyar amsar wadannan tamaboyin ba, wannan Gidauniyar, za ta kasance a cikin shakku, wadda za ta kasance wata hanya ta arzurta ‘yan Kwangila da kuma wasu da za a dauko, a matsayin mutanen tuntba, inda su kuma alumomin da ya kamata, magance masu kalubalen, za su ci gaba kai Gawarwakin ‘yanuwansu, makabartu, suna bizne su, saboda ci gaba da hare-haren na ‘yan bindiga.
Bugu da kari, Gwamonin sun bukaci da a dakatar da hakar ma’adanai, har na tsawon watanni shida, duba da cewa, hakar na’adanan, ta haramtacciyar hanyar, ta kasance tamkar wata hanya, samun kudaden ga ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda.
Alumomin da ke a jihohin Zamfara, Kaduna da Neja, sun ci gaba da fuskantar ‘yan bindiga da kuma’yan ta’adda bakin haure, ke kutsawa cikin alumomin da ke a wadannan jihohin suna hana su, kwanciyar hankali, tare da gindaya masu haraji.
A yanzu, Gwamonin na son ganin an tsaftace fannin na hakar ma’adanai ta hayar bayar da lasisi.
A nan, za a iya cewa, dakatawar ta watanni shida, ba ta wadatar ba, domin har yanzu, wasu na ci gaba da gudanar da ayyukan, ta haramtacciyar hanya.
A saboda haka, ya zama wajibi Gwamonin, su bukaci Ma’aikatar Hakar Ma’adanai ta Tarayya da ta sanar da su, ainahin kamfanonin da suka mallaki lasisin hakar ma’adanai tare da kuma wadanda suke amfana da fannin.
Hakazalika, akwai bukatar jihohin su samu cikakkun bayanan sirri, kan ayyukan da a ke gudanarwa, ba hakar ma’adanai a jihohin su da alumomin da abin ya shafa, inda kuma alummar, na ‘yancin su fada ko har yanzu, ana ci gaba da gudanar da ayyukan a yankunan su.
Kazalika, gungiyay ta kuma goyi bayan kafa ‘yansanda na jihohi, inda shi kasansa, wannan batun ke da bukatar, a yi dogon nazari a kai.
A bisa tunaninsu, kirkiro da ‘yansandan na jihohi, ita ce, hanya daya tilo, za a iya magance kalubalen rashin tsaro
Abu daya da takardar sakamakon taron ba su ta tsalle shi ne, shin a ta yaya ne, yankin ya tsinci kasansa, a cikin wannan matsalar ta rashin tsaro.
Gwamonin su kuma mika ta’aziyyarsu ga shugaba Bola Tinubu da kuma kokarin da yake ci gaba da yi, na tabbatar da tsaro, amma sun gaza yin dubi ga batun cin hanci da rashawa da yin tunani kan yadda ‘yan bindiga da kuma’yan ta’adda, ke ci gaba da aikata ta’asarsu, a cikin alumomi ba.
A nan za mu iya cwa, batun ya fi karfin tara kudade da damar da kayan aiki, amma dole ne, Gwamnonin su fuskanci gaskiya, musamman kan gazawar iya shugabanci wadda ta bayar da damar samun matsalar ta rashin tsaro.
Ya zama wajibi, Gwamnonin su yi dubi kan yadda ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda ke watayawarsu a cikin alumma tare da kakkafa sansanoninsu su kuma kai hare-harensu, ba tare da a far masu ba.
Batun na tara Naira biliyan 228 a shekara, batu ne da ya wuce maganar fitar da sanarwa ga kafafen yada labarai, amma sakamko na gari, shi ne ake bukata.
Shin dalibai a jihar Zamfara, za su iya zuwa makarantunsu na Boko, ba tare da jin wani tsoro ba? Manoma a jihar Kaduna, za su iya zuwa su iya komawa ci gaba da noma gonaksnu ba tare da wata fargaba ba? Matafiya za su iya bin babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna ba tare da ‘yan bindiga sun kai masu hari ba?
Gwamnonin sun dauki matakai da dabaru na zuba kudade domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: hakar ma adanai yan bindiga da rashin tsaro yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
Tafarkin samun ci gaba mai karfi da inganci, da karuwar kuzarin kirkire-kirkire da ci gaba da fadada bude kofa, su ne suka hadu suka samar da wani sabon matsayi ga tattalin arzikin kasar Sin a taswirar tattalin arzikin duniya. Ci gaba mai inganci da fadada bude kofa, ba muhimman jigon ne dake ingiza tattalin arzikin Sin kadai ba, har da nuna yanayin sauyawar abubuwan dake haifar da ci gaba a duniya. Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ta kafar intanet, ya nuna yadda masu bayar da amsa daga fadin duniya suka yi imanin cewa, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba ta kowace fuska ba tare da tangarda ba, lamarin da ya samar da tabbaci ga tattalin arzikin duniya.
Karfin tattalin arzikin Sin ya dagora ne da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi da ke samun ci gaba cikin sauri, wadda ake ganin saurin ci gabanta ta hanyar kirkire-kirkire. Nazarin ya nuna cewa, kaso 93.6 na wadanda suka bayar da amsa, sun yi imanin cewa, kirkire-kirkire na taka muhimmiyar rawa wajen raya tattalin arziki mai inganci na Sin. Wasu kaso 96.6 kuma sun yi imanin cewa, kasar Sin na jagorantar manyan sauye-sauye a tsare-tsaren tafiyar da masana’antu da na tattalin arziki ta hanyar kirkire kirkiren kimiyya da fasaha.
A matsayinta na kasa ta biyu mafi yawan masu sayayya, kasar Sin ce ke da mutane masu matsakaicin kudin shiga mafi yawa a duniya, inda take da gagarumin karfin sayayya da na zuba jari. Nazarin ya nuna cewa, kaso 82.3 na masu bayar da amsu sun yi imanin cewa, kamfanonin kasashen waje za su iya amfani da fa’idojin da suke da shi wajen shiga kasuwar kasar Sin domin kara samun karfin takara a duniya. (FMM)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA