HausaTv:
2025-12-11@17:38:50 GMT

Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya

Published: 10th, March 2025 GMT

Bayanai da kungiyar dake sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar, sun ce rikicin baya-bayan nan tsakanin bangarorin da ke dauke da makamai da suka hada da kungiyar Hayat Tahrir al-Sham (HTC) da kungiyoyin dake da alaka da tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad, ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000 a cikin kwanaki biyu kacal.

Wannan tashin hankalin, ya fi shafar yankin yammacin Syria, wanda ya kara ta’azzara halin da ake ciki.

A baya dai kungiyar ta bayar da rahoton cewa, an kashe akalla mutane 237 da suka hada da 142 wadanda ba mayakan ba ne a yankin gabar ruwan kasar ta Syria, tun bayan fara kazamin fada a ranar Alhamis din da ta gabata.

Wadannan al’amura dai na nuni da karuwar tashe-tashen hankula, mafi muni da aka gani tun bayan faduwar gwamnatin da ta shude a watan Disambar da ya gabata.

Shugaban Syria Abu Mohammed al-Jolani ya yi kira da a samar da zaman lafiya da hadin kan kasa bayan tashe tashen hankula a kasar a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa abubuwan da ke faruwa na daga cikin kalubalen da ake iya fuskanta.

Wannan sabon lamari na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun HTC suka kara kaimi wajen murkushe ragowar tsoffin sojojin Syria a lardunan Latakia, Tartus da Hama.

Ana gwabza fada ne a yankin gabar tekun arewa maso yammacin kasar, inda galibin al’ummar kasar ke da ‘yan tsiraru ‘yan Alawiyya, wanda shi ma tsohon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya fito.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky

Shugaban mabiya Shi’a a Najeriya, Sheikh Ibraheem El-Zakzaky, ya ce zai yi hisabi da tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a gaban Allah kan abin da ya faru a Zariya a 2015.

Rikicin ya fara ne bayan da mambobin IMN sun tare wa tsohon Hafsan Soji, Tukur Buratai, hanya.

Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025 Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa

Lamarin fara a matsayin ƙaramin rikici daga baya ya rikiɗe zuwa babban al’amari, lamarin da ya sanya sojoji buɗe wa mabiyan wuta.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da kwamitin bincike na jihar, sun bayyana cewa an kashe tare binne ɗaruruwan mambobin IMN a asirce bayan faruwar lamarin.

Daga baya an kama Zakzaky da matarsa, an tsare su har zuwa 2021, kafin daga baya kotu ta wanke su.

Bayan cikar lamarin da shekara 10, Zakzaky ya ce gwamnati ta kasa ɗaukar alhakin abin da ya faru.

Ya ce: “Babu abin da aka yi. Ba su yadda cewa wani abu ya faru ba, duk da cewa kwamitin bincike ya miƙa rahotonsa tun 2016.”

Zakzaky, ya kuma zargi gwamnatin yanzu da yin shiru a kan lamarin, duk da alƙawarin da ta yi na duba rahoton da kuma biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ya ce: “Sun tabbatar mana cewa za su magance batun, amma tun daga lokacin shiru kake ji.”

Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a hannun Allah, kuma zai masa hisabi da shi ranar gobe ƙiyama.

Zakzaky ya ce: “Game da Buhari, za mu gana a Ranar Alƙiyama. Lissafin Buhari ya ƙare.”

Ya ƙara da cewa harin bai yi nasarar daƙile IMN ba, sai ma ƙara ɗaukaka sunan ƙungiyar inda ta yi fice a duniya.

Zakzaky, ya ce sun kai ƙarar lamarin kotun ƙasa da ƙasa, sannan ƙofarsu a buɗe ta ke domin tattaunawa da gwamnati.

Ya ce: “Ko ba sa son ganinmu, za su gan mu. Ko ba sa son jinmu, za su ji mu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Kungiyar AU Ta yi Tir Da Harin Da RSF  Takai A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80