Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya
Published: 10th, March 2025 GMT
Bayanai da kungiyar dake sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar, sun ce rikicin baya-bayan nan tsakanin bangarorin da ke dauke da makamai da suka hada da kungiyar Hayat Tahrir al-Sham (HTC) da kungiyoyin dake da alaka da tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad, ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000 a cikin kwanaki biyu kacal.
Wannan tashin hankalin, ya fi shafar yankin yammacin Syria, wanda ya kara ta’azzara halin da ake ciki.
A baya dai kungiyar ta bayar da rahoton cewa, an kashe akalla mutane 237 da suka hada da 142 wadanda ba mayakan ba ne a yankin gabar ruwan kasar ta Syria, tun bayan fara kazamin fada a ranar Alhamis din da ta gabata.
Wadannan al’amura dai na nuni da karuwar tashe-tashen hankula, mafi muni da aka gani tun bayan faduwar gwamnatin da ta shude a watan Disambar da ya gabata.
Shugaban Syria Abu Mohammed al-Jolani ya yi kira da a samar da zaman lafiya da hadin kan kasa bayan tashe tashen hankula a kasar a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa abubuwan da ke faruwa na daga cikin kalubalen da ake iya fuskanta.
Wannan sabon lamari na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun HTC suka kara kaimi wajen murkushe ragowar tsoffin sojojin Syria a lardunan Latakia, Tartus da Hama.
Ana gwabza fada ne a yankin gabar tekun arewa maso yammacin kasar, inda galibin al’ummar kasar ke da ‘yan tsiraru ‘yan Alawiyya, wanda shi ma tsohon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya fito.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
Sojoji a kasar Jamhuriyar Benin sun kifar da gwamnati a wani juyin mulki da suka sanar a ranar Lahadi.
Sojojin sun bayyana ne a gidan talabijin na kasar inda suka sanar da tsige Shugaban Kasa Patrice Talon da kuma rushe duk hukumomin kasar.
Dakarun, karkashin jagorancin Laftanar Kanar Pascal Tigiri, sun rufe iyakokin kasar da rushe jam’iyyun siyasa.
Zuwa lokacin kammala wannan labarin babu labarin halin da Shugaba Talon wanda ke kan karagar mulkin tun a 2016 yake ciki.
Amma ministan harkokin kasar, Olusegun Ajadi Bakari, ya ce an samu yunkurin kifar da gwamnati, amma ana neman shawo kan lamarin.