Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya
Published: 10th, March 2025 GMT
Bayanai da kungiyar dake sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar, sun ce rikicin baya-bayan nan tsakanin bangarorin da ke dauke da makamai da suka hada da kungiyar Hayat Tahrir al-Sham (HTC) da kungiyoyin dake da alaka da tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad, ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000 a cikin kwanaki biyu kacal.
Wannan tashin hankalin, ya fi shafar yankin yammacin Syria, wanda ya kara ta’azzara halin da ake ciki.
A baya dai kungiyar ta bayar da rahoton cewa, an kashe akalla mutane 237 da suka hada da 142 wadanda ba mayakan ba ne a yankin gabar ruwan kasar ta Syria, tun bayan fara kazamin fada a ranar Alhamis din da ta gabata.
Wadannan al’amura dai na nuni da karuwar tashe-tashen hankula, mafi muni da aka gani tun bayan faduwar gwamnatin da ta shude a watan Disambar da ya gabata.
Shugaban Syria Abu Mohammed al-Jolani ya yi kira da a samar da zaman lafiya da hadin kan kasa bayan tashe tashen hankula a kasar a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa abubuwan da ke faruwa na daga cikin kalubalen da ake iya fuskanta.
Wannan sabon lamari na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun HTC suka kara kaimi wajen murkushe ragowar tsoffin sojojin Syria a lardunan Latakia, Tartus da Hama.
Ana gwabza fada ne a yankin gabar tekun arewa maso yammacin kasar, inda galibin al’ummar kasar ke da ‘yan tsiraru ‘yan Alawiyya, wanda shi ma tsohon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya fito.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
Jam’iyyar (APC) a ƙarƙashin kungiyar Wamban Shinkafi ta jihar Zamfara, ta bayyana goyon bayanta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin ɗan takarar shugabancin ƙasa guda ɗaya na jam’iyyar a zaben 2027.
Wannan sanarwar ta fito ne daga wanda ya kafa kungiyar kuma jigo a jam’iyyar APC a Zamfara, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi, yayin taron masu ruwa da tsaki na kungiyar da aka gudanar a birnin Gusau, babban birnin jihar.
A cewar Shinkafi, amincewar da aka bayar ta biyo bayan wani motsi da Yushau Mada, kwamandan kungiyar, ya gabatar, wanda kuma Asma’u Gusau, shugabar mata ta amince da shi ta biyu.
Dakta Shinkafi ya ce, gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu na tafiya kan turbar sauyi, ci gaba da gina ƙasa, tare da tabbatar da cewa yana da cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar mai mulki. Ya kuma yi alkawarin ba da gudunmuwarsa wajen tabbatar da nasarar APC a dukkan matakai.
Ya bayyana cewa jam’iyyar APC a Zamfara ta kasance ɗaya mai haɗin kai, inda ya gargadi mambobi su guji ayyukan da za su cutar da jam’iyyar kafin da lokacin zaɓe.
Ya sake jaddada kudirinsa na kare ka’idojin dimokuraɗiyya da kyakkyawan shugabanci, yana mai cewa jagorancin Shugaba Tinubu ya kawo ci gaba mai ma’ana da gyare-gyare a fannoni daban-daban na ƙasar.
Shinkafi ya kuma yi alkawarin ci gaba da goyon baya ga shugabancin jam’iyyar APC a matakin ƙasa da jiha ƙarƙashin Tukur Danfulani, tare da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin mambobi.
Wannan amincewar da kungiyar Wamban Shinkafi Democratic Front ta bayar ga Shugaba Tinubu, na zuwa ne kwanaki goma bayan sashen jam’iyyar APC na Jihar Zamfara ya yi irin wannan sanarwa.
AMINU DALHATU/Gusau