HausaTv:
2025-03-28@08:49:16 GMT

Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya

Published: 10th, March 2025 GMT

Bayanai da kungiyar dake sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar, sun ce rikicin baya-bayan nan tsakanin bangarorin da ke dauke da makamai da suka hada da kungiyar Hayat Tahrir al-Sham (HTC) da kungiyoyin dake da alaka da tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad, ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000 a cikin kwanaki biyu kacal.

Wannan tashin hankalin, ya fi shafar yankin yammacin Syria, wanda ya kara ta’azzara halin da ake ciki.

A baya dai kungiyar ta bayar da rahoton cewa, an kashe akalla mutane 237 da suka hada da 142 wadanda ba mayakan ba ne a yankin gabar ruwan kasar ta Syria, tun bayan fara kazamin fada a ranar Alhamis din da ta gabata.

Wadannan al’amura dai na nuni da karuwar tashe-tashen hankula, mafi muni da aka gani tun bayan faduwar gwamnatin da ta shude a watan Disambar da ya gabata.

Shugaban Syria Abu Mohammed al-Jolani ya yi kira da a samar da zaman lafiya da hadin kan kasa bayan tashe tashen hankula a kasar a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa abubuwan da ke faruwa na daga cikin kalubalen da ake iya fuskanta.

Wannan sabon lamari na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun HTC suka kara kaimi wajen murkushe ragowar tsoffin sojojin Syria a lardunan Latakia, Tartus da Hama.

Ana gwabza fada ne a yankin gabar tekun arewa maso yammacin kasar, inda galibin al’ummar kasar ke da ‘yan tsiraru ‘yan Alawiyya, wanda shi ma tsohon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya fito.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu

Mai magana da yawun ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya bayyana cewa, kasar tana matukar adawa da yunkurin Amurka na kara yawan dozin-dozin na kamfanoninta a cikin jerin kamfanonin da aka takaita fitar da kayayyakinsu zuwa kasashen waje.

Jami’in, wanda ya bayyana haka a ranar Larabar nan, ya ce, matakin na Amurka ba komai ba ne illa murkushewa da kuma takura wa wasu kamfanonin kasashen ketare, tare da danne hakkokin sauran kasashen duniya na samun ci gaba. Yana mai cewa, hakan zai yi matukar cutar da kamfanonin tare da kawo cikas ga kwanciyar hankali da samun wadataccen tsarin samar da kayayyaki a duniya.

Ya kara da cewa, matakin zai yi kafar ungulu ga kokarin warware matsaloli ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa, kuma kasar Sin tana kira ga Amurka da ta gaggauta kawo karshen kurakuran da take tafkawa, kana ya ce, kasar za ta dauki matakan da suka dace don kiyaye hakkoki da muradun kamfanonin Sinawa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  •  Kasashen Iran Da Katar Sun Jaddada Muhimmancin Shigar Da Dukkanin Bangarorin  Al’ummar Kasar A Cikin  Sha’anin Kasar
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta
  • Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi