HausaTv:
2025-12-13@18:28:06 GMT

Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya

Published: 10th, March 2025 GMT

Bayanai da kungiyar dake sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar, sun ce rikicin baya-bayan nan tsakanin bangarorin da ke dauke da makamai da suka hada da kungiyar Hayat Tahrir al-Sham (HTC) da kungiyoyin dake da alaka da tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad, ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000 a cikin kwanaki biyu kacal.

Wannan tashin hankalin, ya fi shafar yankin yammacin Syria, wanda ya kara ta’azzara halin da ake ciki.

A baya dai kungiyar ta bayar da rahoton cewa, an kashe akalla mutane 237 da suka hada da 142 wadanda ba mayakan ba ne a yankin gabar ruwan kasar ta Syria, tun bayan fara kazamin fada a ranar Alhamis din da ta gabata.

Wadannan al’amura dai na nuni da karuwar tashe-tashen hankula, mafi muni da aka gani tun bayan faduwar gwamnatin da ta shude a watan Disambar da ya gabata.

Shugaban Syria Abu Mohammed al-Jolani ya yi kira da a samar da zaman lafiya da hadin kan kasa bayan tashe tashen hankula a kasar a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa abubuwan da ke faruwa na daga cikin kalubalen da ake iya fuskanta.

Wannan sabon lamari na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun HTC suka kara kaimi wajen murkushe ragowar tsoffin sojojin Syria a lardunan Latakia, Tartus da Hama.

Ana gwabza fada ne a yankin gabar tekun arewa maso yammacin kasar, inda galibin al’ummar kasar ke da ‘yan tsiraru ‘yan Alawiyya, wanda shi ma tsohon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya fito.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi

Adai dai lokacin da ke ta tattaunawa tsakanin Amurka da Indiya kan harkokin kasuwancin , sai ga shi a makon da ya wuce New Delhi ta karbi bakunci daya daga cikin manyan shuwagabannin dake kalubalantar gwamnatin Amurka akan nuna fin karfin a duniya.

Shugaban kasar Rasha viladmir Putin ya kwashe kwanaki biyu a indiya  a wata ziyarar aiki da ya kai, kuma wannan yana zuwa ne adaidai lokacin da indiya ke fuskantar harajin da Amurka ta sanya mata na kashi 25 cikin 100  saboda ci gaba da siyan mai a hannun kasar Rasha , lamarin da ya kawo tarnaki a alakar dake tsakanin Delhi da kuma Washinton.

Bugu da kari Amurka ta sanar da takunkumin ne a ranar 23 ga watan oktoba akan manyan kamfanonin mai na kasar Rasha da hakan ha haifar da barazana ga kasar indiya dake neman shigo da man fetur mai sauki daga rasha, sai dai rahotanni sun nuna cewa har yanzu dai kasar indiya itace babbar mai sayan manfetur din kasar Rasha.

Tun a shekara ta 1960 Mosko da New Delhi ke da kyakkayawar dangantaka ta kud da kud da ya hada da kasuwancin , hadin guiwar Soja , kimiyya ,makamashi da kuma sararin samaniya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na  Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu December 13, 2025 Ali Nuhu, ya yaba wa Iran kan haskaka Musulinci ta hanyar fina-finai December 13, 2025 MDD ta amince da kudurin da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza    December 13, 2025 Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba December 13, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan December 12, 2025 Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe