Aminiya:
2025-12-12@22:41:58 GMT

2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe

Published: 12th, December 2025 GMT

Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanninta a Jihar Gombe, inda ta jaddada muhimmancin haɗin kai da farfado da jam’iyyar tun daga matakin ƙananan hukumomi zuwa jiha gabanin zaɓen 2027.

Taron ya halarta bayan zuwan wakilai daga dukkanin ƙananan hukumomin jihar.

Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno

Mambobin jam’iyyar sun yaba da yadda komai ya gudana cikin lumana da tsari, abin da suka ce alama ce ta daidaito a cikin jam’iyyar.

Elder Ambrose Ismail Mairungu ne, ya zama sabon shugaban NNPP na jihar, yayin da Yakubu Adamu Tela, ya zama mataimakinsa.

Abdullahi Ali Mohammed, ya samu kujerar sakataren jiha, sannan Hon. Amatiga Yila Naboth (ACG) ya zama sakataren yaɗa labarai.

Sauran da aka zaɓa sun haɗa da Musa Mohammed Gargajiga (Jagoran Matasa), Hajiya Hauwa Mohammed (Shugabar Mata), da Kabiru Mohammed Puma (Sakataren Tsara Ayyuka).

A jawabin da ya gabatar bayan rantsar da su, Mairungu, ya gode wa ’yan jam’iyyar bisa amincewa da suka nuna gare shi, inda ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su yi aiki da adalci da tsari, tare da haɗa kowa domin ci gaban jam’iyyar.

Ya ce za su mayar da hankali wajen gina jam’iyyar daga matakin unguwanni, ƙara yawan mambobi, da ƙarfafa shiga matasa da mata a harkokin jam’iyya.

Wasu masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba da sabbin shugabannin, inda suka ce suna da damar gyara jam’iyyar kafin tunkarar babban zaɓe.

Haka kuma, sun yi godiya ga Jagoran NNPP na ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso, bisa tallafi da goyon bayan da ya bai wa taron.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwaso Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.

Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar.

Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa.

Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis.

An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60.

Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba tsammani yayin da yake gudanar da ayyukan ofis, lamarin da ya sa dogarai da ma’aikatansa suka yi gaggawar taimaka masa.

Wasu majiyoyi da ke kusa da marigayin sun nuna cewa mutuwarsa na iya zama sakamakon bugun zuciya.

Lamarin ya haifar da ɗan tashin hankali a gidan gwamnati da kuma fadin Yenagoa, inda mazauna garin suka nuna damuwa game da mutumin da suke kira da “Mataimakin Gwamna Mai Aikin Dare.”

Sun ce sau da yawa yana yin aiki har dare ba tare da hutu ba.

A lokacin da ake rubuta wannan rahoto da yammacin jiya, gwamnatin Jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance a kan lamarin.

Kazalika, da mai taimaka wa mataimakin gwamnan kan yaɗa labarai, Doubra Atazi, da kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ebiuwou Koku-Obiyai, sun ƙi yin bayani lokacin da aka tuntube su.

Sai dai a cikin sanarwarta, PDP ta bayyana kaduwa da alhini kan rasuwar mataimakin gwamnan, tana bayyana shi a matsayin “amintaccen ɗan jam’iyya kuma mai gaskiya.”

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar PDP ta kadu matuƙa da labarin rasuwar Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa kuma ɗan jam’iyya mai aminci, Mai Girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo, wanda rahotanni suka ce ya faɗi ya rasu a yau.

“Wannan labari mai tayar da hankali ya jefa Kwamitin Zartarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, SAN, da kuma dukkan mambobin jam’iyyarmu mai girma, musamman mambobinmu masu aminci a Jihar Bayelsa, cikin baƙin ciki mai yawa.

“Tun yana raye, Sanata Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa mai gaskiya da daidaito wanda ya yi siyasa bisa ƙa’ida. Mutum ne da ya yi tsayin daka, jagora ne wanda rayuwarsa ta ta’allaka da imani, gaskiya da ƙarfin hali. Ya tsaya tsayin daka kan waɗannan dabi’u har zuwa ƙarshe.

“Muna cikin baƙin ciki matuƙa da rasuwar wannan jarumin siyasa mai gaskiya, kuma muna roƙon Allah ya ba shi hutu na har abada. Muna mika ta’aziyyarmu ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan wannan babban rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
  • Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago