Kasar Qatar ta bukaci hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta bayyana cewa, Doha ta bukaci hukumar ta (IAEA) da ta sanya damar gudanar da bincike da ka’ida daga hukumar ta MDD, kan dukkanin cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

Jakadan dindindin na Qatar a Majalisar Dinkin Duniya, Jasem Yacoub al-Hammadi, ya bukaci gwamnatin Isra’ila da ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta ce “Al-Hammadi ya jaddada bukatar kasashen duniya da cibiyoyinta su tabbatar da alkawurran da suka dauka a karkashin kudurorin kwamitin sulhu na MDD, da babban taron MDD, da hukumar IAEA da kuma taron bitar NPT na shekarar 1995, wanda daga bisani ya bukaci Isra’ila da ta mika dukkanin cibiyoyinta na nukiliya ga tsarin kiyaye zaman lafiya na IAEA.”

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce jakadan Qatar ya yi kira da a kara kaimi ga kokarin da kasashen duniya ke yi na shigar da Isra’ila cikin tsarin NPT.

Sanarwar ta kara da cewa, dukkan kasashen Gabas ta Tsakiya, in ban da gwamnatin Isra’ila, suna cikin yarjejeniyar NPT, ta hana yadfuwar makamman nukiliya.

An dai bayyana cewa Isra’ila tana da manyan makaman nukiliya tsakanin 200 zuwa 400 a ma’ajiyar makamanta, wanda hakan ya sa ta kasance kasa daya tilo mai mallakar makaman nukiliya a yammacin Asiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Shugaban Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) da kwamishinoni biyu na hukumar, tare da sabbin manyan  sakatarori guda biyar da aka nada a gwamnatin tarayya.

Daga nan ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Bayan karanta takardar tarihin rayuwarsu, manyan sakatarorin biyar Abdulkarim Ibrahim, Dr John Ezeamama, Dr Abdul-Sule Garba, Dr Isiaku Mohammed da Dr Ukaire Chigbowu, sun dauki rantsuwar kama aiki, sannan suka sanya hannu a kundin rantsuwa.

An kuma rantsar da Dr Aminu Yusuf, wanda shugaban kasa ya nada a matsayin Shugaban NPC a ranar 9 ga Oktoba, da kwamishinoni biyu ciki har da Dr Tonga Betara daga Jihar.

NPC ita ce hukuma da ke da alhakin gudanar da kidayar jama’a a hukumance, yin rajistar haihuwa da mace-mace, da tattara bayanan kimiyyar jama’a domin tsare-tsare.

Majalisar ta yi shiru na minti guda domin tunawa da tsohuwar Ministar Harkokin Waje, Ambasada Joy Ogwu, wadda ta rasu a ranar Litinin, 13 ga watan Oktoban 2025 tana da shekaru 79.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe
  • MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
  • Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin  Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Yankin Gaza
  • Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta  Kama Olmert Da Livni
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  •  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota
  • Kungiyar Hamasa Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a