Kasar Qatar ta bukaci hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta bayyana cewa, Doha ta bukaci hukumar ta (IAEA) da ta sanya damar gudanar da bincike da ka’ida daga hukumar ta MDD, kan dukkanin cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

Jakadan dindindin na Qatar a Majalisar Dinkin Duniya, Jasem Yacoub al-Hammadi, ya bukaci gwamnatin Isra’ila da ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta ce “Al-Hammadi ya jaddada bukatar kasashen duniya da cibiyoyinta su tabbatar da alkawurran da suka dauka a karkashin kudurorin kwamitin sulhu na MDD, da babban taron MDD, da hukumar IAEA da kuma taron bitar NPT na shekarar 1995, wanda daga bisani ya bukaci Isra’ila da ta mika dukkanin cibiyoyinta na nukiliya ga tsarin kiyaye zaman lafiya na IAEA.”

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce jakadan Qatar ya yi kira da a kara kaimi ga kokarin da kasashen duniya ke yi na shigar da Isra’ila cikin tsarin NPT.

Sanarwar ta kara da cewa, dukkan kasashen Gabas ta Tsakiya, in ban da gwamnatin Isra’ila, suna cikin yarjejeniyar NPT, ta hana yadfuwar makamman nukiliya.

An dai bayyana cewa Isra’ila tana da manyan makaman nukiliya tsakanin 200 zuwa 400 a ma’ajiyar makamanta, wanda hakan ya sa ta kasance kasa daya tilo mai mallakar makaman nukiliya a yammacin Asiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya taya al’ummar Iran murnar zagayowar lokacin bukukuwan Nowruz na sabuwar shekarar hijira shamsiyya da ake amfani da itya a hukumance a kasar Iran.

Ayatullah Khamenei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya aikewa al’ummar kasar ta gidan telebijin na murnar shiga sabuwar shekara ta Farisa a yammacin wannan Alhamis.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada bukatar gwamnati da al’ummar kasar su ci gaba da zuba jari don karfafa azamarsu wajen tunkarar takunkumai na zalunci da masu girman kai na duniya suka kakaba ma kasar.

Ayatullah Khamenei ya jaddada cewa samar da kayayyaki na samun bunkasuwa ne idan aka ba da tallafin jari mai karfi.

Jagoran ya kuma yi Allah wadai da sabbin hare-haren da Isra’ila da take kaiwa Gaza, inda ya yi kira ga kasashen duniya baki daya da su nuna adawa da laifukan da Amurka da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.

A yayin da ya koma kan batun kasar Yemen, Ayatullah Khamenei ya bayyana hare-haren da Amurka ke kai wa al’ummar kasar Yemen a matsayin wani laifi da ya zama wajibi a dakatar da shi.

Ya bayyana fatan alheri, nasara, da alheri ga al’ummar musulmi a cikin sabuwar shekara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • Hare-Haren Isra’ila Cikin Dare Sun Hallaka Mutum Aƙalla 50 A Gaza
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
  • Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Samar Da Rijiyoyin Burtsatse A Karamar Hukumar Ringim