Qatar ta yi kira ga hukumar IAEA da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila
Published: 10th, March 2025 GMT
Kasar Qatar ta bukaci hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta bayyana cewa, Doha ta bukaci hukumar ta (IAEA) da ta sanya damar gudanar da bincike da ka’ida daga hukumar ta MDD, kan dukkanin cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.
Jakadan dindindin na Qatar a Majalisar Dinkin Duniya, Jasem Yacoub al-Hammadi, ya bukaci gwamnatin Isra’ila da ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta ce “Al-Hammadi ya jaddada bukatar kasashen duniya da cibiyoyinta su tabbatar da alkawurran da suka dauka a karkashin kudurorin kwamitin sulhu na MDD, da babban taron MDD, da hukumar IAEA da kuma taron bitar NPT na shekarar 1995, wanda daga bisani ya bukaci Isra’ila da ta mika dukkanin cibiyoyinta na nukiliya ga tsarin kiyaye zaman lafiya na IAEA.”
Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce jakadan Qatar ya yi kira da a kara kaimi ga kokarin da kasashen duniya ke yi na shigar da Isra’ila cikin tsarin NPT.
Sanarwar ta kara da cewa, dukkan kasashen Gabas ta Tsakiya, in ban da gwamnatin Isra’ila, suna cikin yarjejeniyar NPT, ta hana yadfuwar makamman nukiliya.
An dai bayyana cewa Isra’ila tana da manyan makaman nukiliya tsakanin 200 zuwa 400 a ma’ajiyar makamanta, wanda hakan ya sa ta kasance kasa daya tilo mai mallakar makaman nukiliya a yammacin Asiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyoyin kare hakkin bil adama na yankin falasdinu sun yi gargadi game da makircin da isra’ila ke kullawa na kashe Marwan bargusu daya daga cikin shuwagabanin falasdinawa a inda take tsare da shi a gidan yari, samakamon gana masa azaba da aka yi .
Babban darektan kungiyar pps Amad Najjar yayi kira ga majalisar dinkin duniya da sauran kasashen duniya da su dauki matakin gaggawa tun kafin lokaci ya kure game da abin da israila ke kokarin yi kan marwan barghusi da hakan ya sabama dokokin kasa da kasa.
Haka zalika yayi kira ga majalisar dinkin duniya da ta ziyarci inda ake tsare da barghusi domin ganin irin halin da yake ciki, kuma su matsa lamba na ganin an sake shi domin tseratar da rayuwasa .
Marwan Barghusu dan shakaru 66 da haihuwa da ake ganinsa a matsayin magajin shugaban gwamnatin falasdinu Mahmud Abbas yana tsare a gidan yari tun shekara ta 2002 an yake masa hukumci daurin rai da rai saboda zargin da ake masa da hannu wajen yunkurin intifada ta biyu da falasdinawa suka yi da aka fara shekara ta 2000.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Limamin Tehran: Idan Abokan Gaba Su Ka Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci