Qatar ta yi kira ga hukumar IAEA da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila
Published: 10th, March 2025 GMT
Kasar Qatar ta bukaci hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta bayyana cewa, Doha ta bukaci hukumar ta (IAEA) da ta sanya damar gudanar da bincike da ka’ida daga hukumar ta MDD, kan dukkanin cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.
Jakadan dindindin na Qatar a Majalisar Dinkin Duniya, Jasem Yacoub al-Hammadi, ya bukaci gwamnatin Isra’ila da ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta ce “Al-Hammadi ya jaddada bukatar kasashen duniya da cibiyoyinta su tabbatar da alkawurran da suka dauka a karkashin kudurorin kwamitin sulhu na MDD, da babban taron MDD, da hukumar IAEA da kuma taron bitar NPT na shekarar 1995, wanda daga bisani ya bukaci Isra’ila da ta mika dukkanin cibiyoyinta na nukiliya ga tsarin kiyaye zaman lafiya na IAEA.”
Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce jakadan Qatar ya yi kira da a kara kaimi ga kokarin da kasashen duniya ke yi na shigar da Isra’ila cikin tsarin NPT.
Sanarwar ta kara da cewa, dukkan kasashen Gabas ta Tsakiya, in ban da gwamnatin Isra’ila, suna cikin yarjejeniyar NPT, ta hana yadfuwar makamman nukiliya.
An dai bayyana cewa Isra’ila tana da manyan makaman nukiliya tsakanin 200 zuwa 400 a ma’ajiyar makamanta, wanda hakan ya sa ta kasance kasa daya tilo mai mallakar makaman nukiliya a yammacin Asiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
MDD ta amince da wani kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza
Majalisar Dinkin Duniya ta amince da wani daftarin kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agajin jin kai ba tare da wani sharadi ba zuwa Zirin Gaza.
Kudurin da aka zartar a ranar Juma’a, ya yi kira ga Isra’ila da ta kare cibiyoyin Majalisar Dinkin Duniya tare da bin dokokin kasa da kasa.
An gabatar da wannan matakin ne a matsayin martani ga ra’ayin da Kotun Duniya ta ICJ, ta bayar ga Isra’ila.
Yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a tsakanin kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da Isra’ila, wacce ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba, 2025, ta wajabta wa Isra’ila bude iyakoki domin ba da damar shigar da abinci, mai, da kayayyakin jin kai ba tare da wani sharadi ba zuwa zirin na Gaza.
Duk da haka Isra’ila ta yi watsi da wadannan alkawuran, inda ta bada damar jigilar kayaki kaɗan zuwa yankin da yakin shekaru biyu ya daidaita.
Tun daga watan Oktoba na 2023, sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa kusan 70,400, yawancinsu mata da yara, tare da raunata wasu 171,000.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba December 13, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan December 12, 2025 Birtaniya Ta yi Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci