Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu
Published: 27th, August 2025 GMT
A hakika, kwarewar kasar Sin a fannin inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa, tana da muhimmiyar ma’ana ga kasashen Afirka wajen fid da kansu daga kangin talauci da kuma tabbatar da hakkin dan Adam. A game da hakan, Prof. Melha Rout Biel, shehun malami a cibiyar nazarin tsare-tsare da manufofi ta kasar Sudan ta Kudu ya yi nuni da cewa, “Kasashen Afirka da Sin dukkansu sun taba fuskantar koma baya sakamakon katsalandan da wasu kasashen suka yi musu.
Har kullum, kasar Sin na dukufa a kan “inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa”, ta kuma gabatar da shawarar raya kasashen duniya, don “kar a bar wata kasa a baya”, kuma ta hanyar inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a wannan fannin tare da cimma kyawawan nasarori. Misali kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararru na kasashen Afirka, don inganta kwarewar kasashen wajen tabbatar da ci gabansu. A kwanan nan, layin dogon Mombasa zuwa Nairobi da kamfanin kasar Sin ya gina ya cika kwanaki 3000 da fara aiki, wanda ya rage kudaden jigilar kayayyaki kimanin kaso 40% ga al’ummar wurin, tare da samar musu guraben aikin yi dubu 74, kuma hakan ya tabbatar da hakkin ci gaban al’ummar kasar. Har wa yau, Kasar Sin ta kuma yi gine-ginen ababen samar da makamashi mai tsabta sama da 100 a Afirka, ciki har da tashar samar da lantarki daga karfin ruwa ta Zungeru, wadanda suka samar da karfi ga kasashen Afirka wajen tabbatar da dauwamammen ci gabansu.
Duk da haka, kasashen yamma sun sha yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin makami wajen tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe masu tasowa. A Afirka, kasashen yamma su kan bayar da gudummawar tattalin arziki bisa gindaya sharuda kan batutuwan hakkin dan Adam, sai dai irin katsalandan da suke yi ta fakewa da batun hakkin dan Adam kan haifar da munanan illoli ga kare hakkin dan Adam a kasashen Afirka. Don haka, a matsayar da aka cimma a gun taron, Sin da kasashen Afirka sun jaddada cewa, suna goyon bayan kasa da kasa su zabi hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki, kuma suna masu adawa da siyasantar da batun hakkin dan Adam ko kuma mai da shi tamkar makami.
A yayin da malama Abiola Issah ke samun horo a kasar Sin, ta taba shiga jirgin kasa mai saurin tafiya na kasar. Ta ce ba ta taba ganin jirgi mai sauri haka ba, kuma fatan ta shi ne, wata rana Nijeriya ma ta samu irin jirgin, kuma ta zama matukiya ta farko ta irin wannan jirgin kasa a gida Nijeriya. A ganina, yayin da ake aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da tabbatar da sakamakon da aka cimma a gun taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, burinta zai cika nan bada jimawa ba, kuma Sin da kasashen Afirka za su tabbatar da ci gabansu na bai daya bisa hadin gwiwarsu, a yayin da za su dada kyautata rayuwar al’ummunsu da kuma kara inganta hakkin dan Adam bisa ci gaban kasashensu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
Kasashen duniya na ci gaba da yin tir da sabon farmakin soji da Isra’ila ta kaddamar kan Gaza.
Kasashen Biritaniya, Faransa, Italiya, Masar, Jordan, Qatar, Spain, duk sun yi tir da farmakin kan Gaza suna masu cewa zai kara dagula halin kunci da ake ciki.
Kungiyar tarayyar Turai, ta bakin Jami’ar kula da harkokin wajen ta, Kaja Kalas, ta yi kira da a sanyawa Isra’ila takunkumi domin matsa wa gwamnatin lamba ta kawo karshen hare-haren da take kaiwa Gaza, tana mai gargadin cewa al’amuran jin kai na kara ta’azzara.
“Hare-haren da Isra’ila ta kai a Gaza zasu haifar da mummunan sakamako game da halin da ake ciki da karin hasarar rayuka, da barna & hijira na jama’a,” in ji Kalas a kan X.
A jiya ne Sojojin Isra’ila suka kaddamar da sabon farmakin ta kasa mai manufar mamaye birnin Gaza bayan shafe makwanni ana kai hare-haren bama-bamai ba kakkautawa ba a kan wasu manyan gine-gine domin tilastawa Falasdinawa kauracewa gidajensu.
Farmakin ya zo ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu a kusa da masallacin Al Aqsa da ke gabashin birnin Kudus da aka mamaye.
Tun da farko dai, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan yankunan Falasdinawa da ke mamaye, Francesca Albanese ta yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa birnin Gaza, tana mai cewa wani bangare ne na shirin Isra’ila na shafe Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci