’Yan bindiga sun kashe mutane sun sace masu ibada a coci a Kogi
Published: 15th, December 2025 GMT
Aƙalla mutane huɗu ne suka mutu yayin da ’yan bindiga suka sace mutane da ba a tantance adadinsu ba a wani coci da wasu wurare a Jihar Kogi.
’Yan bindiga sun kashe mutum guda tare da sace wasu da ba a tabbatar da iya yawansu ba a yayin da ake tsaka da ibada coci a ranar Lahadi a Jihar Kogi.
A safiyar ranar Lahadi ne maharan suka far wa masu ibadar a Cocin ECEWA da ke yankin Àaaaz-Kiri da ke Ƙaramar Hukumar Kabba/Bunu, bayan ’yan ta’adsan sun shiga yankin suna harbe-harbe, kai tsaye suka nufi cocin, a lokacin ana tsaka da ibada.
Wani mazaunin ƙauyen Àaaaz-Kiri da ke kusa da inda aka kai harin ya shaida wa wakilinmu da daddare cewa “Ba za a iya cewa ga haƙiƙnin yawan mutanen da aka kashe ba, amma ana tsaka da ibada da safe suka kawo harin.
“Zuwa yanzu dai an tabbatar da mutuwar mutum ɗaya, iyalai da dama kuma sun ba da rahoton rashin ganin ’yan uwansu bayan da’yan bindigar suka tafe ida mutane.
ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura An kai hare-hare a lokaci gudaA wani lamarin kuma ’yan bindiga sun kashe mutane uku a wani hari da ɓata-gari suka kai har a ƙauyukan Illa da Okeagi da ke Ƙaramar Hukumar Mopa Muro.
Rahotanni sun ce maharan sun kai farmakin ne a lokaci guda, inda suka shafe fiye da awa guda sun cin karensu babu babbaka, kafin a iya isar da saƙon neman ɗauki ga jami’an tsaro.
Mazauna sun ce da farko sai da ’yan bindigar suka kai hari a yankin Jamroro inda suna kashe mutum biyu tare da jikkata wasu uku.
Wasu maharan kuma sun kashe mutum guda tare da sace wasu uku a wani harin da suka kai a wani yanki da ke maƙwabta da makarantar Ilai Grammar school.
Rahotanni sun bayyana cewa manoma ne akasarin mazauna yankunan Jamroro da kewayen yankin Ilai.
Sanata Sunday Karimi ya yi Allah wadai da yawaitar hare-haren, yana mai neman ɗaukin gaggawa daga jami’an tsaro.
Sanarwar da ya fitar ta ce, “Baya ga rahoton kisa da sace mutane da ba a tantance yawansu ba a Cocin ECWA da ke Àaaaz-Kiri a Ƙaramar Hukumar in Kabba/Bunu ranar Lahadi 14 ga Disamba, 2025.
“An kai makamancin harin a Oke-Agi da Ilai da ke Karamar Hukumar Mopamuro inda aka sace kashe mutum guda tare da sace wasu a al’umnar ƙabilar Tuve.”
Sanatan ya bayyana cewa hare-haren na ranar Lahadi sun tilasta wa mutane da dama a yankunan tserewa daga gidajensu, din haka ya yi kiransa a ɗauki tsauraran matakai don murƙushe ayyukan ’yan bindiga.
Ya kuma bayyana damuwa cewa sabon harin cocin ya faru ne ba da daɗewa ba bayan ’yan bindiga sun sace wasu masu ibada a Cocin Cherubim and Seraphim da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Gabas a Jihar.
Shi ma da yake jajen waɗanda abin ya shafa, Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kogi, Kingsley Fanwo, ya bayyana cewa ana ɗaukar matakan ganin an samu tsawon a kwanciyar hankali a yankunan Illai da Okeagi over the attack.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Mopamuro, Ademola Bello da a sarakunan gargajiya a yankunan sun tabbatar da hare-haren, Oke-agi and Ilai, inda rahotanni ke cewa sun je asibiti domin dubiyar mutane da a suka samu raunuka a hare-haren.
Zuwa lokacin da muka samu wannan rahoto dai kakakin rundunar ’yan sanda a Jihar Kogi, CSP William Aya, bai amsa kira da sakonnin neman bahasi da wakilinmu ya tura masa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare Ƙaramar Hukumar yan bindiga sun a Jihar Kogi ranar Lahadi
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
Dakarun Sojin Operation HADIN KAI sun daƙile wani hari da ’yan ta’addan ISWAP suka kai sansanin soji na Mairari da ke Jihar Borno.
Harin ya fara ne daga daren ranar Juma’a zuwa safiyar Asabar.
’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEAA cewar rundunar, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin shiga sansanin ta hanyar amfani da motoci biyu da suka cika su maƙil abubuwan fashewa.
Jami’in yaɗa labarai na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanal Sani Uba, ya ce sojoji sun gano motocin kuma suka tarwatsa su kafin su kai ga shiga sansanin.
Rahotanni sun nuna cewa an kashe ’yan ta’adda da dama, yayin da wasu suka jikkata.
Waɗanda suka tsira sun kwashe gawarwaki da waɗanda suka ji rauni a wajen bayan tafka artabu.
Bayan daƙile harin, sojoji tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, sun gudanar da bincike a yankin.
A yayin binciken, sun gano gawar ’yan ta’adda tare da ƙwato makamai da kayayyaki da dama da suka bari.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi, harsasai, gurneti, babura, na’urorin sadarwa, kayan yaƙi, da kayayyakin jinya.
Laftanar Kanal Uba, ya ce ƙwato waɗannan kayayyaki ya rage ƙarfin ’yan ta’addan da ikonsu na ci gaba da kai hare-hare a yankin.
Ya ƙara da cewa dakarun sun lalata motocin da aka maƙare da kayan fashewa, wanda ya jawo lalacewar wasu wurare biyu, amma ba su yi nasarar shiga sansanin sojin ba.
Ya ce a halin yanzu sojoji na ci gaba da yin sintiri domin hana sake kai hare-hare tare da bai wa al’ummar yankin tabbacin tsaro.
Rundunar sojin ta jaddada ƙudirinta na kawar da ’yan ta’adda tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Arewa maso Gabas.