Leadership News Hausa:
2025-07-09@07:53:44 GMT

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Published: 9th, March 2025 GMT

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Muhimmancin sadaka na da yawa baya ga kariya da take yi, sadaka tana hana bambancin da ake yi tsakanin mai kudi da kuma talaka, sadaka tana hada kan al’umma musulmi guri daya, tana taimakawa marayu, masu takaba da manya wadanda suka manyanta wajen nuna musu cewar suma suna da gata, tana kuma kusanto mutum da Allah ta’alla.

Wadanda ya kamata a bawa sadaka; Marayu, iyalai masu karamin karfi, masu takaba, ‘yan gudun hijra, dalibai da sauransu. Hanyoyin bada sadaka na da dumbin yawa kamar; bada sadaka ta hanyar bada kudi, yinta ta hanyar dauke abu daga kan hanya wanda zai cutar da dan’Adam, hada kungiya ko kirkirar kungiya ko bada gudunmawa a kungiyar taimakon al’umma, ko bada kaya a madadin yardar su, bada kayan abinci a dafe ko danye da dai sauransu. Shawara ga marasa yin sada shi ne su rinka yi da kadan-kadan domin kuwa sadaka ba ta yin yawa ba ta kadan, komai kankantar sadakar da kayi sadaka ce indai har da zuciya da ka bada ita, sannan su san amfanin sadaka, su san hanyoyin sadaka.

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To magana ta gaskiya muhimmancin sadaka a rayuwar dan’adam musamman musulmi tana da yawa, musamman sadakar da aka yi domin Allah, domin tana taimakawa wajen karbar addu’a, kawar da masifu dama karin budi a fannoni da dama na rayuwa don haka muhimmancin sadaka ya fi gaban kidayawa. To magana ta gaskiya wadanda ya kamata a bawa sadaka sunada yawa ,kamar; maskinai, masu karamin karfi, matafiya dama ‘yan’uwa makusanta. To hanyoyin yin sadaka sunada dama kamar; ciyarwa, samar da ruwan sha, rabawa al’umma kudi ko kayan abinci dama fadawa mutane kyakkyawar magana domin ita ma sadaka ce, don sadaka tana da nau’oi da yawa. To magana ta gaskiya kin yin sadaka ga masu hali tamkar tauye Kai ne, domin yin sadaka taimakon kai ne, domin ita sadaka tana bude kofofin alkairai da dama ga masu yin ta, don haka ya kamata mu daure mu rika yin sadaka daidai karfin mu domin za ta zama budi a gare mu, Allah ya bamu ikon yin sadaka domin Allah.

 

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Tana maganin Masifa da wani iftila’ in da bai zo wa bawa ba.

Muskinai musamman wadanda ba su da lafiyar da za su iya neman na kansu wadanda sai an taimaka musu ko sun fito bara suke samun abin da za su ci. Hanyoyin yinta suna da yawa amma wacce Allah ya fi so ita ce; wadda za ka yi da hannun dama hagun ba ta sani ba. Gaskiya shawarata a gare su su daure su rika ko babu yawa kuma ayi ta domin Allah badon ayi a burge wasu ba, sabida koda ayyukan da mamaci yake mora bayan mutuwarsa akwai sadaka a cikinsu to kun ga kuwa ita sadaka ba karamin aikin lada bace gaskiya. Allah ya sa mu dace.

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Sadaka magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka Sadaka garkuwa ce daga sharrin arayi, ko gobara, da dai sauran su. Sadaka na daya daga samun sauki da waraka daga cuta ko wacce irin matsala. A cikin hadisin manzon Allah (S.A.W) an ambaci cewa; sadaka na iya kawar da bala’i kuma tana warkar da cututtuka. Shawara idan mutum yana sadaka tana hana bala’i, sadaka na jawo albarka, sadaka na tsarkake rai da kuma dukiya, sadaka nasa Allah ya saukaka wa mutum.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadam

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

Wannan matakin ya biyo bayan shawarar Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na ASUU wanda ya amince da tsarin “Ba Albashi, Ba Aiki” saboda yawan jinkirin biyan albashi da suke fuskanta.

ASUU ta ɗora laifin hakan kan Ofishin Akanta-Janar na Tarayya.

Shugaban ASUU na ƙasa, Farfesa Chris Piwuna, ya bayyana a ranar Litinin cewa gwamnatin na nuna halin ko-in-kula kan batun.

Ya ce duk da yawan ganawa da jami’an gwamnati, malamai na fuskantar jinkirin albashi ba tare da wani dalili ba.

“Muna so mu yi aiki, amma ba za mu iya ba saboda ba su ba mu damar yin haka ba. Wannan aiki ne da aka yi da gangan. Matsalar ba daga wajen tsarin biyan albashi ba ne, matsalar tana wajen mutanen da ke da alhakin sakin kuɗin ne,” in ji Piwuna.

Ya ƙara da cewa sauyi tsarin biyan albashi daga IPPIS zuwa GIFMIS ya ƙara jefa malamai cikin wahala.

ASUU ta ce duk wata Jami’a da ba a biya malamanta albashin Yuni kafin 7 ga Yuli ba, to, ya kamata su fara yajin aiki nan take.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  • Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
  • Kungiyoyin Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Mamayar Isra’ila Kan Kasar Yemen
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya