Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Published: 9th, March 2025 GMT
Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:
Muhimmancin sadaka na da yawa baya ga kariya da take yi, sadaka tana hana bambancin da ake yi tsakanin mai kudi da kuma talaka, sadaka tana hada kan al’umma musulmi guri daya, tana taimakawa marayu, masu takaba da manya wadanda suka manyanta wajen nuna musu cewar suma suna da gata, tana kuma kusanto mutum da Allah ta’alla.
Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:
To magana ta gaskiya muhimmancin sadaka a rayuwar dan’adam musamman musulmi tana da yawa, musamman sadakar da aka yi domin Allah, domin tana taimakawa wajen karbar addu’a, kawar da masifu dama karin budi a fannoni da dama na rayuwa don haka muhimmancin sadaka ya fi gaban kidayawa. To magana ta gaskiya wadanda ya kamata a bawa sadaka sunada yawa ,kamar; maskinai, masu karamin karfi, matafiya dama ‘yan’uwa makusanta. To hanyoyin yin sadaka sunada dama kamar; ciyarwa, samar da ruwan sha, rabawa al’umma kudi ko kayan abinci dama fadawa mutane kyakkyawar magana domin ita ma sadaka ce, don sadaka tana da nau’oi da yawa. To magana ta gaskiya kin yin sadaka ga masu hali tamkar tauye Kai ne, domin yin sadaka taimakon kai ne, domin ita sadaka tana bude kofofin alkairai da dama ga masu yin ta, don haka ya kamata mu daure mu rika yin sadaka daidai karfin mu domin za ta zama budi a gare mu, Allah ya bamu ikon yin sadaka domin Allah.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:
Tana maganin Masifa da wani iftila’ in da bai zo wa bawa ba.
Muskinai musamman wadanda ba su da lafiyar da za su iya neman na kansu wadanda sai an taimaka musu ko sun fito bara suke samun abin da za su ci. Hanyoyin yinta suna da yawa amma wacce Allah ya fi so ita ce; wadda za ka yi da hannun dama hagun ba ta sani ba. Gaskiya shawarata a gare su su daure su rika ko babu yawa kuma ayi ta domin Allah badon ayi a burge wasu ba, sabida koda ayyukan da mamaci yake mora bayan mutuwarsa akwai sadaka a cikinsu to kun ga kuwa ita sadaka ba karamin aikin lada bace gaskiya. Allah ya sa mu dace.
Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:
Sadaka magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka Sadaka garkuwa ce daga sharrin arayi, ko gobara, da dai sauran su. Sadaka na daya daga samun sauki da waraka daga cuta ko wacce irin matsala. A cikin hadisin manzon Allah (S.A.W) an ambaci cewa; sadaka na iya kawar da bala’i kuma tana warkar da cututtuka. Shawara idan mutum yana sadaka tana hana bala’i, sadaka na jawo albarka, sadaka na tsarkake rai da kuma dukiya, sadaka nasa Allah ya saukaka wa mutum.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ramadam
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya yi wata waqa da ya yi wa laqabi da suna ‘Arewa’.
Muhsin wanda ya fi qwarewa a fagen waqoqin ‘Gambara’, da aka fi sani da Hip Hop, bayyana wa Aminiya cewa, halin da Arewacin Nijeriya ya shiga na rashin tsaro shi ne jigon waqarsa.
A cikin waqar haziqin mawaqin, ya yi tsokaci a kan yadda shugabanni a Arewa suka yi biris da halin da talakawa suka tsinci kansu a ciki na barazanar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro. Inda yake qoqarin ganin ya jawo hankalin masu muli da ma talakawa don su farka daga barci.
Matashi mawaqin ya ce, “waqata mai taken ‘Arewa’, waqa ce da zan ce na yi ta ne saboda in tayar da shugabanni da kuma talakawan Arewacin Nijeriya daga barci. Domin kuwa ga gobara nan ta tunkaro mu daga kogi amma kuma da alamu babu wanda ya damu da ita.”
Da yake amsa tambayar ko me ya sa ya zavi yin amfani da waqa don wayar da kan jama’a kan muhimmancin haxin kai don tunkarar wannan matsala? Mawaqin zamanin sai ya ce, “ka san kowa da dutsen da ke hannunsa zai yi jifa. Don haka tunda yake ina da fasahar waqa, shi ya sa na ga wannan ita ce, kawai hanya xaya tilo da tafi sauqi wajena in isar da wannan muhimmin saqo.”
Matashin ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu akwai fitattun mawaqan da suka yi waqoqi kan abin da ya shafi tavarvarewar tsaro a qasa. Amma duk da haka, ya dace manya fitattun mawaqa na zamani da duniya ta san su, su qara qaimi wajen wayar da kan matasa don su guji shiga ayyukan laifi da ke jefa qasa cikin rashin tabbas.
SKD Arewa, ya kuma shawarci matasan mawaqa da su rungumi karatu, domin a cewarsa, ilimi ne zai taimaka musu wajen inganta sana’o’insu kuma ya basu damar amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata fasahohinsu.