Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce dagewar da wasu kasashe masu cin zarafi suka yi na yin shawarwari da Iran na yi ne don neman amfanin kansu.

Ayatullah Khamenei ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da manyan jami’ai na bangarori uku na gwamnati a ranar Asabar.

Jagoran ya ce “Dagewar da wasu gwamnatoci suka yi kan yin shawarwari ba wai don warware al’amura ba ne, a’a yana nufin aiwatar da abin da suke so.”

Ayatullah Khamenei ya kara da cewa: ” Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta amince da abin da suke tsammani ba.”

Wadannan gwamnatocin da suke cin zalin ba sa neman yin shawarwari kan batun nukiliya kawai; A maimakon haka, suna amfani da shawarwari a matsayin “hanyar cimma manufofinsu” a fannoni kamar karfin tsaron Iran da karfin kasa da kasa, wadan ko shakka babu Iran za ta yi watsi dasu.

Ya kara da cewa, suna tabo batun tattaunawar ne domin matsa lamba kan ra’ayin jama’a, don haka Iran ta ki yin shawarwari da su, duk da cewa sun nuna a shirye su ke.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran

Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai

Al’ummar Iran masu daraja!

Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.

Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.

A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.

Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.

Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122