HausaTv:
2025-11-24@07:29:18 GMT

Senegal, Ta Karbi Wasu Sansanonin Sojin Faransa A Kasar

Published: 9th, March 2025 GMT

Senegal ta karbi wasu sansanonin soja na faransa a kasar a wani bangare na janye sojojin faransar daga kasar ta Yammacin Afirka.

Ofishin jakadancin Faransa a Dakar ya sanar da cewa an mika wurare da gidaje a yankunan Marechal da Saint-Exupery na Dakar ga hannun gwamnatin Senegal.

Sauran kuma “za a mika su ne kamar yadda bangarorin biyu suka amince da jadawalin da suka sanya wa hannu”.

A ranar 12 ga Fabrairu Faransa ta sanar cewa ta kafa wani kwamiti na hadin gwiwa da Senegal da zai shirya tsare-tsaren ficewar sojojin Faransa da kuma mika sansanonin zuwa karshen shekarar nan.

 “Kwamitin ya kuma kaddamar da aikin yin garen-bawul ga hadakar tsaro,” a cewar sanarwar.

A watan Nuwamban 2024 ne Shugaba Bassirou Diomaye Faye wanda ya lashe zabe bisa akidar kawo sauyi, ya bayyana cewa duka sojojin Faransa da na kasashen waje za su fita daga Senegal zuwa karshen 2025.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta ce labarin da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta na kai wa cocin ECWA da ke Kashere hari, ba gaskiya ba ne.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne, ya bayyana haka, inda ya ce sun bincika tare da gano cewar jita-jita ce.

Ya ce DPO na Pindiga da shugaban ofishin ’yan sanda na Kashere, sun tuntuɓi wani dattijo da ya halarci cocin domin yin addu’a a ranar Lahadi.

Dattijon ya shaida musu cewa babu wani abu da ya faru, kuma ’yan sanda suna harabar cocin tun safe a domin kula da sha’anin tsaro kamar yadda suka saba.

Rundunar ta ce yaɗa irin wannan jita-jitar na iya tayae da hankalin jama’a.

Ta kuma ce ta fara bincike domin gano wanda ya ƙirƙiri wannan labari domin ɗaukar matakin doka a kansa.

DSP Abdullahi, ya roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu, tare da ci gaba da harkokinsu, inda ya tabbatar da cewa ’yan sanda za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’ar jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba
  • Iran: HKI Na Faskantar Mummunan Aikin Leken Asiri Daga Kasar
  • Venezuela Ta Gargadi Amurka Kan Shirin Tada Hankali A Kan Iyakokin Kasar
  • Unifil: Girmama Hurumin Kasar Lebanon Ne Ginshikin Kuduri Mai Lamba 1701
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Wani Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • Shugaban Rasha yace Ba zai Janye Ayyukan Soji  Da Yake Yi A Kasar Ukrain Ba