Kamaru: Jam’iyyun adawa sun ayyana Bakary a matsayin wanda ya lashe zaɓe
Published: 14th, October 2025 GMT
Jam’iyyun adawa a ƙasar Jamhuriyar Kamaru sun ayyana Issa Bakary Tchiroma a matsayin wanda lashe zaɓen shugaban ƙasar da gagarumin rinjaye.
Gamayyar jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin fararen hula na Union for Change ta ce sakamakon da suka tattara daga fadin ƙasar da ƙasashen waje ya nuna Bakary ya samu kashi 60 zuwa 80 cikin ɗari na ƙuri’u a rumfunan zaɓe da dama.
Sun buƙaci Shugaba Paul Biya, wanda ke neman wa’adin mulki na takwas a zaɓen da ya gaggauta miƙa saƙon taya murna ga Issa Bakary Tchiroma.
“Muna kira ga shugaban ƙasa mai barin gado da ya gaggauta taya sabon shugaban ƙasa murna,” in ji ƙungiyar,” in ji wata sanarwa da shugabannin ƙungiyar, Anicet Ekane da Djeukam Tchameni, suka fitar a birnin Douala.
Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph“’Yan Kamaru sun yanke shawara. Sakamakon da muke karɓowa daga sassan ƙasar da ma ƙetare ya nuna a sarari cewa, ɗan takarar talakawa, Issa Tchiroma Bakary, ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 12 ga Oktoba 2025,” in ji sanarwar.
Ƙungiyar ta zargi jam’iyyar mai mulki ta CPDM da ƙoƙarin amfani da “tsohuwar hanyar maguɗi,” amma ta ce duk da haka Bakary ya yi mata “mummunar kaye mara misaltuwa,”
Union for Change 2025 ta kuma roƙi hukumomin gwamnati da jami’an tsaro da su mutunta zabin al’umma da zaman lafiya, tare da kira ga ’yan ƙasa da su ci gaba da kasancewa cikin shiri domin kare zaɓinsu.”
Bakary, wanda tsohon minista ne a gwamnatin shugaba Paul Biya, an zaɓe shi a watan Satumba a matsayin “ɗan takarar haɗin kai na jama’a.”
Ƙungiyar, wadda rahotanni ke cewa ta ƙunshi fiye da ƙungiyoyi 50 na siyasa da na fararen hula, ta ce manufarta ita ce haɗa ɓangarorin adawa domin yin aiki tare wajen sauyin siyasa da sake gina ƙasa.
“Ƙungiyar Talakawa ce, wadda take buɗe ƙoa ga kowa — ɗan ƙasa ko ƙungiya, ciki har da waɗanda ’yan takararsu aka hana shiga zaɓen shugaban ƙasa ba bisa ƙa’ida ba,” in ji sanarwar.
Ƙungiyar ta bayyana kanta a matsayin sabuwar ƙarfi na farfaɗo da dimokuraɗiyya, tana mai alƙawarin sake gina Kamaru a cikin lokacin canji na shekaru uku zuwa biyar.
A lokacin da ake rubuta wannan rahoto, Hukumar Ƙoli ta Ƙasar ba ta fitar da sakamakon hukuma ba, lamarin da ake ganin zai iya ƙara ɗaga zullumin siyasa a kwanaki masu zuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bakary Tchiroma Issa Bakary Tchiroma Kamaru Paul Biya Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.
Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA