Aminiya:
2025-10-13@13:38:00 GMT

’Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da kashe ma’aikaciyar Arise TV a Abuja

Published: 9th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, sun kama mutum 12 da ake zargi da hannu a kisan ma’aikaciyar Arise TV, Somtochukwu Christella Maduagwu, a unguwar Katampe da ke Abuja.

Rahotanni sun nuna cewa Somtochukwu, ta rasu bayan faɗowa daga bene mai hawa uku, yayin da ta ke ƙoƙarin tserewa daga hannun ’yan fashin, yayin da mai gadin gidan ya rasa ransa bayan harbin bindiga.

Najeriya ta tafka asarar tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram – UNICEF Majalisa ta yi watsi da zargin Amurka na yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya

Wata majiyar ’yan sanda ta bayyana cewa rundunar Scorpion Squad ƙarƙashin jagorancin ACP Victor O. Godfrey ce ta kama waɗanda ake zargin.

Wasu daga cikin waɗanda aka kama sun amsa laifinsu, inda ɗaya daga cikinsu ya ce shi ne ya harbi mai gadin gidan, yayin da wani ya ce ya yi ƙoƙarin riƙe ’yar jaridar lokacin da za ta faɗo.

Sun kuma bayyana cewa sun sace wata mota ƙirar Honda CR-V mallakin ’yar jaridar, sannan kowa daga cikinsu ya samu Naira 200,000 daga kuɗin da suka sato.

’Yan sanda sun ƙwato bindigogi, harsasai, wuƙaƙe da wayoyi daga hannunsu.

An sake kama wasu daga cikinsu a ranar 8 ga watan Oktoba, lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa aikata wani fashin a Maitama.

Kakakin rundunar Abuja, Josephine Adeh, ta ƙi yin bayani kan lamarin, amma Lere Olayinka, mai taimaka wa Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya tabbatar da kama waɗanda ake zargin a shafukansa na sada zumunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi yar jarida ARISE TV Babban Birnin Tarayya zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno

Ana fargabar sojoji da dama sun rasu yayin da mayaƙan Boko Haram suka kai hari sansanin soji da ke Ngamdu, a Ƙaramar Hukumar Kaga a Jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa mayaƙan sun kai wa sojojin hari a sansanin da ke kan hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe Kwastam ta kama buhunan lalatacciyar fulawa 10,000 ana ƙoƙarin shigo da ita Najeriya

Biyo bayan harin, sojoji sun rufe hanyar Ngamdu har zuwa ƙarfe 11:20 na safe, wanda hakan ya sa matafiya suka maƙale na tsawon lokaci.

“Na tashi daga Damaturu da sassafe ina fatan isa Maiduguri kamar ƙarfe 9 na safe, amma da na isa Ngamdu sai muka tarar da hanya a rufe,” in ji wani matafiyi.

“Jami’an tsaro sun ce mu yi haƙuri saboda an samu matsala a hanya. Daga baya mazauna yankin suka ce Boko Haram ne suka kai wa sojoji hari tare da kashe wasu daga cikinsu.”

Wani mazaunin yankin ya ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ba tare da tsammani ba.

“Harin ya ɗauki lokaci mai tsawo kafin ’yan ta’addan su tafi, amma sun kashe sojoji kuma sun ji wa wasu rauni,” in ji shi.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da faruwar harin, amma ta ce ba a rasa rayuka da yawa kamar yadda aka yaɗa ba.

“‘Yan ta’addan sun yi ƙoƙarin yi wa sojojin kwanton ɓauna, amma sojojinmu jarumai sun yi tsayin daka.

“Wasu daga cikinsu sun ji rauni an kuma kai su asibiti, amma an kashe ’yan ta’adda da dama,” in ji majiyar.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar sojojin Najeriya ba ta fitar da sanarwa kan harin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno