Majalisa ta yi watsi da zargin Amurka na yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya
Published: 9th, October 2025 GMT
Majalisar Wakilai, ta yi watsi da zargin da Ƙasar Amurka, ta yi na cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Wannan martani na zuwa ne bayan wani Sanatan na Amurka, Ted Cruz, ya gabatar da ƙudirin doka a Majalisar Dattawan ƙasar, inda ya ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Sauye-sauyen Tinubu ba su rage talauci a Najeriya ba — Bankin Duniya Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata rahoton Bankin Duniya kan yawan talakawa a NajeriyaA yayin gabatar da ƙudirin ya buƙaci a ƙaƙaba wa wasu jami’an Najeriya takunkumi.
Cruz ya ce: “ Ana kashe Kiristocin Najeriya saboda addininsu… lokaci ya yi da za a ɗauki mataki na gaske kan jami’an Najeriya da ke taimaka wa irin waɗannan ayyuka.”
Sai dai ’yan majalisar Najeriya sun yi watsi da wannan batu.
Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ya ce wannan iƙirarin ba gaskiya ba ne game da halin da Najeriya ke ciki.
“Matsalar tsaro a Najeriya tana da yawa, ta’addanci, ‘yan fashi, rikicin manoma da makiyaya, kuma tana shafar mutane na kowane addini,” in ji Kalu.
“Ba daidai ba ne a fassara waɗannan matsaloli a matsayin hare-haren da gwamnati ke kai wa addini ɗaya ba.”
Majalisar ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aike wa Amurka mar6a hukumance, tare da tattaunawa don fahimtar juna kan wannan lamari.
Haka kuma, ’yan majalisar sun buƙaci a gaggauta naɗa jakadun Najeriya a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.
Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, shi ma ya yi watsi da zargin Cruz, inda ya ce “ba gaskiya ba ne kuma babu wata hujja da ta tabbatar da hakan.”
“Ba gaskiya ba ne cewa an ƙome coci sama da 20,000 ko kuma an kashe Kiristoci 52,000,” in ji shi.
“Najeriya ƙasa ce mai addinai da dama. Babu wani jami’in gwamnati da zai goyi bayan tashin hankali a kan addini.”
Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta tabbatar da cewa an kai wa wasu Kiristoci hare-hare, amma ta ce matsalar tana shafar kowa, don haka gwamnati ta tabbatar da adalci.
“Kiristoci da dama sun rasa rayukansu a wuraren ibada,” in ji Archbishop Daniel Okoh, shugaban CAN.
“Muna kira ga gwamnati da hukumomin tsaro su kare raykan dukkanin ‘yan ƙasa baki ɗaya, kuma a hukunta masu laifi.”
Majalisar ta jaddada cewa Najeriya na da ’yancin yin addini kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada, tare da kira ga haɗin kai da fahimtar juna don kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ke shafar kowa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Najeriya Watsi zargi yi watsi da
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
Shugaban kasar Sudan kuma babban kwamandan sojojin kasar Janar Abdulfattah Alburhan, ya yi watsi da shawarar Amurka ta kawo karshen yaki a kasarsa wanda ya lakume rayukan mutane da dama, ya kuma raba kasar gida biyu a cikin watanni kimani 30 da suka gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘AfricaNews’ ya nakalto Burhan yana fadar haka a ranar Lahadi jim kadan bayan ganawarsa da tawagar kasar Amurka wacce ta gabatar masa da shawarar, ya kuma bayyana ta a matsayin mafi munin shawarar tsagaita budewa juna wuta da aka gabatar masa ya zuwa yanzun. Burhan ya zargi Massad Boulos mai bawa shugaban kasar Amurka a kan al-amuran nahiyar Afirka da da kokarin rusa sojojin kasar Sudan da kuma bawa yan tawaye karkashin jagorancin Amity damar ci gaba da iko da wani daga bangaren kasar.
Burhan ya zargi Amurka da goyon bayan yan tawayen a cikin shawarar da ta gabatar, kuma shawarar ba irin zaman lafiyan da mutanen sudan suke so ba. Masana suna ganin gwamnatin Amurka da kawayenta wadanda suke goyon bayan yantawaye a duniya musamman a cikin kasashen Larabawa suna son sake raba kasar Sudan ne, kuma sun gabatar da wannan shawarar ce a dai-dai lokacinda suka fahinci cewa gwamnatin kasar tana samun nasara a kan yan tawaye wadanda suke iko da yankin Darfur na yammacin kasar ta Sudan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci