Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
Published: 4th, November 2025 GMT
Sarakunan gargajiya, lauyoyi da jami’an gwamnati sun koka bisa yawaitar kananan ’yan mata da ke daukar ciki da kuma zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba, a sansanonin ’yan gudun hijira da ke Maiduguri, Jihar Borno.
Lamarin ya fito fili ne a wani taron tattaunawa na kwanaki biyu da ƙungiyar Grassroots Researchers Association (GRA) ta shirya tare da tallafin We Are Not Weapons of War (WWoW) a karshen makon da ya gabata a Maiduguri.                
      
				
Taron ya haɗa mutane fiye da 500, ciki har da waɗanda suka tsira daga fyade da cin zarafi a lokacin rikici, sarakunan gargajiya, lauyoyi, jami’an gwamnati da abokan ci gaban ƙasa, domin tattauna hanyoyin magance wannan matsala.
“’Yan mata kanana na sayar da jikinsu, suna kuma zubar da ciki a bandaki,” in ji wata mai taimaka wa GRA, Zaynab Abdallah.
NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a KanoShugaban sansanin ’yan gudun hijira na EYN Jerusalem da ke unguwar Wulari a Maiduguri, Mista John Gwoma, ya bayyana yadda kananan ’yan mata da ƙananan yara ke fadawa tarkon lalata da kuma zubar da ciki a asirce.
Ya ce, “Wasu maza daga cikin gari kan zo cikin manyan motoci su ɗauki waɗannan ’yan mata ƙanana, su yi lalata da su har su sami ciki. Saboda haka yanzu zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba ya zama ruwan dare a sansanin.”
Ya ƙara da cewa, “Bandakunan mata sun koma kamar mayanka. Ana samun jini ko’ina saboda waɗannan ’yan matan na shiga su zubar da ciki sannan su bar tayin a ciki. Wasu iyaye na sane da abin da ’ya’yansu ke yi”
Wata mai taimaka wa GRA, Zaynab Abdallah, ta tabbatar da wannan zargi, tana mai cewa karuwanci da kuma zubar da ciki tsakanin ƙananan yara na ƙara yaduwa a Maiduguri.
Ta ce, “Wasu daga cikin waɗannan ’yan mata ƙanana suna lalata ne domin samun kuɗin abinci ga iyalansu. Amma abin takaici, wasu iyaye suna sane da hakan, amma suna yi shiru saboda suna amfana da abin da ’ya’yansu ke samu.”
Zaynab ta ci gaba da cewa, “Talauci ya kai ga karuwanci ya zama tamkar wani ɓangare na rayuwarsu. Ba za ka iya hana su ba. Idan sun sami ciki, sai su zubar da shi a ɓoye domin guje wa tozarci.”
Rikici da talauci sun kai mata ga lalacewa”A yayin zaman, waɗanda suka tsira daga fyade da sauran masu ruwa da tsaki sun ruwaito irin raɗaɗin da suka sha na fyade, da kuma yadda matsin tattalin arziki ke tura mata cikin harkar karuwanci.
Sai dai sun kuma bayyana yadda gangamin wayar da kai na GRA ya taimaka wajen rage tozarci da suka sha, tare da ƙara musu ƙarfin guiwa wajen neman adalci a kotuna.
Daraktan gudanarwa na ƙungiyar GRA, Mista Friday Bitrus, ya ce sakamakon tattaunawar da suka samu daga mahalarta zai zama ginshiƙi wajen fitar da takardar “Kira ga Daukar Mataki” domin tursasa gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su ɗauki matakai na gaskiya.
Ya ce, “Abin da muka tattara daga bakin waɗanda abin ya shafa da sauran mahalarta ya nuna cewa akwai gaggawar buƙatar tsari na musamman don kare ’yan mata da mata daga fyade, ciki da kuma zubar da ciki a sansanonin.”
Kira ga gwamnatiMasu ruwa da tsaki a taron sun yi kira ga gwamnati ta ƙara tsaurara matakai wajen tsaron sansanonin, ta samar da abinci da kayan masarufi, da kuma hanyoyin koyar da sana’o’in dogaro da kai ga ’yan gudun hijira — musamman mata da matasa.
Sun kuma bukaci a hukunta duk wanda aka kama da laifin lalata da yara a sansanonin, tare da samar da ingantattun cibiyoyin kula da lafiya domin dakile zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba.
A cewar wani mahalarcin taron, “Wannan matsala ba wai ta Borno ce kawai ba, tana iya bazuwa zuwa sauran jihohi idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba.”
Taron ya ƙare da amincewa da kafa kwamitin bin diddigi domin tabbatar da cewa an aiwatar da shawarwarin da aka cimma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: da kuma zubar da ciki yan gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza
Turkiyye na karbar bakuncin wani taron ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan halin da ake ciki a Gaza.
Wannan taron ya zo ne bayan makonni uku da fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.
A cewar Turkiyya, manufar taron ita ce taimakawa wajen mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sake tabbatar da rawar da take takawa a wannan batu.
Ƙasashen musulmin dake halartar taron na yau Litini a Istanbul su ne wadanda Donald Trump ya aminta dasu don tabbatar da nasarar shirin zaman lafiya na Gaza.
Ministan Harkokin Wajen Turkiyye Hakan Fidan, wanda ke karbar bakuncin takwarorinsa, ya gabatar da wannan taron a matsayin hanyar yin nazari kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, samar da matakai na gaba, da kuma daidaita su kafin tattaunawa da kasashen Yamma.
Haka kuma hanya ce ga wadannan kasashen da suka fi yawan al’ummar Musulmi su nuna jajircewarsu wajen kiyaye yarjejeniyar tsagaita wuta.
Ya bayyana tsagaita wuta a matsayin mafi rauni idan aka yi la’akari da kalubalen da mataki na biyu na shirin ke fuskanta.
Mataki na biyu na shirin na Trump ya tanadi kwance damarar makamai na kungiyar Hamas, samar da rundunar sulhu, da sauransu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza November 3, 2025 Girgizar kasa ta yi ajalin gomman mutane a Afghanistan November 3, 2025 Najeriya : tun kafin kalamman Trump muka dauki matakai November 3, 2025 Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali November 3, 2025 UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza November 3, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza November 3, 2025 El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci