An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
Published: 4th, November 2025 GMT
Jami’an tsaro sun kama wani mutum da wayoyin sata guda 17 da kuma kudi a wurin taron sauyin shkear Gwamna Douye Diri daga Jam’iyyar PDP zuwa APC.
A ranar taron, Gwamna Diri tare da yawancin ’yan majalisar dokokin jihar Bayelsa sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar PDP zuwa APC, a gaban Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, da wasu gwamnoni da manyan jami’an siyasa na ƙasa.                
      
				
Shugaban sa-kai na jihar, Doubiye Alagba, wanda ya jagoranci kama wanda ake zargin, ya bayyana cewa an mika mutumin ga jami’an Operation Puff Adder na rundunar ’yan sandan jihar domin gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.
A cewar Alagba, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya shigo daga jihar Ribas ne musamman domin amfani da taron siyasar da aka shirya wajen yin sata.
Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a NajeriyaYa ce jami’ansu sun kama shi ne bayan sun lura da motsinsa da ya sa suka zarge shi. Bayan bincike, sai suka gano wayoyi 17, kudi N91,000, da kuma katunan ATM da dama a cikin jaka da yake dauke da ita.
Alagba ya kara da cewa, Francis ya shaida musu cewa yana aiki tare da wasu abokan laifi da suka tsere yayin kamun.
Ya kuma bayyana cewa kafin a kama shi, sun riga sun kwashe sama da N400,000, sannan daya daga cikin wadanda suka gudu yana da karin wayoyi da sauran kayayyakin da suka sace.
Shugaban sa-kai din ya gargadi masu aikata laifuka da su guji shiga Bayelsa, yana mai cewa jami’ansa sun samu horo na musamman kan tattara bayanan sirri, lura da halayen jama’a da kuma tsaron taruka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa Gwamna Diri waya wayoyo
এছাড়াও পড়ুন:
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA