Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano
Published: 5th, November 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa daƙile hare-haren ’yan bindiga a wasu sassan jihar.
Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.
Kocin Super Eagle ya lashi takobin lashe kofin nahiyar Afirka Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na AmurkaAbba ya yi wannan yabo ne, yayin da yake karɓar babban kwamandan rundunar soji ta 1, a Hedikwatar Kaduna, Manjo Janar Abubakar Sadiq Muhammad Wase, a fadar gwamnati da ke Kano.
Manjo Janar Wase, ya ziyarci Kano domin duba halin tsaro a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa.
Ya bayyana yadda mahaifinsa, marigayi Kanal Muhammad Abdullahi Wase, ya taɓa zama kwamishinan soja na Jihar Kano a shekarar 1994.
“Tun lokacin da na karɓi jagorancin rundunar, na ziyarci wuraren da aka kai hare-hare domin na yaba wa jarumtar sojojimmu,” in ji Janar Wase.
Gwamnan ya gode wa sojoji bisa jajircewarsu, tare da jinjina wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan naɗa sabbin hafsoshin tsaro masu ƙwazo da kishin ƙasa.
Ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda 10 da babura 60 ga rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yankunan da abin ya shafa.
Haka kuma ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu.
Idan ba a manta Aminiya ta ruwaito yadda dakarun soji suka daƙile hari tare da kashe ’yan bindiga 19 a yankin Shanono yayin wani samame da suka kai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Abba hari Tsanyawa Tsaro yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
Daga Yusuf Zubairu Kauru
Al’ummar Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun shiga halin kaka-ni-ka-yi duba da yadda rayukansu ke kasancewa cikin hadari yayin da suke gonakinsu.
A wata tattaunawa ta wayar tarho, wani jagoran matasa, Junaidu Ishaq, ya bayyana cewa kusan shekaru biyar ke nan da hare-haren ’yan bindiga ke ta faruwa akai-akai, wanda ya bar al’umma cikin fargaba da ƙuncin rayuwa.
Ya ce manoma suna shiga gonakinsu ne cike da fargaba domin komi na iya faruwa yayin da suke aiki a gonakin.
Mazauna yankin sun bayyana cewa Kauru, wadda aka fi sani da yawan gonaki da ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da abinci a jihar Kaduna, yanzu manoma ba sa iya shiga gonakinsu cikin kwanciyar hankali saboda yadda ‘yan bindiga ke yawan kai musu hare-hare.
A koda yaushe iyayen yara suna fargaba kada ‘ya’yansu su yi nesa da su, yayin da iyalai da dama da ke fama da ƙangin talauci ke kara shiga cikin matsanancin hali.
Sun yi kira gwamnati da hukumomin tsaro su yi gaggawar kai ɗauki wanda zai bai wa manoman karkara kwarin gwiwa, waɗanda su ne ginshiƙin samar da abinci a yankin.
Mazaunan sun yi gargadin cewa idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, hare-haren na iya haifar da ƙaruwar matsalar rashin abinci da yawaitar ƙaura daga yankin.
“Idan zuwa gona zai sa mutumya rasa ransa, to lalle akwai babban matsala,” in ji wani manomi a yankin.
Sun yi fatan cewa za a dawo da zaman lafiya a yankin, yadda ƙasar da Allah Ya albarkace su da ita za ta ci gaba da ciyar da al’ummar Kauru ba wurin binne su ba.