Aminiya:
2025-11-05@00:10:36 GMT

Ba addini ne kaɗai ke haifar da rikici a Nijeriya ba — EU

Published: 5th, November 2025 GMT

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta EU ta ce ta fahimci cewa ba addini ne kaɗai ke haifar da rikice-rikice a Najeriya ba.

Jaridar Vanguwar ta ruwaito wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar kan harkokin ƙasashen ƙetare, Anouar El Anouni ya fitar, yana cewa ƙungiyar EU na jajanta wa mutanen da rikicin ya rutsa da su a Kudanci da Arewa maso Gabashin ƙasar.

HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar

Jaridar Vanguard ta bayyana cewa matakin na ƙungiyar EU na zuwa ne bayan da Shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, kan abin da ya kira kisan Kiristoci a ƙasar.

Sai dai EU ta ce akwai abubuwa da dama da ke haifar da rikicin ba addini kaɗai ba ciki har da talauci da siyasa.

“Mun fahimci cewa akwai abubuwa masu yawa da ke haifar da rikici a Najeriya, addini guda ne daga cikinsu, amma ba shi kaɗai ba,” in ji Mista El Anouni.

ECOWAS ta yi watsi da iƙirarin Trump

Ita ma Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS ta yi watsi da abin da ta kira iƙirarin ƙarya mai cike da hatsari da shugaban Amurka ya yi cewa ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi na far wa kiristoci tare da kashe su a Najeriya.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Talata, ECOWAS ta ce irin wannan barazana ta Shugaba Trump ka iya ta’azzara matsalar tsaro tare da haifar da matsalar zamantakewa a yankin da dama ke fama da matsalar masu tsattsauran ra’ayi.

ECOWAS ta jaddada cewa hare-haren masu tsattsauran ra’ayi a yankin Afirka ta Yamma na shafar mutanen da ba su ji ba su gani ba, ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ko jinsi ba.

Dangane da hakan ne ƙungiyar ta buƙaci ƙasashen duniya su tallafa wa kowace ƙasa wajen yaƙi da ta’addanci da ke shafar kowa da kowa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ECOWAS Tarayyar Turai ke haifar da

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

Fadar Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa nan da wasu kwanaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gana da takwaransa na Amurka, Donald Trump, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.

Mai ba wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan

A cewar Daniel Bwala, shugabannin biyu — Tinubu da Trump — sun yi tarayya da juna kan fahimta ta haɗin kai wajen yaƙi da ta’addanci da duk wata barazana ga bil’adama.

“A bayan nan Shugaba Trump ya taimaka wajen ba da izinin sayar wa Nijeriya makamai, kuma Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar yadda ya kamata wajen yaƙi da ta’addanci, kuma muna da sakamakon da za mu iya nunawa,” in ji Bwala.

Ya ƙara da cewa duk wani saɓanin fahimta kan ko ‘yan ta’adda a Nijeriya na kai hari ne ga Kiristoci kaɗai ko kuma mabiyan addinai daban-daban, “za a tattauna kuma a warware su” a yayin ganawar shugabannin biyu, wadda za ta gudana “ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, ko a Fadar White House da ke Washington.”

Sanarwar ta zo ne bayan barazanar Shugaba Trump ta kai farmaki a Nijeriya, inda ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta fara tsara yadda za a kai hari kan ƙasar, saboda abin da ya kira “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci” a Nijeriya.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce Amurka “a shirye take ta turo sojojinta da manyan makamai zuwa Nijeriya don kare Kiristoci,” yana mai cewa idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma “mai yiwuwa ta shiga ƙasar don kawar da ‘yan ta’adda masu zafin kishin Musulunci.”

Barazanar Trump ta jawo cece-kuce bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaiman inda ya samo waɗannan alƙaluman ba.

Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai kiyaye dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar
  • Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
  • Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
  • “Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
  • Barazanar kawo hari abin ɗaga hankali ne ga duk ’yan Nijeriya — Peter Obi
  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump
  • Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump