Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-05@11:05:13 GMT

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba

Published: 5th, November 2025 GMT

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta ce ta samu amincewar gwamnatin tarayya domin gina sabbin gada biyu na sama da kuma ta karkashin kasa (under-pass) a yankin Mararaba da ke Karamar Hukumar Karu.

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mr. Peter Ahemba, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

A cewar Ahemba, gwamnati za ta fara aikin kafin gwamnatin yanzu ta kai ga karewar wa’adinta a shekara ta 2027. Ya ce tun da dadewa Gwamna Abdullahi Sule ya ware kudaden aikin, kafin ma a kammala tsarinsa.

Ya bayyana cewa, tun daga shekarar 2019, gwamnatin jihar ta kan ** tabbatar da ajiyar kuɗi kafin fara kowanne babban aiki**, saboda dorewa da tabbatar da kammalawa akan lokaci.

Ahemba ya ce gina wadannan flyovers da under-pass ya zama dole sakamakon cunkoson ababen hawa da ke addabar yankin Karu–Mararaba, musamman ga mazauna da direbobi da matafiya.

“Wannan aiki zai magance matsalar cunkoso, ya inganta tafiyar ababen hawa, tare da ƙara ingancin hanyoyi,” in ji shi.

Ya kara da cewa gwamna ya bai wa Hukumar Nasarawa State Urban Development Agency (NUDA) umarnin gudanar da bincike da tantance wuraren da suka fi dacewa domin gina wadannan ayyukan.

Mr. Ahemba ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar fara aikin, ta kuma kammala shi kafin karewar wa’adinta a 2027.

Aliyu Muraki, Lafia.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

 

A halin yanzu, sashen saukar kumbuna da dukkan na’urori da tsare-tsaren da ke aikin tallafa wa saukar kumbo suna ci gaba da shirye-shiryen tarbar ‘yan sama jannatin, kamar yadda Hukumar Kula da Zirga-zirgar Kumbuna ta kasar Sin ta bayyana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar November 4, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya November 4, 2025 Daga Birnin Sin Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa November 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
  • China ta yi martani kan barazanar Trump ta kai hari Najeriya
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka