Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
Published: 17th, May 2025 GMT
Sojoji da mafarauta don halaka mayaƙan Boko Haram biyar tare da daƙile wani hari da ’yan ta’addan suka kai a ƙauyen Warambe da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno.
Warambe na daga cikin yankunan da mazanaunansu suka dawo da zama a baya-bayan nan, kuma mayaƙan Boko Haram sun sha yin yunƙurin kurɗawa cikinsa.
Shugaban mafarautan wanda ɗan asalin garin ne ya ce a safiyar Juma’a ne maharan suka nemi shiga ƙauyen, “amma muka gana su, muka kashe mutum biyar daga cikinsu. An miƙa makaman da muka ƙwato daga hannunsu ga sojoji.”
Sanata Mohammed Ali Ndume mai wakiltar Kudancin Borno, ya jinjina wa ƙoƙarin jami’an tsaron, musamman wajen ɗaukar mataki cikin gaggawa yana mai ba su ƙwarin gwiwar su ƙara jajircewa.
Mutum 3 sun mutu, 21 sun jikkata a turmutsitsin karɓar kuɗin tallafi a Borno Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a TarabaSanata Ndume yace ce, “ina farin cikin sanar da ku cewa an kashe ’yan ta’adda biyar a ƙauyen Warambe. Ina kunjinjina wa mafarauta da kuma yadda aka yi saurin ɗaukar matakin tura sojojin rundunar ‘Operation Hadin Kai’ zuwa wurin, wanda ya ƙara wa al’ummar yankin ƙwarin gwiwa.”
Makaman da aka ƙwato sun hada da bindiga ƙirar AK47 guda biyu da harsasai, kuma an damƙa su a hannun sojoji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram mafarauta
এছাড়াও পড়ুন:
Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
Farashin Man Fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran, lamarin da ya tayar da hankalin masu zuba jari.
Ana fargabar cewa rikicin da ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin ƙasashen biyu zai iya kawo tangarɗa wajen samar da man fetur daga yankin Gabas ta Tsakiya.
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8Wani muhimmin wurin da ake safarar man fetur na duniya, wato mashigar Hormuz da ke kusa da Iran na da matuƙar tasiri, domin kashi ɗaya cikin biyar na dukkanin man da ake fitarwa daga nan ne ake bi da shi.
Amma duk da haka, kasuwannin hannun jari sun fuskanci faɗuwar daraja saboda rashin tabbas da harin ya haifar.
Sai dai darajar wasu hajojin da ake ɗauka amintattu a lokutan rikicin irin su zinariya da kuɗin ƙasar Japan, Yen sun tashi sama, domin masu zuba jari na ƙoƙarin neman mafaka a cikinsu.