HausaTv:
2025-08-15@21:46:33 GMT

Isra’ila ta yi barazanar kashe shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen

Published: 17th, May 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta yi barazanar kashe jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Abdul-Malik al-Houthi, idan har Sana’a ta ci gaba da kai hare-hare da makami mai linzami kan Isra’ilar don goyon bayan Falasdinu.

Ministan harkokin soji na gwamnatin, Isra’ila Katz ya ce idan har Yemen ta ci gaba da ayyukanta “za su sha azaba mai radadi.

” 

Katz ya ce kisan da gwamnatin za ta wa al-Houthi zai yi kama da kisan gilla kan “Deif da Sinwars a Gaza.”

Ministan na Isra’ila yana magana ne a kan tsohon kwamandan kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da ke Zirin Gaza, Mohammed Deif, wanda gwamnatin kasar ta sanar da kashe shi a watan Janairu.

Katz ya kuma ce yuwuwar nasarar kisan gillar da gwamnati ta yi kan al-Houthi zai iya tunawa da kisan gillar da Tel Aviv ta yi wa tsohon babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah, da kuma kisan Ismail Haniyeh, wanda shi ne shugaban ofishin siyasa na Hamas da Yahya Sinwar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawar alaka da kafafen yada labarai.

 

Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya, da ‘yan majalisar zartaswar NUJ na kasa (NEC) da suka je Kano domin taronsu.

 

Gwamnan wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta, ya yaba wa kungiyar ta NUJ bisa zabar Kano a taron ta na kasa, yana mai jaddada cewa wannan shaida ce ta kyakkyawar alakar aiki tsakanin gwamnatin jihar Kano da kafafen yada labarai.

 

Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara wajen inganta rayuwar jama’a, da kuma tabbatar da cewa dole ne a cika alkawuran yakin neman zabe.

 

“Wadannan alkawuran sun hada da samar da ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma, da karfafa matasa da mata,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da fitar da wasu ayyuka da za a yaba don inganta rayuwar al’umma.

 

Mataimakin gwamnan ya ci gaba da yaba wa kungiyar ta NUJ bisa rawar da take takawa wajen tabbatar da dimokuradiyya, da tabbatar da bin doka da oda, da wayar da kan al’umma, inda ya ce kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen samar da shugabanci na gari.

 

Ya kara da cewa “Gwamnatinmu tana da abokantaka da kafafen yada labarai kuma za ta ci gaba da bayar da dukkan goyon bayan da suka dace don tabbatar da cewa ‘yan jarida suna gudanar da ayyukansu cikin ‘yanci, da sanin ya kamata, da kuma samar da yanayi mai kyau,” in ji shi.

 

Shugaban kungiyar ta NUJ, Kwamared Alhassan Yahaya ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa karbar bakuncin taron, ya kuma yaba da ci gaban jihar, wanda tawagar ta lura da haka a ziyarar gani da ido da ta kai a babban birnin.

 

“Mun gamsu da ci gaban da aka samu kawo yanzu ta fuskar samar da ababen more rayuwa da ake samu a Kano,” inji shi.

 

Alhassan ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa goyon bayan da take baiwa kafafen yada labarai, kuma ya nemi a dore da wannan matakin.

 

Tun da farko kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya ya yi maraba da shugabannin kungiyar ta NUJ tare da yi musu fatan zaman lafiya a yayin taron, inda ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kafafen yada labarai.

 

Ana sa ran taron NUJ NEC zai tattauna kan muhimman batutuwan da suka shafi aikin jarida a Najeriya, da suka hada da jin dadin kafafen yada labarai, kare lafiyar ‘yan jarida, da dabarun kungiyar na kare ‘yancin ‘yan jarida.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida