HausaTv:
2025-07-01@18:01:06 GMT

Isra’ila ta yi barazanar kashe shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen

Published: 17th, May 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta yi barazanar kashe jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Abdul-Malik al-Houthi, idan har Sana’a ta ci gaba da kai hare-hare da makami mai linzami kan Isra’ilar don goyon bayan Falasdinu.

Ministan harkokin soji na gwamnatin, Isra’ila Katz ya ce idan har Yemen ta ci gaba da ayyukanta “za su sha azaba mai radadi.

” 

Katz ya ce kisan da gwamnatin za ta wa al-Houthi zai yi kama da kisan gilla kan “Deif da Sinwars a Gaza.”

Ministan na Isra’ila yana magana ne a kan tsohon kwamandan kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da ke Zirin Gaza, Mohammed Deif, wanda gwamnatin kasar ta sanar da kashe shi a watan Janairu.

Katz ya kuma ce yuwuwar nasarar kisan gillar da gwamnati ta yi kan al-Houthi zai iya tunawa da kisan gillar da Tel Aviv ta yi wa tsohon babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah, da kuma kisan Ismail Haniyeh, wanda shi ne shugaban ofishin siyasa na Hamas da Yahya Sinwar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa

Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayya shugaban kasar Amurka Donal Trump a matsayin mutum wanda baya iya yin magana guda ya tsaya kanta, mutumtum ne wanda yake tupka da warwara a lokaci guda.

Tashar talabijin ta Presstva a nan Tehran ta nakalto kakakin  majalisar dokokin yana fadar haka a zaman majalisar dokokin kasar a jiya Talata.

Qalibof ya kara da da cewa kalaman da Trump yake fada na kaskanta shugabannin JMI yana daga cikin yakin kwakwale ne da mutanen kasar Iran. Kuma yakamata ya sani, kuma wadanda suke tare da shi su sani mutanen Iran zasu ci gaba da kare kansu su kuma yaki da wadanda suke shishigi a kan kasarsu.

Daga karshen yan siyasan makiya ne zasu bace a cikin kwandon sharer siyasa nan ba da daewa ba.

Tun lokacinda Amurka ta kai hare-haren kan cibiyoyin nukliyar kasar Iran guda uku wato Natanz ta Fordo da kuma Esfahan ne kasashen biyu suke mu sayar magangannu a tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  •  Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
  • Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba
  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan