An tabbatar da mutuwar mutum uku tare da jikkatar wasu da dama sakamakon turmutsutsu a yayin wani taron rabon kuɗaɗen tallafi a garin Bama da ke jihar Borno.

Wasu bayanai sun bayyana cewa ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Najeriya da UNICEF suka shirya rabon tallafin.

Shaidun gani da ido sun ce, turmutsitsin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin karfe 8:00 na safe a makarantar firamare ta Kasugula, daya daga cikin cibiyoyin bayar da tallafi da aka kebe a garin Bama.

Rahoton na nuni da cewar waɗanda suka ci gajiyar shirin sun taru ne domin karɓar tallafin kuɗi na naira 28,500 kowannensu.

Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta da cizo a Ribas Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta da cizo a Ribas

Turmutsitsin ya faru ne a daidai lokacin da jama’a suka yi cincirundo a bakin  kofar makarantar, lamarin da ya haifar da turereniya.

 

Wani dan shekara 60 mazaunin Mazaɓar Bukar Tela, wanda lamarin ya ritsa da shi ya rasu ne a lokacin da aka isa babban asibitin garin Bama. Daga baya wasu mutane biyu da suka jikkata sun mutu yayin da ake jinya a asibiti.

Majiyar ta ce, waɗanda suka samu raunukan sun hada da mata da maza, kuma an tura karin sojoji wurin da lamarin ya faru domin dawo da zaman lafiya tare da saukaka kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Daga bisani aka bayar da gawarwakin mamatan ga iyalansu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Kungiyar ta ICRC_Africa ta ce ba ta da hannu a aikin rarraba kudaden a Bama wanda ya haifar da wannan turmutsitsin da ya kai ga asarar rayuka, kamar yadda aka gabatar a cikin rahoton farko.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

“Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya.

“Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi.

Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara.

Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin.

“Wannan ziyara tana da matuƙar muhimmanci ga mutanen da abin ya shafa. Muna godiya, kuma Allah Ya ci gaba da maka jagoranci,” in ji shi.

Gwamna Lawal ya kuma yi alƙawarin inganta ayyukan more rayuwa a yankunan, kamar hanyoyi, wutar lantarki, ruwan sha, da sauransu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani
  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara
  • ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 
  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno